Main menu

Pages

zulfa complete Hausa novel

: ●● ZULFAH ●● 1⃣ By Aysha Ya'u Kurah Dare ne mai cike da dumbin rahama, kowa na cikin gidanshi sakamakon Ruwan da ake tsugawa, masu abin hawa suna ciki, masu tafiya a kafa da mashin sun fake saboda ruwan yinshi akeyi kamar da bakin kwarya, ma'aikatan dare suna wajen aikinsu, A wannan lokacin zulfa'u na cikin ruwan tana wanke kwanukan da aka ci abincin dare a gidan, yawan ruwan da akeyi baisa goggo marka ta tausaya mata ba, yayin da ita kuma take dakinta na kasa, kan rubabiyyar katifarta, rushi ne a gefenta suna shan dumi ita da yarta Salaha, can gefe kuma mahaifin zulfa ne zaune yayi tagumi yana leken yarshi dake faman aiki cikin ruwa, zuciyarshi na zafi amma bashi da yadda zaiyi saboda marka ta fi karfinshi, Allah Allah takeyi ta gama ta shiga dan karamin dakinta da bai wuce taku shida ba, tana gamawa ta gyara gurin da sauri saboda ruwan kamar dada ingizoshi akeyi, tayi maza ta tsaya bakin kofar dakinta ta cire kayan jikinta saboda kar ya jika mata daki dama ga dakin ba kofa ruwa duk ya jika kofarshi, matse kayan tayi ta shanya a saman kwanonta, tasa wasu yagaggun kaya da suka zaizaye saboda tsufa, da sauri ta hau kan katifarta wacce bata da maraba da tabarma, yunwa sosai take ji dan ragowar da take samu ma yau basu rage ba, gara ma na kabiru yayan salaha ya dan rage kadan saboda ta samu, amma saboda tsabar ta kosa taji muryar dake debe mata kewa tasata bacci cikin farin ciki, muryar dake sata manta ko wani irin bacin rai yasa ta share yunwar da takeji, ta dakko redionta da gurin kunnanawan a cire yake, in ka ga radion bazaka taba cewa in an kunna zaiyi aiki ba, kibiyarta tasa ta kunna shi, cikin zakuwa ta kamo tashar liberty ta kure muryar radion dan battery ya kusa mutuwa, ta tura kanta cikin zaninta ta kara radion a kunnenta, saura 5mints takwas tayi, ta dinga sauraren wakokin da akeyi, takwas dai2 taji ansa sassanyar waka mai tsuma zuciyar masoya, lumshe idonta tayi saboda tasan taken isowar gwaninta kenan, kara gyara kwanciya tayi ko kadan sanyin da takeji ya gushe, muryar "Abubakar sadiq marafa" ita ta daki dodon kunnenta cikin salonshi na isa da kasaita, salon dake burge dubban mata masu aji dake cikin garin kaduna da kewayenta, sallama ya fara yi cikin harshen hausa da larabci, ya mika gaisuwa gurin masoyanshi da turanci, sannan ya fara programme dinshi cikin harshen hindu (indianci) cikin kwarewa yake gabatar da program dinshi, duk wata mace da ta isa a duk ranar friday to tana manne da radionta tun takwas har tara na dare, wasu ma da radion suke fita tadi saboda gudun kar a barsu a baya, ko wata shida sadeeq marafa baiyi da fara program dinshi ba amma saboda kwarewarshi da yadda mutane ke sonshi zaka rantse tunda aka bude gidan radion yake aiki a gurin"""!, kasancewarshi mutum mai girmama soyayya da son yanayi na damuna yasa aka kayata mishi wannan daren da wakoki masu sanyaya zuciya, karfe 8:40 bayan ya kammala da gabatarwa, ya rage amsa tambayoyin masoya, tambaya uku kadai yace zai iya amsawa a ranar saboda yana son yin bankwana da masoyanshi, gaban zulfa ya fadi hankalinta ya tashi, ta yaye xanin da ta lulluba dashi saboda wani gumi da taji ya keto mata"", cikin taushin murya zee gayu ta fara wurgo mishi tambayar farko, tace tambaya ta farko ta fito daga gurin "Salma Ibrahim, " tambayar da akullum sai MARAFA ya amsata babu mamaki malama salma bakuwace a cikin wannan shirin namu, tambayar itace shin sadeeq yana da aure,,, dariya sadeeq yayi saboda yadda zee ta karasa maganar yace zeee kenan, malama salma bani da aure, sai dai kuyi min fatan samun mace ta gari kuma kamila, zee tace bakayi niyya ba dai ga mata nan kamar zasu ci kansu, murya can kasa saboda kar masu sauraro suji yace zee ban hadu da muradin raina ba har yanzu, ya lumshe idonshi yana siffanto irin macen da yakeso tun yana yaro, zee ta bude murya da karfi tace to masu sauraren mu marafa dai yace bai hadu da muradin ranshi ba har yanzu, sai ku tayashi addu'ar samu nan kusa, in kuma wacce zata kasance muradin ran nashi tana sauraronshi to sai tayi fatan Allah ya hada ta dashi komin daren dadewa, zo kuga mata a gidajensu yadda suke amsa ameen, zulfa ta share kwallar dake idonta, dama ita tasan bazata taba haduwa da sadeeq ba, saboda yayi mata nisa sosai yafi karfin ajin mace marar galiho da gata irinta, amma muryar dake sata manta bacin ran da ake mata a gida yau zata ma kunnenta bankwana, , to saboda me zaiyi bankwana?? Ta tambayi zuciyarta, kafin ta samo amsar tambayar har ya gama amsa tambayoyin, cikin taushin murya yace zanyi bankwana daku masoyana, zan ajiye wannan progrm din saboda bukatar hakan ta taso, ina rokonku da duk wanda na taba batawa a rayuwa ya yafe min, na yafe ma duk wanda ya bata min, wadanda basu sanni a fuska ba ina adduar Allah ya hada mu daku a aljanna firdausi, nagode da kaunarku Allah ya kawo wanda zai maye muku gurbina, a karshe ina bukatar addu'ar ku akan Allah ya taimakeni ya bani nasara akan abin da nake nema, nagode, nagode Allah ya barmu tare,,, wakace ta cigaba da tashi a kunnuwan masoyanshi dake kuka, zulfah ta wurga radion bayan yagalgalalliyar jakar kayanta ta shiga kuka baji ba gani, daren da ya kasance mai cike da sanyi da dadi ga ma'abota soyayya, ya kasance dare mafi zafi da kuncin a gurin baiwar Allah zulfah.... Mrs tijjani shattima ... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ●● ZULFAH ●● 2⃣ By Aysha Ya'u Kurah Washe gari tun biyar na asuba ta farka duk da ba wani isashshen bacci ta samu ba, tsakar gida ta fito taga tulin kayan wanki a kofar dakinta kayan goggo marka ne da na salaha, ta kalli kayan cikin faduwar gaba saboda yawansu ga danshin damina, ga kanta na masifar sara mata saboda rashin bacci da bata samu ba, ta zauna ta buga tagumi da buta a gabanta tana tunanin irin rayuwar da take ciki tun bayan rasuwar mahaifiyarta tana yar shekara goma take aikin bauta bata da wani lokacin farin ciki kullum tana cikin wahala, bata ko samun isashen abinci, wannan dalilin ne yasa ko da yaushe in kaga zulfa bata cikin walwala, bata kula kowa koda a makaranta ne, magana mai yawa tana yi mata wuya, in tayi magana ko kai wanda take ma maganar ba lallai bane kajita saboda tsabar sanyin maganar, tasha dukan asara gurin goggo saboda yanayin maganarta amma duk da haka bata sauya zani ba, saboda babu wanda zai iya canza nature, rankwashi mai karfin gaske shi ya katse mata tunanin da ta keyi, tayi maza ta sauka daga kan dakalin da take rike da kanta, goggo tace uban me kika zauna kikeyi agurin nan, duk ga ayyukan gidan nan babu ko daya da kika fara saboda tsabar iskanci da lalaci, to bari kiji kinga wannan wankin wallhy kika kuskura gari ya waye baki gamashi ba sai nayi mugun saba miki shegiya mai suffar mayu, ta wuce gurin kullun wainarta ta na masifa kamar zata ari baki, makota sun riga sun saba dajin muryar marka me waina a ko wace safiya, bare mahaifin zulfa malam ado da abin ya zame mishi jiki kuma bashi da yadda zaiyi ya fitar da yarshi daga cikin bautar marka, shiyasa a ko da yaushe yake fata da yi mata adduar samun miji tayi aurenta ta bar gidan, ya kudura a ranshi ko dan garuwa ne yazo neman aurenta in dai zai dauke mata ci da sha wallhy zai bashi, zulfa ta idar da sallah tayi yan adduointa, ta fito da sauri ta dauki katon bokitin penti ta shiga jido ruwa a mono din dake masallacin layinsu Allah ya taimaketa babu layi saboda gari bai waye ba,,, saleem dan limamin unguwarsu kuma malamin islamiyyarsu shi ya ganta tana diban ruwa bayan ya fito daga sallah, cikin tausayawa ya karasa gurin mono din, tanata bugawa tana haki taji sallamarshi tayi murmushi a hankali tace ina kwana malam, lafiya lau yace mata yana kokarin fara tayata buga panpon, tace ka bari malam nama gama wannan shine na karshe, bai saurareta ba saida ya gama cika bokitin, ya sa hannu zai dauka ta rike gefen bokitun tace dan Allah malam ka barshi kar in baka wahala, kallonta yayi yace saki bokitin ki wuce muje, batayi musu ba ta saka suna tafe har suka kai kofar gidan, ya ajiye dai2 dakalin shiga gidan, shi kanshi da yake namiji saida kirjinshi ya dan amsa saboda nauyin bokitin,,,, , ya kira sunanta a hankali yace kiyi hakuri zulfa wuya bata dorewa, komai na duniya mai wucewa ne,, kullum ki dinga addu'a Allah ya kawo sanadin da zai fitar dake cikin wannan bakar rayuwar, idonta ya ciko da kwalla tace nagode malam Allah ya saka da alkhairi, yace ameen,, kinsan yau zaku fara jarabawa kiyi sauri ki gama ki taho makaranta, tace to nagode malam, ta dauki bokitin ta shiga ciki da sauri ta fara wanki sai gurin shida da rabi ta gama duk sanyin da akeyi zulfa bata ji saboda tsabar wahala, tana gama dauraya ta shanya wasu a gidansu ta shiga gidansu inna delu inda suke shanya ta shanya sauran,,, hanne ce ta fito daga daki tana mika alamar yanzu ta tashi daga bacci, hararar zulfa tayi taja tsaki tace wahalalliya, a wahala zaki kare har karshen rayuwar ki sai shegen girman kan tsiya sai kace wata yar sarki, zulfa ko kallonta batayi ba saboda ta riga ta saba da duk wata masifar da inna delu da diyarta hanne suke mata, goggo ameena ce ta fito daga daki tace haba hanne ku sakar ma yarinyar nan mara tayi fitsari mana, da wanne zataji da na marka da salaha ko da naki ke da delu, ko dai wani ta kashe muku ya isa ace kun barta haka bare ba daya bare kanwar biyu,,,! haba ay nan goggo ameena ta kara harzuka hanne ta rufe ido tana surfa mata bala'i cikin raini har inna delu ta jita ta fito ta tayata suka dinga yi harda zungurin zulfa,,, faiza yar goggo amina ita ta taya zulfa shanya har suka gama ko kallon su hanne basuyi ba, goggo Ameena tace faiza kice zulfa kar ta tafi ta tsaya taci tuwo, fa'ee tace to mama, taja zulfa suka zauna suna dan hirar jarabawa goggo ta kawo musu dumamen tuwon dawa miyar tafasa, nan suka wanke hannunsu da ruwa suka fara ci saida sukayi katt saboda yawan tuwon, da sauri zulfa ta tashi ta deka dakin tace goggo nagode sosai bari in shiga gida, goggo ameena tace to zulfa ayita hakuri dai,, mai hakuri shi keda riba wata rana sai labari, tace to goggo nagode sosai, ta fito tace fa'ee sai kin biyo ta fita da gudu da bokiti a hannunta, tana shiga ta tarar maza da yawa zagaye da goggo marka masu siyan waina sai hayaniya sukeyi, ruwan sanyi ta diba a ruwan da ta debo ta wuce bayi tayi wanka saboda yawan mazan dake gurin yasa ta dauko kodaddan uniform dinta ta shirya a bayin, dakinta ta shiga ta dakko robar vaseline ta dinga kwakuloshi saboda ya kare da kyar ta samu kadan ta shafa a fuskarta, gurin kitchen taje ta tsuguna tace ina kwana goggo, ta kalleta a wulakance ta amsa tace rikakkiya ina kuma zaki, tace goggo islamiyya yau zamu fara jarabawa, salaha dake zaune kusa da wani me napep sun hada kansu guri daya wai suna kallon waya tayi tsakii sosai tace uban waye zai gyara miki dakin,, haka zaki barshi da datti saboda ba a ciki kike kwana ba, zulfa ta marairaice ko kallon salaha batayi ba tace goggo yau zamu fara jarabawa kuma ance muzo da wuri walhy daga na dawo zanyi, murfin tukunyar dake gefenta shi ta wurgo ma zulfa ya sameta a jikinta duk manja da bakin tukunya suka b'ata hijab dinta, cikin tsawa goggo tace dan ubanki wuce kije ki gyaro ko ina kuma ki fita ki k'aro ruwa ki cika ko'ina na gidan nan, kiyi zaman jiran a gama waina ki wanke komai ki daura girki,, idon zulfa ya ciko da kwalla ta mike ta shiga daki tanajin mazan gurin yan tasha suna shewa suna taya goggo aibata ta wasu ma har tafawa sukeyi da salaha da ke zaune a tsakiyarsu, ta gyara dakin goggo ,, ta fito ta dauki bokiti ta fita a kofar gida sukaci karo da fa'ee, fa'ee tace a'ah ina kuma zaki da bokiti, tace ruwa zan debo ki tafi kawai kar in bata miki lokaci, fa'ee ta fisge bokitin da karfi cikin tsiwa ta wurga shi cikin gidan taja hannun zulfa da karfi suka fita tana janta zulfa na tirjewa, hakan bai sa faiza ta saki hannunta ba har saida suka karya kwana, zulfah cikin muryar kuka tace fa'ee kinsan irin bala'in da kika jamin ne, meyasa zakiyi haka, kinsan bani da mafita dan wallhy goggo bazata yarda bani na wurgo bokitin ba, yau Allah ne kadai zai iya kwatata a hannunta dan yau kasheni ne kadai ba zatayi ba, Kuka sosai ta tsuguna a kasa takeyi, fa'ee tace tsoronki shi ke ja miki matsala, kalleki zulfa wallahi kin wuce duka, amma kullum ayita kirbarki kamar jaka ke bazaki iya kwatar ma kanki yanci ba saidai ki zauna ki dinga kuka shiyasa duk suka raina ki, wani yanci fa'ee ni har inada wani yanci a rayuwata, mahaifina bai nemar min yanci ba sai ni zan nemawa kaina, fa'ee rayuwar nan da nake cikinta bana neman taimakon kowa sai Allah, shi kadai yasan dalilin barina cikin wannan halin, kuma ina gode mishi a ko da yaushe tunda ya barni da rai da---- da lafiya suka ji an karashe daga bayansu, fa'ee ta tsuguna tana murmushi tace ina kwana malam, ya amsa yana kallon zulfa dake ta faman kuka, itama ta gaisheshi, ya amsa a gajarce yace ku wuce maza makaranta dan lokaci na kurewa, fa'ee ta kamo hannunta suka wuce tana share hawaye, binsu yayi da ido cikin tsananin tausayi a ranshi yace Allah ka kawo sauyi cikin rayuwar baiwarka zulfa'u.... Mrs tijjani shattima.. [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ●● ZULFAH ●● 3⃣ By Aysha Ya'u kurah Tafiya nakeyi da sauri duk kafata ta gaji saboda rashin abin hawa ga unguwar da zanje da nisa, a wani katafaren kayataccen gida kafata ta tsaya, gidan da zan iya cewa duk cika da batsewar GRA babu gida kamarshi, a kofar gate na tsaya saboda na duba gabas da yamma kudu da arewa ban samu hanyar shiga ciki ba, gefe na rabe ina dan hutawa kusa da wasu flowers, kamar daga sama na hango sojoji sun wangame gate din gidan, da sanďa na shiga gidan dan kar su ganni in shiga uku, tsaye jikin wata ford 2014 na hango wani magidanci kyakykyawa mai cikar zati da kyawun fasali cikin white uniform din navy kuma da dukkan alamu babban sojan ruwa ne, gefenshi wata kyakykyawar mace ce black beauty rike da wata farar yarinya da bata wuce 4yrs ba, kamaninta da namijin gefenta yasa na gane y'arshi ce, daga nesa na hango wata yarinya mai masifar kyau wacce shekarunta zasu kai 18 rike da kannenta biyu masu kama da junansu cikin kaya iri daya suna tahowa, kusa da macen suka tsaya, babbar tace yaya ina kwana, ya amsa cikin fara'a yana shafa kan twins, taja hannun babyn dasuke tare da ita tace adda laila gud morning, tace morning dear, kunga ku wuce ku shiga mu tafi kar su daddy su dawo bamu karasa ba, motoci biyu suka shiga kowacce soja ke janta sai wata da sojoji biyu ke cikinta, suka fita daga cikin gidan sojoji na sara wa motocin,, Farar mace ce kyakkyawa zaune cikin kayataccen parlon da sanyi da qamshi ke tashi a ciki, tana zaune cikin wasu lafiyayyun kaya masu masifar kyau, 40rabbna ne a hannunta tana dubashi, sakkowar mutum naji daga sama na daga kai na hango wata kyakykyawar mace itama cikin shiga ta alfarma, fuskar nan tasha makeup, ta karaso ta zauna kusa da matar dake parlon, ina kwana "yaya" naji tace cikin fara'a, wacce ke zaune ta dago kanta itama cikin fara'a tace anty amarya kin tashi lafiya, lafiya lau tace suka cigaba da hira anan na gane amarya da uwargida ne, Awansu daya da fita suka dawo gida,, da sallama suka shigo parlon wani farin dattijo ne ya fara shigowa sannan duk suka take mishi baya, wani saurayi na gani cikin uniform irin na jikin dattijon da nakeda tabbacin mahaifinsu ne, ya karasa kusa da matan gidan dake tsaye suna tarbar mijinsu, yace mummy, antyna gud morning, anty ta amsa tana shafa kanshi tace morning my son hw r u, yace am fine mun sameku lafiya ko, lafiya lau suka ce dukkansu,, kowa ya nemi guri ya zauna anata yan hirarraki cikin farin ciki,, Mrs tijjani shatima... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ●● ZULFAH ●●4⃣ By Aysha Ya'u Kurah Nasan masu karatu zasu so suji tarihin wannan gida to muje zuwa.. Gidan chief of air staff of the nigerian airforce "AIR-MARSHAL HASHEEM ABUBAKAR MARAFA", nan na kaiku,, yanada mata biyu haj Aisha (mummy) itace uwargida, sai anty Hadiza ( anty amarya) yana da ya'ya 6 kuma duk ya'yan na mummy ne dan anty amarya bata taba haihuwa ba, Usman (Nurain) shine babba, sojan ruwa ne da ya samu nasorori da dama, yanzu haka shine NAVAL COMMANDER, yanada mata daya Laila da ya' daya "Ayda", yana zaune da iyalinshi cikin gidan iyayenshi, suna zaman lafiya dan laila mace ce mai kirki sosai da son mutane, Abubakar sadeeq (abba) shine ďa na biyu a gidan, ya gama stanford univesity dake california, sannan yanzu ya samu training a university in "Montgomery albama", "Air force university" inda zaiyi 2yrs yanayi, yanzu haka sunje sun gama komai na reg da mahaifinshi zai koma nan da 1wk, kafin samuwar training din ne ya fara programme a gidan radion liberty inda wata sec skool mate dinshi ke aiki "zee gayu", tun yana yaro yake da son programs, dramer, da dai sauran abubuwan da ya shafi media, babu yadda baiyi ba akan mahaifinshi ya barshi ya karanci abin da yake so amma firr yaki saboda shi a ra'ayinshi yafi son jininshi ya yi soja kowane iri ne, da kyar mummy ta lallaba sadeeq ya yarda ya zabi sojan sama, basu sha wani wahala gurin samun skull din ba saboda matsayin mahaifinshi,,, sai Umar (farouk) shine na uku, yana Oxford uni, Jalila itace ta hudu, ta gama secndry skul dinta a dambo international skul, sai twins Afrah da Amrah yan shekara 7 suna primary 2 a legacy school, Anty amarya ta damu matuka saboda rashin haihuwa, babu asibitin da ba'a kaita ba amma an tabbatar musu da bazata taba haihuwa ba, tun abun na damunta har ya daina damunta saboda yadda take samun kulawa gurin mijinta, ya'yanshi da matarshi, mummy na zaune tsakaninta da Allah da anty amarya, tana bata hakkinta saboda ta karanci hukuncin mai tauye hakkin dan uwansa, mace ce da zamu iya kiranta da mai kin duniya da kyalekyalen cikinta, kullum mummy kome takeyi bakinta baya rabo da tasbihi, anty amarya kuwa yar son a huta ce, rayuwarta gaba daya ta ginata ne akan karya, burinta tasa kaya mai kyau ta fita yawo sojoji na take mata baya, ta shiga cikin kawaye a fantama, dan ma Allah ya rageta da rashin haihuwa da abinda zatayi sai yafi haka abinda take yawan sakawa a ranta kenan,, ,,,,, Duk ranar jumma'a ake zuwa koyar da mummy karatun addini, wata yar bukka suke zama ita da matashin malaminta Saleem Abdulrahman, yauma suna zaune kamar kullum bayan sun gama karatu, jalila ta kwashe qurani da littafan tayi daki dasu, malam saleem yana dan kara ma mummy wa'azi kamar yadda suka saba, bayan ya gama, ya mika mata katin saukar dalibanshi da za'ayi nan da sati biyu, cike da murna ta amsa tace in shaa Allah zaka ganmu, amma bayan kun gama saukar zaka tafi law skool din ko, yace in shaa Allah hajiya, mummy tace Alhamdulillah to Allah yasa munada rai, yace ameen hajiya sukayi sallama ya tashi ya tafi... Zaune suke da daddare a parlon gidan,, twins da ayda suna kwance suna home work jalila na koya musu, daddy da Nurain basu nan sun fita, sadeeq na kwance gefen mummy yana mata hira, can kuma anty amarya ce da lailah suke ta kai komo a kitchen,, murda kofar akayi babu sallama, helllo dearies ta fadi hade da tura kofar, jalila ta daga kai da sauri ta mike tace SANAH luv oyoyo, duk suka rungumeta harda twins, ta ajiye akwatinta ta karasa kusa da mummy da ke kallonta tana yake dan sam ďabiun sanah basu mata ba, ta rungume mummy tace mom ya gida mummy tace lafiya lau sanah ya ummanki, sanah tace fyn ta kalli sadeeq dake gefen mummy ya kasa dauke idonshi akanta, ta hura iska a fuskarshi, tace yaya abba ait, ya lumshe idonshi saboda wani qamshi da yaji a iskar, jalila ta jata suka dauki akwati suka wuce ciki, saida ta gama frshup cikin wata karuwar doguwar riga sannan suka fito parlor, anty amarya baki sake tace sanah yaushe kika shigo, mummy tace ay bazaki ganta ba tunda taga kawarta, sanah tayi dariya tace anty "dee" ya kike, tayi murmushi ta amsa tana cigaba da gyaran dining, sadeeq da yayi mutuwar zaune saboda kallon sanah, ya kara gyara kwayar idonshi ya tsaida su a kanta sosai, gaskiya yarinyar ta fisgeshi lokaci daya, wani irin sonta yakeji a can cikin ranshi, ta dace da irin matan da ya dade yana mafarki, shidai bai santa ba to a ina kowa yasanta a gidan su, "SANAH HAMEED" yar yayar anty amarya ce dake zaune a abuja, mahaifiyarta yar siyasa ce babba, mahaifinta kuma custom ne, sanah ta tashi cikin gata da sangarta saboda ita kadai Allah ya ba iyayenta, rayuwar sanah gaba daya babu No a cikinta komai tayi dai2 ne, iyayenta sam basu kula da tarbiyyarta dan su a ganinsu komai tana yinshi bisa tsari, irin kayan da sana ke sawa in ka ganta zaka rantse ba musulma bace, kyakywace sosai doguwa ga kyan jiki ta hada komai na mace mai aji, sai dai hali daya mata cikas, Allah ya zuba ma sanah son kyawawan maza ko namiji baida kudi in dai kyakkyawa ne to ya gama da ita, dan sai tasan duk yadda tayi suka zama masoya, daga ta hadu da wani wanda yafi wancan zata yar dashi ta kama wani, in dai akan namiji ne to sanah bata da alqibla ita kanta bazata iya kirga mazan da tayi mu'amala dasu ba tun tana js3 har kawo yanzu,, sadeeq yana makaranta lokacin da sanah ke zuwa hutu gidansu, har ta gama hutunta ta tafi basu taba haduwa ba, amma ita tasanshi sosai dan har hotonshi gareta.... Mrs tijjani shattima... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ●● ZULFAH ●● 5⃣ By Aysha Ya'u Kurah A hankali take leķen gidan da ganin idonta a firgice take, ganin babu kowa a tsakar gidan yasa ta karanta addu'a tashiga ciki tana waige, ta kai dai2 dakinta taji an fisgota da karfi har saida hijab dinta ya yage sosai a wuya, fitsari ta saki a wando saboda yanda taga idon goggo marka babu imani a cikinsu hannunta rike da wani murďaďďen sanda wanda ta saba dukanta dashi, durkushewa zulfa tayi idonta yanata ambaliyan ruwa, cikin sanyin muryar kuka tace goggo dan girman Allah kiyi---- saukar sanda taji a bakinta ta fara ihun neman taimako, dukanta marka takeyi babu ko digon tausayi a ranta, saida ta tabbatar ta mata liss sannan ta kyaleta ta wurga sandar gefe tana huci, tace dan kutumar ubanki har ni zan saki aiki saboda ke tabbatacciya ce tsinanniyya, har kinada karfin gwiwar wurgo min bokiti daga waje, to tsaya kiji in kina ganin kin fara balaga nonuwa sun tsuro miki kina ganin yanzu kin ri'ka kamar rikakkiyar kubewa, tashen balaga zai fara bayyana kanshi, to bari kiji in fada miki wallhy kinji na rantse da Allah daga yau karfe hudu zaki dinga tashi a gidan nan, waina ma na daina zaman suyanta ke zaki dinga soyawa kina siyarmin, islamiyya kuma sai dai kiyi a lahira in anayi, haka boko ko kun koma hutu na haramta miki shi, duk ranar da kika kuskure abu daya cikin abinda na lissafa miki hummm"" zulfa'u ki kira kanki gawa kinaji na, eh ta fadi a hankali jikinta ciwo yake mata sosai, zafin da takeji a zuciyarta yafi wanda takeji a jikinta, yanzu shikenan an hanata zuwa islamiyyar da saura kwanaki tayi sauka, kuka ta dingayi a gurin taji an sa kafa anyi ball da ita, a tsorace ta fara rarrafawa tana kuka har ta kai ďakinta, hada kanta tayi da gwiwa ta cigaba kukan da babu mai rarrashi, yanzu shikenan babu wanda zai kwatar mata yancinta, shikenan ita haka zata kare cikin wahala, ta dade tana kuka kiran sallar azahar ne yasa ta ta mike dan taje tayi sallah, tana kokarin mikewa kafarta tace bata san zancen ba, ta koma da baya ta xauna hawaye na bin idonta, targade goggo tayi mata a hannu da kafa, da jan jiki ta fito ta shiga bayi ta dauraye jikinta ta canza kaya, tayi alwala ta koma daki tayi sallah, ta dan kwanta dan taga fitar su goggo da salaha, bacci ne yayi gaba da ita, bata san lokaci yaja har haka ba saboda baccin yayi mata dadi ko ba komai ta dan huta, ruwa taji an sheka mata a jiki, ta farka tana waige2 a firgice, ga warin da ya ishi hancinta, ta kalli jikinta cikin kyankyami ta kalli salaha, tace ruwan kwata kika watsa min, innalillahi kadai take fadi a ranta ga wani amai daya taso mata, salaha ta wurgo mata bokitin jikinta tace an watsa miki ko kina da abinda zakiyi ne, zulfa ta girgiza kanta tace babu,, Allah ya isar min, salaha tace kambuu lallai yarinyar nan, ni kike ma Allah ya isa, zulfa ta mike da kyar tana dingishi salaha ta kara tare kofar dakin rike da kugu tace dan uwarki wa kike ma Allah ya isa, zulfa tayi banza da ita zata bi ta gefe ta fita salaha ta hankada ta da karfi kanta ya bugu da bango, rike kanta dake juya mata tayi kwata2 bata iya gane zagin da salaha ke mata saboda azaba, ta dade a durkushe tana kuka kafin nan ta fita ta cire kayan jikinta tayi wanka ta yi alwala da kyar tayi sallah, ta fito jiri na ďibanta ta fara iza murhu har ya kama ta daura ruwan talge, a daddafe take aikin har ta gama abinci goggo marka bata dawo ba, ta gyara ko ina ta dauraye kayanta, sannan ta shiga daki ta dan kwanta idonta kamar an daura dutse, sallamar babanta taji a hankali bayan magriba ya dauka marka ta dawo daga gidan biki ne, ďakinta ya leka yaga bata nan, da sauri ya fito ya shiga ďakin zulfa, a hankali ya ďan bubbugata ta mike a firgice, yace zulfa'u ni ne, ta mike a hankali ta zauna tace ina wuni baba, idonshi ya ciko da kwalla saboda yadda yaga jikin yar tashi yace dukanki sukayi ko, ta fashe da kukan da take boyewa ya rike hannunta yaji zafi rau yace kiyi hakuri zulfau, nasan komai ake miki a gidan nan nine sanadi, ki yi ta addu'a komai na duniya mai wucewa ne, kuma wata rana sai labari, zuciyar zulfa ta kara zafi a ranta tace kullum sai ace mata wata rana sai labari wai ita yaushe labarin nan zai zo har ya wuce ne,, cikin muryar kuka tace baba" goggo tace bazan kara zuwa islamiyya ba kuma jarabawar sauka mukeyi, dan Allah baba ka taimakeni kar a katse min karatuna, ya rungumeta sosai ajikinshi shima kukan yakeyi dan yasan marka baxata taba janye kudirinta ba, yace kiyi hakuri zanyi miki kokari zulfa share hawayenki, ya dagota yana share mata hawaye itama ta share mishi nashi, da sauri yasa hannu a aljihunshi jikinshi har rawa yakeyi ya dauko leda ya bude nama ne yanka biyu ya fito dashi yace dazu aka kawo naman walimar sunan y'ar datti shine aka raba mana kowa bibbyu shine na kullo miki nawa, karbi kici yakai bakinta, ta rike hannunshi tana kuka tace baba kaci daya nima inci daya ya kara share mata hawaye yana girgiza kai yace kinfi ni bukatarshi cinye duka kinji, tasa hannu zata karba taji an warce naman ana huci kamar kura, suka dago kai suka kalleta tana kallon naman tana huci kamar bata taba cin nama ba, tace nama, nama ne fa salaha ta fadi tana nuna ma 'yarta, tabdi lallai ado ka cika munafuki, yaushe rabon da muci nama a gidan nan shine yanzu dan kaga bana nan ka kullo ka kawo mata, tayi kan zulfa da jikinta ke rawa tace dan ubanki nawa kikaci, yau sai kin amayar dashi duka, ta danneta zulfa na kakari tace wallhy ko daya banci ba goggo, da kyar malam yayi ta maza dan yaga ana kokarin raba yarshi da ranta ya tura marka da karfi, cikin zafin nama kamar namiji tayi kanshi tana dukanshi har saida ta yaga mishi riga, hakuri kawai yake bata tana kara turashi tana masifa, kabiru ne ya shigo da sauri saboda yaji hayaniyar tayi yawa, dakyar ya iya rabasu yana kuka yace haba goggo wai meyasa kike irin wannan abun ne, ji yadda---- mari ta kai mishi har biyu tana huci tace to sallamame watsatstse wanda baya kishin uwarshi, wallhy ka kara fadin kalma daya anan saina daga maga nono shege dan iska, kabiru ya rike kuncinshi ya fita ranshi a bace, zuciyarshi na kara jin tsanar mace, ya kudira aranshi bazai taba yin aure ba har ya mutu in dai haka mata suke, a cikin gida kuwa marka nata masifa,, abinda zai baku mamaki bai wuce duk damben da marka tayi baisa ta saki naman ba yana nan makale a cikin hannunta, saida ta gaji dan kanta tayi shuru ta wuce daki, salaha ta bita tace goggo ina naman, ta harari salaha tace yana can a waje na watsar, salaha ta fita da sauri harda daukar fitila, tana fita goggo marka ta watsa naman a bakinta duka biyu, salaha tayi ta neman naman harda dakin zulfa saida ta duba ko ina kamar mayya, daki ta koma tana nishi tace ban gani ba goggo babu mamaki wani a cikinsu ya dauke, ummm goggo tace saboda naman na bakinta bata gama taune shi ba, salaha tace goggo dazu kinsan yarinyar nan zagina ta dinga yi, goggo dai ta kasa cewa komai saboda kar salaha ta gane abinda ke bakinta, salaha tace goggo kinajina kuwa, uhumm goggo tace tana kokarin kwanciya, salaha ta matso kusa da ita ta dafata tace wai goggo me yasameki ne, goggo ta kifa kanta a katifa tafara kukan karya tana ummmm, salaha tace to goggo meye na kuka, ay tunda kin musu laga2 xasu shiga taitayinsu goggo bata dago ba tana kokarin hadiye naman ta kware sosai ta dago da sauri tana tari ragowar da bata hadiye ba suka zubo ta dinga tari tana kakarin amai, salaha ta debo ruwa da sauri ta bata ta sha zata ajiye kofin a kasa taga naman da goggo ta fito dashi, salaha ta kara haskawa ta tabbatar nama ne, ta dago kai ta kalli goggo, ta tabe baki tace walhy gogg---- cikin sarkakakkiyar murya tace Allah ya tsine ma wanda yayi min magana ta juya bayanta ta kwanta idonta zuru2, salaha ta tashi ta fita tana girgiza kanta aranta tace mugunta fitsarin fako, lallai goggo ta shahara a mugunta, dama hausawa sunce bazaka taba kwarewa a mugunta ba har sai kama naka, walhy saina rama abinda goggo tamin tayi kwafa ta fita daga gidan gaba daya......... Mrs tijjani shattima.... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ●● ZULFAH ●● 6⃣ By Aysha Ya'u Kurah Washe gari ta tashi da wuri kamar yadda goggo ta umurceta, aikin gidan tayi gaba daya tana yi tana hutawa saboda hannunta, karfe shida da kwata ta iza wutar waina, tana zaune hayaqi ya turnuke gurin idonta ya cika da ruwa tana ta fiffita ga yunwa tanaji sosai,,, saida tandar ta dau zafi sannan ta fara suyar wainar, maza da yara suka fara shigowa cikin gidan, ta na suya tana siyarwa,,, sallamar wani wanda a kullum idan yazo gurin ke kaurewa da ihu saboda siyan ma duk wanda yake gurin yakeyi,, hannu ya daga musu yana zukar wiwi, ya kalli zulfa da ke iza wuta ya shafo gefen kunnenta, tayi maza ta ja baya ta dago kai tana kallonshi, yayi murmushi yace kuce yau yar kyakykyawa ce ke mana waina, ya daga murya da karfi yace a kira yara a basu waina yau waina ko daya bazata rage ba,,, wani yaro a gefe ya fita yana ihu yana fadin sai baban house Allah yaja zamanin baba uban baba, ya kara kallon zulfa ya matso kusa da ita sosai zai rike hannun ta, ta watsa mishi kullun wainar a fuskarshi, ta mike tsaye tace wani irin iskanci ne wannan, yan tashan dake gurin suka fara ihu suna bangis din kikayi wa haka, tayi tsaki ta cigaba da zuba kullun cikin tanda, sunata hayaniyar su, bangis bai kallesu bare ya tanka musu, hayaniyarsu ita ta fito da goggo da sauri tana hamma tace lafiya dai kuka cika min gida da ihu, ta kalli bangis da ya cika ya batse, ta dunkule hannu tace Allah yaja zamanin ka mai gidan masu gida, laminu dan koranshi yace dalla matsa can da wannan kirarin naki, in ba iskanci ba wannan kazamar yarinyar ta rasa wanda zata watsa ma kullu sai bangis, yau sai munga wanda ya tsaya mata dan uwarta, goggo ranta ya baci matuka saboda in bangis ya daina zuwa gurinta siyan waina ay ta kaďe, ta matso kusa da zulfa gadan2 har tana gurďe kafa, wani katon ice ta dauka zata buga mata, zulfa ta rintse idonta haďe ihu mai karfin gaske, da sauri bangis ya rike icen, cikin muryar kauraye yace haba haj markus, irin wadannan kayan masu tsada ay ba'a dukansu, barta taci bashi, zata biyashi nan bada dadewa ba, ya wurgar da icen gefe ya goge fuskarshi ya zaro dubu uku ya mika ma goggo yace ki raba ma yara wainar yau, ya shafi gefen hannun zulfa ya rintse idonshi hade da zukar wiwi, yasa kai zai fita goggo dai sai kallonshi takeyi cikin mamaki dan tasan bangis ba'a takashi a kwana lafiya, har ya kai kofa ya juyo yace zan auri yar nan taki markus nan da sati biyu, sai ku fara shirye2, ihu mutanen gurin suka Sá sunata fadin sai kayi wallhy,, Goggo marka ta kasa dauke idonta daga kofar waje, tana mamaki aranta, ta waiga ta kalli salaha dake tsaye bakin kofa ta kumbura tayi fammm, dan ba karamin so takeyi ma babangida BBG ba, daki ta fada da gudu tana kuka, zulfa ma kuka sosai takeyi kamar ranta zai fita, ya za'ayi ta auri bangis, innalillahi wa inna ilaihir rajiun shi ta dinga faďi, a ďaki kuwa baban zulfa ne ya dafe kanshi saboda jin furucin babangida, dan ba a unguwar "babbar saura" ba ko ina an sanshi a unguwar rimi da kewayenta, ya ďaga hannunshi sama idonshi na zubar da hawaye yace ya Allah kaine kake da hanyoyi da yawa wanda bamu san dasu ba, Allah ka kawo mana hanyar da take billewa cikin gaggawarka ni da ďiyata zulfa'u..... Mrs tijjani shattima... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ●● ZULFAH ●● 7⃣ By Aysha Ya'u kurah Zulfa na zaune ta gama suyar waina goggo ta rarraba ma yara, amma ita ko ďaya ba'a bata ba, fa'ee ta shigo da sauri dan sunyi latti, turus" tayi saboda ganin zulfa a gaban tanda tana kuka, ta dafa ta tace ke lafiyarki baki shirya ba, zulfa zatayi magana goggo ta ce bazata ba kinibabba uwar tsari, fita ki bar min gida muha'ina kawai, in kara ganin shegiyar kafarki a gidan nan kiga yadda zanyi dake, fa'ee ta murguda mata baki tace zanga uban da zai hanata zuwa makaranta, goggo tayo kanta da gudu ta fita da karfi tace karki damu zulfa babu wanda zai katse miki makaranta, goggo ta kulu matuka ta juyo ciki bata ce ma zulfah komai ba, kuma batayi mata magana kan babangida ba saboda kar maganar ta koma kunnenshi, jira takeyi ragowar yan tashan su fita ta ci ubanta, ta shiga ďaki tana rarrashin salaha dake faman kuka, salaha tace haba goggo, shikenan ni babu wanda zaice yana sona, na fa girmi zulfa da kusan shekara hudu amma kullum sai ita samari ke zuwa nema, haka nura telan bakin titi saboda zulfa baki ga wulakancin da yayi min ba, yanzu ga bangis da na kwallafa raina akanshi shima ya fara sonta, ya kike so inyi da raina, ta kara fashewa da kuka, goggo ta dinga rarrashinta akan tasha kuruminta indai bangis ne kamar ta aureshi ta gama, Malam ado a ranshi yace ko meye abin sha'awa a auren mashayi dan tasha oho, ya ce marka ni na fita, ta yi mishi kallon banza tayi tsaki tace kafi ruwa gudu, matsiyacin banza, ta juya ta cigaba da rarrashin yarta, A kofar gida ya tarar da liman da salim da wani dattijo, cikin girmamawa ya mika musu hannu sukayi musabaha, liman yace malam ado yanzu salim yazo ya sameni da wata magana, shine naga muna tare ya kamata inzo inyi muku magana tunda ay "ďa" na kowa ne, malam ado yace Allah dai yasa lafiya liman, liman yace lafiyar kenan, kawar yarka zulfa'u ce take fada ma salim wai ance zulfa'u bazata kara zuwa makaranta ba, haba malam ado sanin kanka ne saukar yaran nan bata wuce yan kwanaki ba, kuma ana yabon kokarin zulfa a ko'ina babu adalci ace za'a hana yaro mai hazaka yin saukar alkurani saboda wannan ranar yara da yawa suna ďokinta badan komai ba sai dan su nuna bajintar su a gaban alumma, wanda yayi kokari yaji dadi a yaba mishi ayi mishi kyaututuka su dawo gidajensu cikin farin ciki, zan iya takaice maka cewar yara suna sanya wannan ranar ta zama tarihi a cikin rayuwarsu, saboda haka na rokeka kayi hakuri ka barta ta cigaba da zuwa makaranta kwanaki kadan suka rage,, malam ado yayi jugum cikin tunani yace to liman nidai ban hanata zuwa makaranta ba, ku shigo daga ciki sai inyi muku magana da marka ku roketa nasan zata ga girmanka, liman suka shiga kallon kallo, suka maida numfashi sannan suka shiga suka zauna a dan karamin zauren, Marka ta fito kamar mutuniyar kwarai ta nemi guri a gefe ta gaishesu, suka amsa mata da fara'arsu, sannan suka koro mata abinda ya kawo su, bata nuna musu komai ba, tace au to to to, ba komai zata cigaba da zuwa, saleem yaji dadi sosai suka dinga mata godiya, tace babu komai ay ba saikun gode ba, har sun mike zasu tafi tace,,, Ammmm nace ba, suka waigo dukansu, tana dan murmushi ta kalli liman tace tun mutuwar saude buhun masara nawa ma ka taba kawowa gidan nan kace a ciyar da zulfa'u, cikin rashin fahimta liman yace ban gane ba, tace da hausa fa nayi magana, inaga kanada matsalar ji ne, ta kalli salim da ya haďe rai sosai tace ay kai ka fahimta ko, bata jira ya bata amsa ba ta kalli dattijon dake tsaye a gurin tace malam tanimu, sau nawa ma ka taba dinkawa zulfa'u kaya tunda muke tare dakai, , ran saleem ya baci sosai dan ya gane inda ta dosa, yace kinga malama bawai munzo kici mana mutunci bane, ta katseshi cikin masifa tace nidai kuka shigo kuci min mutunci har gidana, ku fada min uban da na taba shiga gidanshi sulhu ko rabon fada wato shine ni dan kun raina ni kun wani taso zugwi2 kunzo wai a bar zulfa tayi makaranta, in akwai uban da ke ciyar da ita sai ya fada min, ko kunya bakuji ba, wai kuma a haka kuna da ilimi, to lallai iliminku bai amfana muku komai ba, haka goggo tayita surfa musu ruwan bala'i malam ado na basu hakuri, saleem ya fita a fusace yace yau zan ganar da matar nan kurenta, zata gane taba zulfa'u kamar taba raina ne, bai zame ko ina ba sai police station, yan sanda uku ya bukaci a bashi suka taho tare har kofar gidan, lokacin goggo da salaha suna kan zulfa suna mata izayar da suka saba, sallama yansandn suka yi da karfi, goggo ta fito babu ko mayafi tace uban waye yake min sallama haka kamar gidan uban--- maganarta ta koma ciki saboda ganin masu bakin kaya, murya na rawa tace la-fiya daga ina, salim yace ku kamata itace nake fada muku, kuma ku tabbatar kun mata azabar da wani ma in yaganta bazai ganeta ba, durkushewa goggo tayi ta fara kuka ta rike rigar salim tace kayi wa Allah da manzonsa kayi hakuri, islamiyya ce zulfa yanzu zata tafi kuma ko za'a shekara a can wallhy bazan damu ba, dazu din ma wasa nake muku dan gata can ma tayi shirin makaranta, ya fisge rigarshi yace karya takeyi yallabai ku kamata kawai ku rufeta har sai dan kaina na sa a sakota, in kunga irin azabar da take ma yarinyar nan wallahy sai kun tausaya mata, kuma anjima kadan zan tafi gurin human ryt dole a kwato mata yancinta, da karfi yace take her out, zamuyi sharia dake daganan har lagos, wayyyyyyyyyyo Allah na abinda goggo ta fada kenan saboda "human ryt" din da yace da kuma "take her out" kuma ya ambaci shari'a lagos ta dauka wasu nau'ikan azaba ne da za'ayi mata ko ma akasheta, ihu takeyi tana crolln da gwiwinta tana rokon salim da ya daga kanshi sama, ihunta ne ya fito da salaha ganin yan sanda yasa ta zubewa a gurin itama tana ihu, ya raďa ma police din magana a kunne sannan yace duk ku tafi dasu azzalumai kawai, ya wuce ya shiga cikin gidan, hangota yayi a daki kanta a kasa tana kuka, sai da ya ķare ma dakin kallo sannan ya girgiza kanshi ya tsuguna yana mata magana a hankali, ta dago kumburarren idonta ta kalleshi, yace tashi kije ki shirya mu wuce makaranta, tace to, ta mike a hankali tana ďingishi jiri na neman yar da ita, dakewa tayi saboda tana son zuwa makaranta, uniform dinta ta hango can kasa duk anyi tsumma dashi, ta kwaso su tana kuka, zatayi magana yace ki sa ko wani irin kaya muje tara ta wuce ya fita waje yana kara jin tausayinta, a zaure ya tsaya yana kallon dramar goggo da yan sanda, bindiga daya ya saita a kanta nan take goggo ta saki fitsari, ta sulale a kasa ita bata suma ba kuma bata tashi ba, jikinta sai rawa yakeyi, saleem yace yallabai barta muje kawai kukan kurciya jawabi ne, yau in mun barta gobe in ta kuma wallhy babu lamuni, suka fita salim ya durkusa yace "karen bana goggo," wannan gargadi ne, ya fita ya sallami yan sandan yayi ta musu godiya...... Mrs tijjani shattima..... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ●● ZULFAH ●● 8⃣ By Aysha Ya'u Kurah Mummy me yake damunki, kwana biyun nan naga kina yawan shiga damuwa, mummy tayi murmushi ta kalli jalila tace babu abinda ke damuna jalila, me zai dameni ina da Allah da manzonsa, sannan inada miji mai kaunata kuma inada nutsatsun ya'ya kamarku ta karasa faďi tana shafa kan jalila, jalila tayi dariyar jindadi tace hakene mummy, suka cigaba da hirarsu ta ďa da mahaifi, a cikin hikima mummy ta jefo ma jalila tambaya akan abinda ke damunta tace jalila wai niko ina abba ya tafi tun dazu, tayi murmushi tace sun fita da sanah na manta ne ban fada miki ba ya shigo kina wanka, uhumm kawai mummy tace ta cigaba da kallon tv amma da gani hankalinta baya gurin kwata2,, kwanan sanah hudu da zuwa gidannan gaba daya ta canza mata sadeeq dinta, ko dayaushe yana like da ita kamar kaska wannan itace damuwar da tayi ma mummy katutu a zuciyarta, shigowarsu rungume da juna shi ya katse ma mummy zancen zucin da ta keyi, ko kadan basu san su mummy na parlon ba, sanah na narke a cikin kirjinshi sai shagwaba take mishi, shi kuma yana biye mata kamar wani dolo, gaba daya sanah ta gama da zuciyarshi, bayajin zai iya kara son wata mace a irin sonta da yakeji a zuciyarshi, bakinshi ya daura kan goshinta ya manna mata kiss yace sorry babie muje in taya ki ajiye kayan sai ki rakani, ta yi murmushi tace yanzu naji magana, suka karaso cikin parlon suna dariya, a hankali ya zare jikinshi da na sanah yana sosa kai saboda ganin mummy zaune a gurin, ko kallonsu batayi ba ta cigaba da kallon tv, sanah ta zo ta dafata tace mummy sannu da gida, yauwa kawai tace ba tare da ta kalleta ba, sanah bata kawo komai a ranta ba saboda ita a gurinta ba wani abu sukayi ba, hannun jalila taja suka wuce ďaki, sadeeq ya zauna gefen mummy yace sannu da hutawa mummy, ko kallonshi batayi ba, Allah ne kadai yasan irin bakin cikin dake ranta, in har aka cigaba da tafiya a haka to tabbas sanah zata jefa mata danta cikin halaka, gara tun wuri ta nemi kimtsatsiyar yarinya irin laila ta aura mishi, Sadeeq ya dukar da kanshi kasa yace mummy magana nake miki, nan ma banza ta bawa ajiyarshi, laila ce ta shigo twins da ayda na biye da ita suna cin apple, tace sannu da hutawa mummy, Mummy tayi murmushi tace sannu maman yara, ta kalli sadeeq da baya cikin walwala, tace abba lafiya, ko dai cikinka bai dauka bane, nasan dai babu abinda zai saka damuwa sai maganar gas, yayi yake yace kaii anty laila wato ma sharrin da kike min kenan ko, tace ba wani sharri sai gaskiya, ka dai kusa tafiya kaje ka dinga cin jagajaga mukuma mu huta, murmushi kawai yayi yana kallon mummy da ta kara hade fuskarta, laila tace mummy me zan dafa ma daddy?, Mummy tace ki dafa kome kika ga ya dace, ay kinsan abubuwan da yafi so, laila tace to mummy ta tashi tana tsokanar sadeeq, sanah ta fito cikin matsatsatsun kaya kamar zasu yage in tayi nishi mai karfi, tace anty laila ashe kina nan, laila ta kalleta sosai tace eh yanzu na fito ina zuwa haka, tace zamu dan kara fita ne, mummy ta mike ta wuce daki ta barsu a parlon, anty laila tace a haka zaki fita, ko dankwali babu, sanah ta yatsine fuska tace wallhy zafi2 nakeji, ta zauna kusa da abba tace muje ko dear, ya kalli anty laila dake musu kallon mamaki ya dan matsa kaďan yace to muje, laila taja hannun su twins suka wuce ciki zuciyarta cike da tambayoyi, matsowa kusa dashi tayi ta fara shafa fuskarshi, murya can kasa yace no sanah ki bari mana baki ganin a gida mu--- bata bari ya karasa magana ba ta tura harshenta cikin bakinshi, irin waďannan abubuwan da sanah ke mishi su ke kara tsumashi cikin kaunarta, nan da nan ya mance damuwar da ya gani a fuskar mummy, kuma ya kasa hana sanah sarrafashi a wannan lokacin, saida ya ji motsin taba kofa sannan ya maza ya janye daga jikinta yana maida numfashi, Nurain ne ya shigo drivern shi na biye dashi da kaya kallon su yayi yadda suke a kasalance a yamutse yasa shi zargin wani abu, cikin sauri ya kauda zargi saboda yasan sadiq bazai taba aikata wani abu na sabon Allah ba, sadiq ya taso yace yaya sannu da dawowa, yayi murmushi yace yauwa abba, yau baka fita ba kenan, yace na fita ban dade da dawowa ba, sanah ta gaisheshi ya amsa mata a dakile dan nurain ya tsani mace mara kamun kai, ga shegen son maza dan shi kanshi tasha kawo mishi hari, amma bai taba barin wani ya sani ba saboda shima ya iya maganin mata irinta, dauke kanshi yayi hade da dan tsaki da ya tuno abinda ta mishi last zuwan da tayi, dakin mummy ya wuce, zaune ya sameta tayi tagumi, ko sallamar shi bata ji ba, saida ya dan taba ta ta ďago ta kalleshi ta kirkiro murmushi tace a'a yaushe ka dawo, ya tsuguna a gabanta yace ban dade da dawo ba mummy, fada min damuwarki dan fuskarki ta bayyana min abinda ke ranki, fada min ko menene in dai har bai fi karfina ba zan nemo miki,, mummy ta kara kirkiro murmushi tace babu abinda ke damuna Nurain me ka gani a fuskata, cikin damuwa yace abubuwa da yawa mummy, ki daina kirkiro murmushi kina daura shi kan fuskarki, komin kankantar damuwa ina ganeta musamman a gurinki mummy, dan Allah fada min damuwarki, tayi ajiyar zuciya, tace ba wata damuwa bace Nurain, kawai dai ina son in sama ma abba matar aure ne, mace nakeso kamar laila ko ma wacce tafita Nurain, banason abba ya auri macen da zata kaishi ga jahannama, wannan ita kadai ce damuwata, Nurain yace wannan ba damuwar da zata dameki bane mummy, ki kwantar da hankalinki kiyita addua, kuma bazamuyi gaggawa ba domin samun natsatsiyyar mace a wannan zamanin sai an nutsu, nima nayi matukar sa'ar dacewa da uwa irinki wacce ta iya dubawa ta hango min mace kamila kamar laila, mummy tayi murmushi tace ai laila daban take Nurain Allah ya bamu wacce zatayi hali ko bai kai nata ba, dan nasan samun mace kamarta akwai matukar wahala, Nurain yace zamu samu mummy wacce ta fita ma,, in shaa Allahu daga abba har farouk sai sun auri kamilallun mata mummy mudai cigaba da addu'a, Ameeen mummy tace sannan addua ay kullum munayi saidai mu kara Allah ya bamu sa'a...... Mrs tijjani shattima... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ●● ZULFAH ●● 9⃣ By Aysha Ya'u kurah Shiri sosai zulfa takeyi, saboda tsabar farin cikin da take ciki yau ko kadan aikin gidan bai mata wahala ba, tun kafin 4 ta tashi ta gyara ko ina, dan yanzu da taimakon Allah da taimakon malam saleem goggo bata yi mata komai, tsakaninsu harara ce daga nesa amma bata gigin dukanta saboda tsabar tsoron abinda kaje yazo, abinci ne dai yanzu ko loma basa bata, sai dai goggo ameena ta bata in ta shiga gidansu , ledar da malam saleem ya aiko mata dashi jiya ita ta dauko ta kwance ta fara fito da kayan ciki, sababin uniform ne da takalmi mai kyau sai turaren tony mantana, cikin murna ta sa kayan bayan ta gama shafa man da ta roko gurinsu fa'ee, uniform din yayi mata kyau sosai tasa takalminta ta feshe jikinta da turare ta kimtsa dakinta ta tsaya tayi addu'oi kafin ta fito, goggo na zaune tana tuyar waina maza sun fara shigowa ta tsugunna ta gaishe ta, goggo ta kalleta sama da kasa cikin bakin cikin da ya kasa boyuwa a fuskarta, ta debo ruwan miya a ludayi tace uban waye dinka miki uniform, salaha dake zaune tace ai harda takalmi goggo, zulfa taga goggo na neman bata mata kaya da ruwan miya, tace jiya malam saleem ya aiko min dashi, gaban goggo ya fadi amma sai ta dake tace ko uban malam salim ne sai in watsa miki ruwan miyan nan inga wace tsiyar za'ayi dan ni bana tsoron uban kowa, ta ajiye ludayin miyar tace Allah ya taimakeki yau banjin bala'i da wallhy bazaki fita ko nan da can ba, rabani da wannan koďaďďiyar fuskar taki ta fadi tana harararta, tayi maza ta tashi ta fita, a zaure tayi karo da bangis, innalillahi kawai take fadi a ranta saboda yadda yayi mata katanga, alamarin BBG shine yanzu babbar matsalarta a rayuwa dan ba karamin matsa mata yayi ba, gyaran murya yayi yace amarya amarya, ta dago kanta ta kalleshi, yace kinsan yau ne daurin aurenmu, jiya nazo tambayarki abinda kike bukata ban sameki ba, marka ta baki sako? Na bata dubu hamsin ayi miki siyayya saboda kurewar lokaci, idon zulfa ya ciko da kwalla, ta kalleshi tana girgiza kanta tayi waje da gudu, gidan su fa'ee ta shiga tana kuka sosai, goggo ameena tace me yasameki zulfa, Zulfa cikin kuka ta fada mata abinda ke faruwa tsakaninta da babangida goggo tasa salati, tace Allah ya kyauta ki auri wannan yaron, ay share hawayenki yanzun nan zanje in samu ado, zulfa tace goggo ko kin sameshi babu abinda zai iyayi, tunda goggo ta karbi kudinshi nasan Allah ne kadai zai kubutar dani daga aurenshi, fa'ee ta gama shirinta ta fito suka haďa baki da goggo sunata rarrashinta, goggo ta basu kosai da koko zulfa ko kadan bata hango ta inda abinci zai bi bakinta har ya wuce makoshinta ba, da kyar suka lallabata taci kosai daya goggo ta kawo mata kwalli tace maza kisa kuma ki nutsu kiyi karatun saukarki, ta daga ma goggo kanta, suka gama shirinsu delu na gefe tana musu habaici, saboda babangida saurayin hanne ne, jiya ma a dakinshi ta kwana, ya gayamata dalilinshi na auren zulfa'u dan ya bata mata rayuwa ne ba wai dan yana sonta ba, wannan dalilin shi ya kwantar da hankalin su hanne dasu goggo marka, A kofar islamiyya suka ga malam salim cikin farar shadda mai kyan gaske, tsugunawa sukayi suka gaisheshi, ya amsa yana kallon zulfa'u, bai taba ganin tayi kyau ba irin yau, yace malamai kuma ďalibai har kun iso, suka daga mishi kansu sama suna murmushi, yace to maza a shiga ciki ayita bitar karatu kafin lokaci yayi, zulfa ta wuce ciki fa'ee ta tsaya ta labarta mishi komai dake faruwa, Fuskar saleem ita zata nuna miki ainihin tashin hankalin dake zuciyarshi,, ya daga kai ya kwala ma zulfa da ke tafiya kamar wacce kwai ya fashe ma a ciki, ta karaso gurin tace gani malam, yace dagaske ne abinda fa'iza ta faďa min, ta kalli fa'iza sannan ta daga kanta tace eh malam, innalillahi wa inna ilaihir rajiun abinda malam ke fadi kenan a bayyane, cikin tsawa yace me yasa baki fada min ba tuntuni, muryarta na rawa tace ban dauka dagaske yakeyi ba, yayi huci mai zafi a zuciyarshi yace ta ina zan fara, lokaci ya riga ya kure, kuma aure ba wasan yara bane, ga mugun sonta da yakeji kamar zai kasheshi ya kasa fada mata, gashi yanzu ko ya aureta bashi da gurin ajiyeta dan matar babanshi azzaluma ce zai iya cewa gara ma goggo marka dan ma shi namiji ne shiyasa kuma bawai zai zauna a gari bane karatu zai tafi, dama ya riga ya tsara musu rayuwarsu tana js3 yanzu yasan zai gama law skull har Allah yasa ya samu aiki yazo ya aureta lokacin ta gama makaranta, yanzu duk plan dinshi sun rushe kenan, idonshi ya kaďa sosai yanata karanto adduoi cikin ranshi, kauda kanshi yayi yace ku wuce ciki, har sun fara tafiya ya kira zulfa, ta dawo, yace dago idonki ki kalleni, a hankali ta ďago kanta suka hada ido tayi maza ta saukesu yace kisa a ranki duk wata matsala da zata dameki to Allah da kuma ni saleem Abdulrahman muna tare dake, wannan issue din ki fitar dashi a ranki ki nutsu kiyi karatunki ta yadda zai gamsar, ki manta da anyi wannan maganar saboda zata zama tarihi in shaa Allah,, Zulfah taji wani dadi a ranta ta tabbatr zai shawo mata kan matsalar,, tace nagode malam ta ruga cikin makaranta tana murna, kallo ya bita dashi, to yanzu ta ina zai fara, yasan halin bbg sarai tunda ya fada sai ya cika, shi kuwa ya dau alkawarin bazai zuba ido yaga wanda zai cutar da zulfa'u ba, ko bai aureta ba zaiso ta sami wanda zai kula da ita sosai, "to waye shi kuma a ina yake," wani sashi na zuciyarshi ya tambaya, , yayi addu'oi sosai sannan yaji duk wata damuwa ta yaye mishi yasan in shaa Allahu kafin karfe biyu ya samu mafita..... Mrs tijjani shattima.. [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ●● ZULFAH ●● 1⃣0⃣ By Aysha Ya'u Kurah A nutse ta gama shiryawa cikin rantsatstsen lace mai matukar kyau ta dauko milk hijab ta saka , parlor ta fito anan ta tarar da nurain yana zaman jiran fitowarta, mikewa yayi, ya dan tsuguna ya gaisheta, ta amsa tace ka dade kana jira ko, yace a'a mummy, laila ta fito ta gaisheta itama ta shirya cikin java holland tasa hijab dinta , yara duk suna islamiyya, anty amarya ta fito daga kitchen suka gaisa da mummy, tace har kun gama shiri, mummy tace walhy ai mun ma kusa makara, tace to sai kun dawo, ta koma kitchen, su mummy suka fita suka wuce, tun suna cikin gida wayar mummy ke kara taki dagawa sai danna reject takeyi, kiran karshe ne anty laila ta kalli screen din taga abba, ta juyar da kanta dan tana sane da irin fushin da mummy keyi dashi tun kafin ya tafi, kuma duk a dalilin sanah, wayar nurain ya kira ya dauka yace abba ya kake, cikin damuwa sadeeq yace lafiya lau yaya, yayi dan tsaki kamar zaiyi kuka yace yaya mummy fushi takeyi dani ko na kirata bata dagawa dan Allah ka bata hakuri ni bansan me nayi mata ba, Nurain yace ok ka bari zan tambayeta sai in kiraka ka bata hakuri, cikin farin ciki yace to yaya nagode sosai, suka danyi hira akan school dinshi sannan ya kashe wayar, Nurain ya waigo ya kalli mummy cikin girmamawa yace mummy abba yayi miki laifi ne, kanta kawai ta girgiza ba tare da ta kalleshi ba tace wani abu yace maka, Nurain yace eh yace wai baki daukar wayarshi kuma baisan abinda yayi miki ba, mummy tace uhumm tunda bai san abinda yayi ba shikenan nima bansan meyasa bana daukar wayar shi, laila ta kyafta ma mijinta ido saboda yadda taga yadda ran mummy ya fara baci, tayi mishi alama da yayi shuru, hakuri kawai ya bata ya juya yana kallon titi, mummy kuwa ta tsunduma cikin tunanin yadda sanah tayi ma ďanta qawanya cikin zuciyarshi da kissarta da yaudararta, in ta tuno abinda ta kamasu sunayi ana gobe zai tafi har kuka takeyi, wai sadeeq dinta ke rungumar mace har saboda ficewar hayyaci yake fada mata duk duniya babu macen da yakeso kamarta kuma bayajin zai iya son wata bayan ita, sanah harda kuka tana fadin to idan mummy ta nemo maka mata kamar yadda tayi ma yaya nurain fa, ni gaskiya inada kishi sosai in har kayi aure to walhy bazan aureka ba, ya kara rungumeta yace ni ba yaya nurain bane baby, babu wanda ya isa yayi min aure bada son raina ba, kima daina wannan maganar, mummy ta runtse idonta cikin bacin rai tace zaka ga isata akanka abba, idonta ya soma canzawa kuma ya ciko da kwalla, dai2 lokacin sukayi parking a islamiyyar "Abdulrahman bin Auff" Nurain ya fito da sauri ya bude ma mummy ta fito ta boye bacin ranta ta kirkiro murmushi tace sannu Nurain yayi murmushi yace yauwa, malam saleem ta hango yana tahowa kusa dasu da sauri yana murmushi, ya karaso ya tsuguna ya gaisheta ta amsa tana murmushi suka karasa cikin makaranatar lokacin har ďalibai sun fara karatu, guri na musamman aka bawa mummy suka zauna tare da anty laila, Dalibai aka dinga kira suna karatunsu kowa cikin kwarewa, kirarsu ma mai dadi dukansu, daga wata "Amina rabi'u" sai aka kira ZULFA'U ADAM, da sauri malam saleem ya xagoyo ya tsaya saitin munbarin, ta fito cikin nutsuwa ta hau kan mumbari, hada ido sukayi dashi yayi mata murmushin da ya kara mata karfin gwiwa, cikin sanyin murya tayi "mukaddma" sannan ta fara karatunta cikin kira'a mai dadi, sanyin muryarta da yadda take bawa ko wani harafi hakkinshi shi ya burge duk wanda yake gurin, mummy gaba daya ta kasa dauke idonta akan yarinyar, duk wadanda sukayi karatu a gurin babu wanda ya burge ta kamar yarinyar, gashi an bata surar da mummy keso kuma take bitarta a kullum suratul Nisa'i, mummy bata san lokacin da yarinyar ta sauka a kan mumbari ba, sai jin karatun wata tayi itama cikin nutsuwa takeyi, gaba daya daliban sun burge mummy, har aka gama karatun aka rabawa yaran shahadarsu mummy na yabawa yaran a ranta, Kiran dalibin da yazo na farko a maza akayi mai suna "Musa Ahmed" yaron yasha kyaututtuka sosai, sannan aka kira wadanda sukazo na farko a mata su biyu ne Marks dinsu daya, Zulfa'u Adam Da Bilkisu Nabayi, a tare suka fito cikin murna suma sun sha kyaututtuka harda envlp din kudi aka basu, zulfa ta kasa boye murnarta sai dariya takeyi, Mummy nata kallonta, laila ta lura da mummy sosai, dan ta faranta mata rai yasa tace yarinyar can ta burge ni mummy, mummy ta washe baki tace ashe dai bani kadai ta burge ba, yarinyar ta shiga raina laila, muryar wasu mata a bayansu sukaji suna maganar irin wahalar da marka ke ba zulfa, dayar tace ay laifin duk na ado ne dama mace in taga gida nata ne kuma kana zaune baka tabuka komai sai dai tayi sana'a ta ciyar da kai ai dole ta rainaka, dayar tace Allah sarki dije ai halin marka sai wadanda suka santa, ta rage murya tace bakusan da kudinshi ta siya gidan ba, ita fa ta sace kudinshi lokacin da ya tara zai siya gida, kuma tasa aka rufe mishi baki, shima ba a son ranshi yake zaune a gidan ba dan dai tafi karfinshi ne, Amara tace ni fatana ma Zulfa'u tasamu miji tayi aure tabar musu gidan taje ta huta da wahalar marka, mummy ta nutsu ta gama sauraronsu, tausayin yarinyar ya shigeta sosai, tana hangota tana dariya da ganinta tana cikin farin ciki, ta mika ma saleem komai na hannunta shima sai murna yakeyi, kusa da malam ado salim yaje ya mika mishi shahadarta da kudin, kuka ya fashe dashi saboda kofar gidanshi na can cike da su bangis da mahaukatan iyayenshi suna jiranshi yazo a daura aure; salim yace baba murna zakayi ba kuka ba, malam ado yace kukan rayuwar da Zulfa'u zata fada nakeyi, ka taimakeni salim, ka taimakeni a cikin malamanku kayi ma wani magana a daura mata aure dashi yanzun nan kafin jama"a su watse, kaga idan aka daura aurenta dole su Alhaji mati su hakura su tafi, saleem ya shiga cikin tashin hankali, ya kalli mahaifinshi dake zaune a gefe shima cikin damuwa, mummy ce ta karaso gurin lokacin da taji furucin mahaifin zulfa, ta kalli saleem tace malam, in har banyi muku katsalandan ba, inaso a aurawa sadeeq dina yarinyar da naji kuna magana, saleem gabanshi ya tsananta bugawa zuciyarshi ta karye, ya zaiyi da son da yake ma Zulfa'u, da ya tuno da gidan da zata je kuma yasan wacece Haj Aisha nan da nan ya kauda duk damuwar dake fuskarshi ya kirkiro murmushi yace Alhamdulillah hajiya mun gode wallhy kin taimakemu a lokacin da muke bukata, malam ado ya kalleta kamar an mishi albishir da gidan aljanna, suka dinga mata godiya tace ay nice zanyi muku godiya, yanzu bari in kira yayanshi yazo ayi magana a daura auren ko, liman yace kwarai kuwa ay bazamu bata lokaci ba, Mummy tasa laila ta kira nurain, da sauri ya fito daga mota ya shiga cikin makaranatar, mummy tana murmushi ta fada mishi abinda ke faruwa, yayi ajyar zuciya yace to mummy bari in kira daddy in fada mishi, tace to maza ka fada mishi, ya kira daddy ya fada mishi, daddy yayi dariya yace Aisha case, to ni me zance kaima uba ne a gurin shi, Allah ya sa alkhairi ce a cikin familyn mu, nurain ya ji dadi sosai yace Ameen daddy sukayi sallama ya kashe wayar, ya fada ma mummy abinda yace, mummy tace to madalla muje ka basu sadaki sai a daura auren mu wuce da amaryar mu, Nurain yayi mamakin yawan farin cikin da ya gani kan fuskar mummy, ya karasa kusa dasu liman ya zaro dubu 100 ya mika musu yace ga sadakin nan, suka amsa liman yayi adduoi duk malaman dake gurin suka taru guri daya aka gabatar da daurin auren kamar yadda musulunci ya tanadar, bakin mummy ya kasa rufuwa ta dinga rabon kudi a gurin, ana gama daurin auren wani malami ya je kusa da speaker ya sanar ma da mutane, dukka mutanen gurin mamaki ne a kan fuskokinsu, saleem office ya shiga ya daura kanshi a kan table zuciyarshi kamar zata buga, har aka gama komai zulfah bata san wainar da ake toyawa ba tanacan cikin kawayensu,, Mrs tijjani shattima... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ●● ZULFAH ●● 1⃣1⃣ By Aysha Ya'u Kurah Labari tuni ya cika "babbar saura," murna yan unguwar suka dinga yi, barin goggo ameena har sujjada tayi tasan duk wata wahalar zulfah ta kare tunda an ce mata masu kudi ne ko babu komai zulfah ta shiga daular duniya, ta dinga jero mata adduo'i kamar tana gabanta, Marka na zaune dasu delu an ci gayu cikin kayan da ta ragargazo cikin kudin bangis suna zaune suna kulla mugun abu shewa kadai ke tashi suna zaman jiran dawowar malam ado da zulfah a daura aure, shigowar bangis gidan kamar zaki shi ya katse musu shewar da sukeyi, marka ta tashi da sauri ta matsa kusa dashi tace ango lafiya na ganka haka, wani gigitaccen mari ya kai mata wanda ya dauke jinta na yan sakwanni, tayi ihu taja da baya rike da kunci, delu tace innalillahi babangida me ya faru ne, saida yayi mata mugun kallo sannan ya fara magana cikin karaji, ni za'a raina ma wayau, kun sanni marka kunsan bana ďaukar rainin hankali, wallhy tun wuri ki fito min da duk kudaden da na baki ko kuma inyi miki abinda babu wanda zai ganeki, Marka da har yanzun zafin mari bai saketa ba tace ni bangane abinda kake nufi ba, bangis yace yanzun nan zaki gane, ya karbi wata karamar wuka a hannun laminu yayo kanta suka sa ihu dukansu suka arce daki, mazan dake kofar gidan su suka shigo da sauri suka bi bangis da kamar ba'a hayyacinshi yake ba, har daki ya bisu mazan suka rikeshi ya dinga tirjiya yana zagezage, dakyar aka fita dashi zaure, marka dasu delu gaba dayansu sun fita a hayyacinsu, saida aka fitar dashi sannan delu ta ďago a hankali ta kalli mutanen dake dakin a hankali tace wai me ya faru ne mu kun barmu cikin duhu, wani a cikin mazan yace ai yau marka kun tabo babangida ya za'ayi ya biya kudin aure ya tara jama'a sannan aje a daura mata aure saboda tsabar kun raina mishi hankali, goggo marka ta mike da sauri tace aureee? Mutumin yace kwarai kuwa aure ga labari nan ya zaga ko ina, saboda haka tun kafin bangis yayi miki rashin mutunci ki bashi kudinshi in ba haka ba wallahi zai muku iya wuya,,, Marka tasa salati hade da kuka tace ado ya cuceni, wallhy bansan an shirya wannan munafurcin ba, na shiga uku ni marka yanxu ta ina zan fara bawa bangis kudinshi, kuka sosai takeyi tana aibata malam ado tana fadin har abada shi da gidan nan wallhy yau sai ya rabu da ita, ta dinga tsine mishi, ai marka bata kara haukacewa ba saida aka fada mata zulfa a gidan masu kudi tayi aure, wani yaron dake gurin saukar ya fito da dubu uku a aljihunshi yace sirikarta tanata raba kudi marka, nima kinga wanda nasamu, sannan naji ance ďan shugaban sojojin sama na nigeria gaba daya ta aura, Marka da hassada ya mai da idonta kanana, kirjinta yayi nauyi tana masifa karshe ta fashe da kuka sosai, zuciyarta kamar zata buga lallai ado ya munafurceta, ga salaha a gida bai bada aurenta ga masu kudi ba sai zulfa yarinya karama, lallai yau ta kara tabbatar da ado baya kaunarsu yafi son saude da yarta, bangis ne ya sake shigowa tare da zugarshi da suka gama bashi baki da shawarar ya auri salaha a madadin kudinshi, ya na shigowa marka ta katse kukan da takeyi ta boye bayan delu da ke zaune kamar matacciya, Wani abokin bangis yace marka ki fito kizo ki sa wani yayi wakilcin yarki salaha, bangis zai aureta a madadin kudinshi, marka ta kalli fuskar bangis taga irin mugun kallon da yake musu, salaha kuwa murna ta cikata kamar anyi wata wahayi zata shiga aljanna, hanne ta mike da sauri tace wace salahar, laminu ya harareta yace salaha nawa ne anan gurin, hanne idonta yayi jawur tace walhy bazai yiwu ba, ni zaka ci amana bangis, to wallhy tallahi yau za'a uwar watsi a gidan nan sai dai kowa ya rasa ta daura dankwalli a kugu tana girgirza, Sai a lokacin marka ta samu karfin gwiwar mikewa dan taga hanne na neman yi musu salalar tsiya, (sai kace bangis din mutumin kwarai ne mtswww) tace ke hanne kinci ubanki bangis din kike fadawa magana, dan yace zai auri salaha shine kike bakin ciki to sai ya aure ta din, haba ay nan delu ta kara kaiwa bango ta mike suka dinga cacar baki kamar zasu ci kansu, duk irin hakurin da ake basu a gurin suka ki yin shiru sai tonetone sukeyi ma junansu, salaha dai ko ajikinta dan waje ma ta fita neman babanta ko yaya kabiru, lokacin da suka shigo tare da kabiru da ta ganoshi gurin mai shayi, bangis na tsaye a tsakar gida yana rarrashin hanne rarrashi na musamman wanda ya kwantar mata da hankali, yace kiyi hakuri ay kinsan duk duniya babu wacce nakeso kamarki, ki bari in aureta in ci kudina kema sai in aureki mu hadu muci kudin tare ta hanyar bata wahala, salaha taji kamar zata mutu dan takaici amma saboda zuciyar kare da kwakwalwar kifi gareta sai ta basar a ranta tace ai in na aureka dole in koyar da kai yadda zaka soni, ta wuce ciki tana ma hanne gwaloo, Bayan kurar fadace2 ta lafa duk mazan suka fita waje aka je aka gabatar da daurin aure hanne da delu gida suka wuce suna kulle kullensu, goggo amina dai ko kallonsu batayi ba ta cigaba da gyaran kazar da ta siyo a kudin da aka bawa fa'ee tana yi tana wakar da ya kara kular dasu amma sun kasa tanka mata,, Malam ado bai dawo gida ba sai bayan magriba lokacin motar daukar amarya tazo har sun wuce ya bi motar da kallo, kabiru ya fito daga cikin gida yace baba yanzu ka karaso ya kalleshi yace eh kabiru, motar waye waccan ta bar kofar gida, kabiru yace uhunm salaha aka daura ma aure da bangis shine suka zo daukarta, ya bawa babanshi labarin duk yadda abin ya faru, malam ado yayi ajiyar zuciya yace to Allah ya basu zaman lafiya, kabiru yace ameen, suka danyi hira ya bashi labarin yadda akayi auren zulfah kabiru yayita murna yace itama Allah ya basu zaman lafiya gaskiya naji dadi baba, malam ado yayi murmushi yace nima haka kabiru suka karasa ciki, Sun sako kafarsu kenan marka cikin tsawa tace dakata2 ta mike da sauri ta isa gabanshi ta nuna shi da yatsa, tace yanzu ado kai har kana da idon da zaka kalleni, har kanada kwarin gwiwar da zaka shigo min gida, to wallhy kaji na rantse tunda har baka kaunata nima bana kaunarka, ka sauwake min aurenka kaje can ka karata da wahalarka, in ma gidan zulfan zaka koma su baka mazauni to amma dai kai da zama a gidannan har abada tunda ba tare da kai muka siya ba, ta wurgo mishi ledar kayanshi tace ban takadda, kabiru ya tsuguna cikin bacin rai yace haba gog-- ta katseshi tace zan tsine maka albarka dan ubanka, malam ado yace yi shiru kabiru, ya karbi ledar kayanshi yace to zan tafi marka in har na zalunceki Allah ya saka miki, in kuma ke kika zalunceni Allah ya sa hakkina ya hanaki sukuni, yasa kai zai fita ta biyoshi tana masifa tace takaddar fa, yace zan bayar a kawo miki, tayi shewa tace tafi nono fari matsiyacin banza kawai, har sukayi nisa da kabiru suna jiyo masifarta, A dai2 masallaci suka zauna kabiru yana kuka yace to baba ina zaka je, malam ado yace zan kwana cikin masallaci da safe in wuce kano ina son in cigaba da sana'ar da na bari ne, kabiru yace to baba kanada kudi ne, malam ado yace eh ina dashi ya fito mishi da dubu 200 yace dubu dari sadakin zulfa ne, sai wannan kyauta sirikarta ta bani, kaga ya isheni in yi duk sana'ar da zanyi, kabiru yace kwarai kuwa baba amma tare zamu tafi in dinga taimaka maka dan zaman bazai yiwu mana ba gara mu hada hannu, malam ado yaji dadi sosai yace gaskiya kayi tunani sai kaje ka kwaso kayanka kuma ka sallami mahaifiyarka ya bashi dubu 5 ya kai mata, kabiru ya tashi ya wuce cikin farin ciki dan dama ya gaji da zaman banza..... Mrs tijjani shattima... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ●● ZULFAH ●● 1⃣2⃣ By Aysha Ya'u Kurah Zulfa'u na zaune cikin mota a takure, anty laila na dan janta da hira jefi2, sai dai tayi murmushi kadan, amma a tsorace take sosai saboda rashin sanin inda zasu, in ta tuno malam saleem yasan su sai hankalinta ya dan kwanta, Mummy ta kalli laila tace yamma tayi laila da kunje shopping kin siyo mata duk abun da bata dashi amma gobe da wuri sai ku fita ko, cikin girmamawa laila tace Allah ya kaimu mummy, Kallon unguwar zulfa takeyi tsoronta ya kara zurfi saboda bude wani tankamemen gate da akayi tun daga waje taketa kalle2, hankalinta a tashe sojoji suka bude musu kofa suna sara musu, idon zulfa ya ciko da kwalla anty laila tace fito muje mana, ta fito a hankali suka jera suna tafiya har cikin gida, sanyin kamshi ne ya daki hancin zulfa da aka bude kofar, anty laila ta kamota suka bi bayan mummy suka shiga da sallama, twins suka rugo da gudu suka dane jikin mummy, ayda na bacci a gefen anty amarya, mummy ta saukesu tace nagaji dayawa ku bari in huta ko sweeries, suka daga kansu suka koma jikin anty laila suna bata labarai na shirme, Anty amarya ta kalli mummy da ta zauna tana maida numfashi tace kun dade yaya, da har zan bi sahu ta fadi cikin zolaya, laila suka karasa cikin parlon zulfa ta tsuguna ta gaida anty amarya, ta amsa tana murmushi tace wannan yar kyakyawar fa laila a ina kuka samota, mummy tayi murmushi ta kalli laila tace kuje ciki laila, ki kaita ďaki daya a bangarena kisata tayi wanka, anty laila tace mummy wai da mu tafi side dina in tayi wanka sai taci abinci anjima sai in kawota dakinki, mummy tace to ba laifi duk yadda kikayi Allah miki albarka, tace ameen taja zulfa suka wuce bangarenta tare da twins, Mummy ta kalli anty amarya tace yarinya na samo a gurin sauka, yarinya marainiya kuma mai hankali, gata abin tausayi, ta kwashe duk labarin zulfah wanda taji ta fada mata, anty amarya ta dinga gyada kai cikin tausayi tace Allah sarki har naji tausayinta, mummy tace kedai bari yarinyar ta shiga raina lokaci guda shiyasa na nema wa abba aurenta saboda nutsuwarta kuma an bashi har an daura auren, ba anty amarya dake zaune ba hatta jalila da sanah da suka dawo daga garden lokacin saida suka girgiza, jalila ta kalli sanah da idonta yayi ja sannan ta zagayo ta gaban mummy, tace mummy wani abban, mummy ta harareta tace inada wani abba da ya wuce sadeeq ne, sanah ta ruga daki da gudu zuciyarta na tsananin bugawa gaba daya ta nemi kuka ta rasa, Anty amarya tayi kokari matuka ganin ta boye bacin ranta amma ta kasa, saboda sau biyu kenan mummy tanayi mata haka, tun akan nurain da taso kanwarta Aneesah ta aura har sun gama magana da daddy, kawai washe gari mummy taje ta auro mishi yar aminiyarta, anty amarya ta kalli mummy ta kirkiro yake tace Allah ya sanya alkhairi, mummy tayi murmushi tace ameen a fili amma a zuciyarta tace sai dai ranki yayita baci, ta mike tace bari in dan watsa ruwa bata jira jin amsar ta ba ta wuce hanyar sama tana kwala ma jalila da tabi sanah daki kira, jalila ta fito da gudu tabi mummy samah,,, Anty amarya zaune a dakinta tana rarrashin sanah dake kuka kamar ranta zai fita, dan mummy ta rikirkita mata plans dinta, wayarta dake gefe tanata faman kuka tasan sadeeq ne amma ko kallon wayar batayi ba, kiran ya ishi anty amarya ta dauki wayar,, '"Hello" tace babu dariya a fuskarta, daga daya bangaren jikin sadeeq har rawa yakeyi ya dauka sanah ce ta dauka, yace sweet baby menayi haka kika zabi ki yi min irin wannan ukubar, kinsan in banji mur--- anty amarya ta katse shi da cewa ba ita bace abba nice, yayi murmushin jin kunya yace anty ina wuni, lafiya kadai tace mishi, yace anty sanah bata da lafiya ne, cikin kissa anty amarya tace lafiyarta kalau, ka saurareni da kyau abba, daga yau karka kara kiran layin sanah, kayi biyayya ga zabin mahaifiyarka, ka bar sanah itama Allah ya hada ta da mai sonta, cikin kidimewa yace anty ban gane abinda kike nufi ba, ta rage muryarta ta fara ďan kukan munafurci tace abba bansan me yasa yaya bata kaunata ba, duk irin biyayyar da nake mata bata gani, a kullum burina in hada zuria daku amma yaya sam bata kaunar hakan, anyi na aneesah ya wuce ban damu ba, saboda shi dama nurain bai ce yana sonta ba, amma yanzu kowa yasan irin soyayyar da kukeyi da sanah har muna fatan kuyi aure shine yaya tayi ma sanah wulakanci sosai akanka har karshe taje ta auro maka wata yarinya yar talakawa wanda basu gaji arziki ba, irin yaran da burinsu su aureka ka mutu suci dukiya, ta kara fashewa da kuka tace Allah ya sani inason jinin yaya Aisha da jini na, saboda ban haihu a cikinku ba shiyasa nakeson wani ya auri jinina in ya haihu ko na mutu baza'a manta dani ba, sadeeq ya kara rudewa yace anty dan Allah kiyi shuru waye ya fada miki wannan maganar, ya za'ayi ayi min aure ba tare da sanina ba, anty amarya tace walhy da gaske ne abba, amma kayi hakuri kayi ma mahai--- karki ce inyi mata biyayya anty ya fadi cikin daga murya kamar zautacce, yace wallhy bazanyi biyayya akan abinda zai cutar dani ba, yanzun nan zan kira mummy ta warware auren da ta dauko ma kanta, da sauri anty amarya ta katse shi cikin kwarewa a iya bariki tace karkayi haka, ka nuna musu bakasan zancen ba in ba su suka tare ka dashi ba, in ba haka ba ni zaka jawa masifa kasan banason duk abinda zai bata ran yaya ta karasa fadi tana kanne ma sanah ido, dan tasan sadeeq ya shiga tarkonta.... Mrs tijjani shattima... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ●● ZULFAH ●● 1⃣3⃣ By Aysha Ya'u Kurah A hankali yace to anty amma dan Allah kuyi hakuri, tace babu komai kaima Allah ya baka hakurin juriyar rashin sanah dan tausayi kuke bani dukkanku, gata nan banda kuka babu abinda takeyi, kuka ne kadai sadeeq baiyi ba, yace bazan iya rabuwa da ita ba anty, ko me za'ayi sai dai ayi wallhy dan sanah ta zama wani bangare a zuciyata dan haka ki ma daina wannan maganar, anty amarya tace dole kayi hakuri da ita ab-- ya katseta da sauri yace anty bani sanah pls, tayi murmushi dan tasan sanah ta diga mishi dafinta mai wuyar goguwa lallai ta samu damar aiwatar da kudirinta ta hanyar sadeeq, ta kwantar da murya tace bazai yiwu kayi magana da ita ba kayi hakuri kawai Allah ya hada kowa da rabonshi tayi saurin kashe wayar tana murmushin mugunta, ta kashe wayar gaba dayanta, ta kalli sanah tace mun kama sadeeq sanah, tabbas zai bijire ma mahaifiyar shi, ni kuma zanyi ta hura wuta ta a can kasa tsakanin dukansu ukun, daddy, mummy da shi sadeeq, wannan karan sai nayi nasara akanta dan haka gobe ki shirya ki tafi kuma karki kara daukar wayarshi ke kima canza layi nasan bazai jure ba zai biyoki, ke kuma sai kisan yadda zakiyi ki rikita shi ya dawo ya saki waccen sauran yunwar, kinga anan komai zai dagule sai insan yadda zanyi in jawo abba jikina ta yadda zamu cin ma burin mu, sanah ta share hawayenta tayi murmushin jindadi zuciyarta tayi sanyi dan bata jin zata iya rayuwa ba tare da sadeeq ba... ****** Sadeeq juyi kawai yakeyi wani abu ya tokare mishi maqogoranshi, kuka kawai yakeson yi amma ya kasa, meyasa mummy zatayi mishi haka, wace irin mace mummy ta aura mishi? Tambayoyin da ya dinga yi kenan ya kasa samun amsoshinsu, yayi huci ya daga murya yace gaskiya mummy sai dai kiyi hakuri amma bazan iya zama da macen da bana so ba, shi a tsarinshi yafi son mace wayayya mai aji amma shi sam bazai iya zama da irin macen da mummy ke kwaso musu ba, yayi tsaki ya kara kiran layin sanah karo na na ashirin da uku ya kara jinta a kashe, ya wurgar da wayar ta fadi ta fashe ya buga hannunshi a bango yanajin wani irin zafi a ranshi, bazan iya jure wannan punishment dinba bazan iya baaaa ya fadi da karfi, dole ya nemi hutu ya dawo gida yayi solving problems dinshi, dole ya ganar da mummy kowa yanada yancin yin abinda ya keso, ya wuce bayi a fusace ya sakar ma kanshi ruwa yanajin tsanar duka yan gidansu saboda suna neman rabashi da ruhinshi, bazai kara nemansu ba sai dai kawai su ganshi... lailah tsaye gaban mudubi tana tsefewa zulfa kanta da yayi mugun datti, tanayi tana goge hannunta saboda dauďar tayi yawa, tace ke kuwa yaushe rabonki da tsifa kinga kanki yanda yayi datti ya cukurkuďe, zulfa tayi murmushi cikin kunya tace hmmm kawai, laila na gama mata tsifa ta taje mata tayi mata parking dinshi a tsakiyar kai, laila tace gaki da gashi amma saboda rashin gyara ya dunkule guri ďaya, shi kanshi ya galabaita ta fadi tana dariya, zulfa tayi murmushi a ranta tace inata kaina wake ta gashin da na manta rabona da budeshi, anty laila tace tashi ki cire uniform din nan muje in nuna miki komai na bayi sai kiyi wanka a kaiki saloon, ta mike tace to, sun kusa da bayin jalila ta shigo da sallama, anty laila ta amsa tace jalee ina kuka shiga ne, jalila ta ajiye doguwar rigar da mummy ta bata bayan ta gama mata tatass kuma tace tazo gurinsu lailan ta dinga Jan zulfa'u a jiki, ta kalli anty laila tace muna garden ne, tayi murmushi tace amaryar yaya abba sannu, zulfa ta tsuguna tace ina wuni, jalila ta kwashe da dariya tace tashi ni ba ruwana kar ki kara tsuguna min kisa mummy ta yi punishing dina da fushinta, laila tayi dariya tace ai fa, ta ďago zulfa suka wuce bayi, jalila ta rike baki tana mamakin mummy, yarinyar tana da kyau amma tayi karama da yawa, yadda yaya abba keji da kanshi, yan mata masu aji ke kawo kansu ya kare a wannan kucakar, lallai akwai bala'i in ya dawo, ta kwantar da kanta kan kujera..... Mrs tijjani shattima... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ●● ZULFAH ●● 1⃣4⃣ By Aysha Ya'u Kurah Washe gari tun kafin asuba zulfah ta farka saboda ta riga ta saba lokacin nayi bacci zai kauracewa idonta, ta dinga bin dakin da aka kaita ta kwana da kallo karo barkatai dan tun da aka shigo da ita take kare ma dakin kallo barin toilet din da yaji kayan gyara, Tashi tayi a hankali ta shiga bayin tayi tsarki ta kunna ruwa kamar yadda jalila ta nuna mata tayi alwala, tsayawa tayi gaban mudubin bayin tana kare ma kanta kallo, sai da ta dan dade sannan ta fito ta shimfida dadduma tayi nafila kafin a kira sallar asuba,, karantun qur'ani ta dinga yi da "ka" batare da ta duba qur'ani ba, har aka kira sallah tana karatu tana idarwa ta mike tayi sallah, ta zauna tana addu'oi tana tuno rayuwarta ta baya, ko yanzu me goggo takeyi tasan tana can tana aikin waina, haka ta dinga tunanin su goggo da salaha da babanta, ta share kwallar da ta digo mata a idonta ta karasa adduointa ta nade daddumar ta maida ita mazauninta, Kofar dakin taji an bude ta waigo suka hada ido da mummy, ta karaso ciki itama da hijab da carbi a hannunta tana murmushi, zulfah ta durkusa da sauri tace ina kwana, mummy ta dagota tace lafiya lau zulfa'u ya kwanan bakon guri, zulfah ta sunne kanta tace lafiya lau, mummy tace to alhamdulillah ki saki jikinki kema yar gida ce, banason wannan dari darin da kikeyi, da ke da laila da jalila duk daya kuke a gurina, saboda haka ki daukeni matsayin uwa kinji, Zulfah tace to in shaa Allah, mummy tace yauwa diyata, bari inje daki kema ki kwanta ki huta kafin a kawo miki abin kari, zulfah tace to, amma babu wani aikin da zanyi, mummy tace a'a je ki kwanta ki huta kinji, zulfa ta gyada kanta ta koma ta zauna bakin gado, Gurin karfe 9 jalila ta turo kofar dakin, lokacin zulfah na tsaye tana goge jiki, ta juyo da sauri zata tsuguna jalila ta hade rai tace tashi2, wai so kikeyi kija min bala'i ne, na fada miki karki kara tsuguna min bakiji ba ko, ki rufamin asiri mu dinga gaisawa daga tsaye, kuma ki saki jikinki kinji? Zulfah tace to, jalila tace yauwa, yanzu ki shirya ki fito mu karya ta ajiye mata doguwar riga a kan gado ta fita, zulfah ta duba rigar taga katuwa ce irin ta jiya, har kasa take kai mata, ta koma gaban madubi, mai kadai ta shafa ta dauki rigar ta saka ta rufe kanta da gyalen ta sakko parlon, a bangaren dining taga mummy da jalila suna zaune suna hira, karasawa tayi ta tsuguna ta kara gaida mummy, mummy tayi murmushi tace ai mun gaisa zulfa'u tashi ki zauna anan, ta nuna mata kujerar kusa da ita, zulfa ta zauna cikin jin kunya tana ta sinne kai, jalila tayi srvn dinsu mummy da kanta ta hada ma zulfa tea mai kauri ta tura gabanta tace maza ki shanye duka, zulfa tace to, da kyar kunya ta barta ta fara cin dankali da sauce din hanta, a tare suka gama karyawa dukkansu, mummy ta koma cikin parlon ta zauna, zulfa ta taya jalila kai kaya tsaftataccen kitchen din da kamar ba anan ake girki ba, fatsin ce tsaye a ciki tana wanke2, zulfah ta karasa kusa da fatsin tace kawo in tayaki, fatsin ta wage baki tace a'a jeki abinki ay na kusa gamawa, zata kara magana jalila taja hannunta tace zo mu tafi ciki mummy zatayi fada in taga kina aiki, parlor suka wuce zulfa ta rabe gefen kujera, mummy tayi murmushi a ranta tace da sannu zaki saki jiki, sai da suka dan dade sannan mummy tace zulfah ajinki nawa a school, zulfa tace js3 nake zan shiga ss1, mummy tace wace makaranta kikayi, ta kara sunkui da kanta tace nayi l.g.e.a unguwar rimi dana gama malam salim ya samo min capital school, mummy tace gud, kina sha'awar cigaba daga ss1 din, jalila tayi dariya tace haba mummy me zai hana tayi sha'awa, ai kawai gara in anyi resuming ta dinga zuwa ko, mummy zatayi magana shewar da taji ta katseta, daga kanta tayi taga sanah janye da trolley anty amarya rike da jaka, har suka karaso cikin parlon basu kalli inda su mummy suke ba sai hirarsu sukeyi suna dariya, sai da suka zo dapp dasu anty amarya tayi murmushn rainin wayau tace yaya ina kwana, mummy da mamaki ya cika ta tace lafy lau, sanah ta kara gyara dankwalinta tana kallon zulfa'u tana kas kas da cingam, ina kwana zulfah ta fadi hade da kara tankwashe kafa, suka mata kallon uku saura kwata, sannan sanah ta kwashe da dariya harda rike ciki, anty amarya ta dake cikin kissa tace banason iskanci wuce mota gani nan, ran mummy ya baci sosai da abinda sanah tayi mata dan ko gaishe ta batayi ba, anty amarya tace yaya bari in kai sanah gidan aneesah, mummy tace to a dawo lafiya, bata jira jin abinda zata ce ba ta kalli jalila tace tashi kuje gurin laila in ta gama kuzo ku tafi shopping din, jalila tace to mummy suka mike suke wuce side din laila, mummy ta mike tayi hanyar sama ta bar anty amarya tsaye tana hararar bayanta, sai da ta gaji dan kanta tayi kwafa ta wuce waje tana sakar zuci.... Mrs tijjani shattima.... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 1⃣5⃣ By Aysha Ya'u Kurah Sai gurin 11 suka fita, saloon suka fara zuwa aka wanke mata kanta da kafa, daga nan suka wuce kasuwa sukayi siyayya sosai, atamfofi, laces da material takalma sai sarkoki, sun kashe kudi sosai a kasuwa, a hanyarsu ta komawa gida suka biya passion trust suka kwaso mayuka da turaruka masu kyau da tsada, zulfa dai kallonsu kawai takeyi kamar basu jin zafin kudin haka take fadi a ranta, "senegls" nan suka je karshe inda tela ya gwada zulfah, jalila tace kayi mata styles masu kyau fa, ina material dina, yace saura kadan kinsan aikin akwai wahala, tace haka dai ka ke cewa ka iya yawa wollah, yaushe zaka kawo wadannan to, yayi jumm sannan yace tunda express ne kuma kunce Inji mummy zan gama nan da 1mnt, anty laila ta rike baki tace lallai Hayatu baka da m, ka bari sai nan da shekara daya ma wannan kai da mummy, Hayatu yayi dariya yace anty kayan da yawa zanyi kokarin gamawa cikin 1wk in shaa Allah, anty laila tace now u r talkn, jalila tace Allah yasa dan ban yadda ba, hayatu yace aiko zan baki kunya, tace da dai wani ne bakai ba, ta fita tana dariya... Sai yamma likis suka dawo gida a gajiye, anty amarya suka tarar zaune a parlo tana waya da sadeeq itama dawowarta gidan kenan, sannu da gida suka ce mata gaba dayansu sannan sukayi hanyar dakin mummy, tayi tsaki mai karfi ta cigaba da wayar da takeyi, sadeeq yace anty ke da wa kike tsaki kuma, tace ni da wadannan kitifaffun mana, wai daukar wannan yar kauyen sukayi suka yo mata shoppn, jalila harda rungumeta saboda munafurci, yayi tsaki yace duk zasu gane kurensu anty, ina nan dawowa nan kusa zan warware duk kullin su, ni dai dan Allah ki taimakeni ki fadamin numbr da zan sami sanah, wallhy ina cikin tsananin damuwa, Tayi murmushin mugunta tace abba kayi hakuri da maganar sanah, ni banason tashin hankali, karka kara kirana ma bare ayi tunanin ni ke zuga ka, cikin damuwa yace haba anty, so kikeyi in mutu ko kuma wani ciwo ya kamani, wallhy na kasa maida hankalina a karatu, kirjina zafi yake min, meyasa sanah zata hukunta ni akan laifin da bansan dashi ba, Anty amarya zuciyarta wasai dan taga alamun daga zuciyarshi yake fadin wadannan kalaman, a hankali tace dukkanku hakuri zakuyi, dan itama sanah tana can bata ko iya cin abinci, Cikin damuwa yace can ina anty, tace ta tafi ay, muryarta ta dan fara rawa tace yau tun safe yaya tayita zaginta akan yarinyar nan, zagi sosai tayi mata har jalila na sa baki, Sadeeq ya dafe kanshi yama rasa me zece, shurun da anty taji ne yasa tace kana jina abba, uhmm kawai yace mata, tace kayi hakuri kayi ma yaya biyayya, ka cire---- sallamar nurain ce ta katse mata maganar, tayi saurin kashe wayar suka gaisa cikin sakin fuska, sai da yayi gaba tabi bayanshi da harara, aladar anty amarya kenan kowa a gidan haka take mishi sai kun gaisa ko kun gama magana da ita cikin sakin fuska sai tabi bayanka da harara, ta tsani yaran gidan da mahaifiyarsu amma saboda tsabar iya bariki da kissa babu wanda yake ganewa dan nunawa takeyi tafi son su akan mahaifansu, wannan dalilin yasa daddy yake girmamata saboda tana nuna ma ya'yanshi da matarshi so da kulawa ta karya, ta dade tana neman dalilin da zai haddasa fada a gidan sai yanzu ta samu wannan damar daga gurin sakarai sadeeq.... Mrs tijjani shattima.. [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 1⃣6⃣ By Aysha Ya'u Kurah Tavern hotel nan naga motar da sanah ta shiga a bakin titin governr rd tayi parking, Wani hadadden gaye ne ya fito daga cikin motar ya zagayo gefen sanah ya bude mata kofa, ya rungumota suna tafe suna hira har suka kai ciki, a kofar shiga ne sukayi karo da wani saurayi shima kyakykyawa, baya ya koma da sauri yana fadin sorry pls, suka hada ido da saurayin da suka shigo tare da sanah, bude baki sukayi dukkansu suna dariya, saurayin dake tare da sanah yace Hilal kana duniya, dayan saurayin ya mika mishi hannu yace ina nan Hafiz 2dys ka buya, rabona da kai zai kai 3yrs fa, hafiz yace hakane kam ya kake ya su baba, hilal yace suna nan lafiya tare muke dashi ma suna ciki shi da abokinshi, ya kalli sanah dake makale jikin hafiz tana kallonshi, yace sannu ko yammata, tayi fari da ido tace yauwa, hilal yace hafiz sauri nakeyi zanje in dauko ma su baba abinci a gida bani numbrka, yace to ya karbi wayar ya sa mishi numbr, yace ma sanah ta jirashi ya rakashi**** Hilal ya kalle shi da suka fita yace hafiz kana nan da neman mata har yanzu, hafiz yayi dariya yace sune ginshikin rayuwa mutumina, wannan ma yau na hadu da ita, dama ina tunanin kwana ni daya a hotel kasan a kano nake yanzu, hilal yace Allah ya shirya to ai gara ka riketa ka aureta dan ta hadu sosai, hafiz yayi tsaki yace wannan ba ta aure bace mutumina macen da daga haduwa ta yarda da kai ai ba irinsu ake aure ba, hilal yayi murmushi yace ka dai ji tsoron Allah ni bari in wuce sai na kiraka, hafiz yace okk sai na jika abokina,,, Satin zulfa'u uku a gidansu mummy, fatarta ta murje saboda mayukan da take shafawa, ta koyi komai na gidan cikin kankanin lokaci, kullum ita ke karawa mummy karatun qur'ani da littafai, haka wasu ayukan girki tare sukeyi da laila,, Wata ranar jumma'a suna tsaye dukkansu a kitchen suna girkin jumma'a kamar yadda aka saba yi a gidan, kowa da aikin da yakeyi suna hira, jalila ta kalli zulfah dake haďa salad, cikin tsokana tace anty laila kinga matar yaya abba an dan fara murjewa ji yadda ta daddage tana hada salad, zulfa tayi murmushi bata kalleta ba dan ta saba da tsokanar jalila, anty laila tace kedai jalila baki da kunya walhy,, matar yayan naki kike ma iskanci, bari in gama foiln zaki sani dan da mummy zan hada ki, ko kuma in kira abban in fada mishi, jalila tace yauwa anty yaya abba na kiranki kuwa, tace a'a kuma ko na kirashi ma baya ďauka, jiya ma abban ayda ke min korafin baya kiranshi, jalila tace umm ko mummy baya kira kuma kinsan bai san maganar auren nan ba, laila tace eh ina ganin akwai abin da ya tsareshi ne, jalila ta tabe baki tace babu wani abun da ya tsare shi ay yana kiran anty amarya, laila tace kai jalila bansan sharri, jalila tace Allah anty ba sharri bane, naga missd call dinshi har 7 a wayarta, anty laila tayi jugumm sannan tace to Allah ya kyauta amma baki fada ma mummy ba ko, tace eh ban fada mata ba, tace to kiyi shuru da bakinki,, zulfah ta mika ma anty laila salad din ta kama wani aikin, anty laila ta kalleta tace baki gajiya ne ke, kije kiyi wanka fatsin zata karasa gyara kitchen din, zulfah tace to anty, ta wanke hannunta ta kalli jalila dake mata wani irin kallon tsokana kasa2 tana murmushi, ta yarfa mata ruwan hannunta tace kyaji dashi ta fita da gudu, jalila ta kwashe da dariya tana goge fuskarta tace lallai yarinyar nan taci abinci, laila tace ay tamin dai2, jalila tace zan rama ne ay tasan hali na, Zulfah na fita daga kitchen tayi karo sosai da mutum wayar dake hannunshi ta faďi,, da sauri taja da baya jikinta ya fara rawa ta dago kai ta kalleshi yana tsaye shima kallonta yakeyi sanye yake da red top da ta karbi fatar jikinshi gashin kanshi a kwance da ganinshi kasan hutu ya gama ratsa shi kamarshi daya da Nurain sai dai yafi nurain kyau, ta tsuguna da sauri ta dauki wayar tace dan Allah kayi hakuri wallhy bansani ba, bai amsa mata ba ya mika hannu ya karba, ta bi ta gefenshi ta wuce ya bita da kallo har ta bace ma ganinshi sannan yayi ajiyar zuciya ya shiga kitchen ...... Mrs tijjani shattima.. [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 1⃣7⃣ By Aysha Ya'u Kurah Laila ce ta fara ganinshi ta fadada fara'arta tace farouk yaushe ka dawo, yace yanzun nan anty, ya rankwashi kan jalila dake shan fruit salad yace acici, ta ajiye spoon din ta rungumeshi tace yaya farouk oyoyo, shine baka fada azo a dauke ka ba, ya harareta yace sai kace wani yaro, anty ina mummyna, anty laila tace suna skool nasan yanzu zaka gansu, sannu dan autan mijin yau kai zanyi yayi fadi duk abinda kakeso in kawo maka, yayi dariya yace I trust u anty ki kawo min kome kuka dafa, jalila cikin murna tace to broo, ta kwaso ragowar kayan da basu jera a dining ba ta jera, sannan ta zuba mishi abinci tana mishi hira dan taji dadin dawowarshi, yace to parrot barni in ci abinci, ta turo baki tace kai yaya dan ma kaga ina murna ka dawo shine kake min wulakanci ko, yace sorry sis surutunki ne yayi yawa, tace to shikenan da naso in baka labarai amma na fasa, yace yi hakuri kanwata zauna ki tayani cin abinci in mun gama sai ki bani ko, ta zauna ta zuba abinci suka ci tare tana mishi hira.. Zulfah na daki tsoro ya hanata fitowa duk tunaninta shine wanda aka daura mata aure dashi, afrah ce ta shigo dakin ta tsaya gabanta tace antie zage min zip mummy tana sallah kuma anty jalila tace bazata zage min ba saboda naki bata ice cream din da daddyn ayda ya siyo mana, zulfah ta janyota ta zage mata zip tace me yasa kika hanata rowa babu kyau, , afrah tace ba kowa yasha nashi muna bacci ba, ni bazan bata nawa ba, zulfa tace to muje in miki wanka sai ki kira amrah ma in mata ko, afrah tace ay anty jalila ta mata saboda ita ta bata nata, zulfah tayi dariya tace to muje in miki, suka shiga bayin ta mata wanka suka fito ta shafa mata mai, tace je ki dakko kayanki in sa miki, ta fita da gudu taje daki ta dakko kayanta da mummy ta fito musu dashi, tama jalila dake ma amrah kwalliya gwalo ta ruga da gudu jalila tabi bayanta itama da gudu, ihuu afrah ta dinga yi saboda jalila ta kusa kamota, a tare zulfah da farouk suka fito a firgice sun dauka wani abun ne ya sameta, jikin zulfa afrah ta fada tana maida numfashi tana dariya, jalila ta karaso ta daga hannu zata kai mata duka, farouk dake tsaye yana kallon zulfah ya daka mata tsawa, yace baki da hankali ne, me ta miki, jalila tace wallhy yaya yarinyar nan ta raina ni, da ta miki me ya fadi yana kallonta,. afrah tayi saurin guduwa bayanshi tace (yaya umara sunan da mummy ke kiranshi suma haka suke kiranshi ita da amrah) babu abinda na mata wai dan tace in tsammata ice cream naki shine taki min wanka kuma ta biyoni zata duke ni, jalila tace wallhy karya take min gwalo fa ta min ni sa'arta ce da zata min gwalo, farouk yace kusan sa'arta dince ke tunda bakinki ya iya kwadayin abun yara komai kika gani sai kinsha,, ta turo baki kamar xatayi kuka tace wallhy yau Allah ne kadai zai kwaceki, afrah ta kara mata gwalo tana dariya, jalila tace yaya kana ganin abinda takemin ko wallahy yau sai naji ma yarinyar nan ciwo, ta wuce daki ranta a bace, zulfah ta dauki kayan afrah tace zo muje in shiryaki, afrah ta rugo gurin zulfah suka wuce daki suka bar farouk baki sake yana kallonta, wai wacece wannan, ya fadi a fili, yarinyar is so cute, ya daga kafadunshi ya juya daki yana siffanta yanayin zulfah a zuciyarshi,, Da safe bayan ya dawo sallar asuba ya shiga dakin mummy, zaune ya samesu tare da zulfa'u tana kara ma mummy karatu, gefensu ya zauna yana sauraron kira'arta yana bin karatun idonshi a lumshe, sai da suka idar sannan ya bude idonshi ya kalli zulfah da ke kwashe qur'anai, ta sunkuya tace ina kwana, yace lafiya lau malama, ta ajiye qur'anan gurin da suke ta fita, ya dawo kusa da mummy yace ina kwana mummy, tace lafy lau umara ya gajiyar hanya, yace tabi lafiya mummy, nan suka fara hirar skool dinshi, har gurin karfe takwas suna hira, har ya tashi zai tafi ya dawo yace wai mummy a ina kika samo wannan kyakykyawar malamar, mummy tayi dariya tace malama ce amma tá gida, ya zauna yace ban gane ba, tace Amaryar Abba ce, gaban farouk ya fadi sosai yace wane abban, mummy tace na nan gidan yayanka, abinda yasa bamu fada muku ba saboda muna son muyi muku surprise, ko shi abban bai sani ba, farouk yayi ajiyar zuciya yace gaskiya yaya abba ya dace sosai, Allah ya basu zaman lafiya, mummy ta bude murya cikin farin ciki tace ameen umara cika daji, yayi murmushi ya tashi ya fita jikinshi a sanyaye..... Mrs tijjani shattima... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: [3:40PM, 20/01/2016] Mrs Tijjani shattima💏: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 1⃣8⃣ By Aysha Ya'u Kurah Dakinshi ya wuce ya kwanta yana ta juyi, Astaghfirullah... Astagfirullah...... Astagfirullah...... Kalmar da ya dinga fadi kenan a bayyane, saboda farat daya zuciyarshi ta kamu da son macen da ta haramta a gareshi har abada,, ya dinga godiya ga Allah da yasa ya sani da wuri, tabbas kallo ďaya yayi mata yaji wani abu game da ita, a kallon da yayi mata na biyu zuciyarshi ta fara kitsa mishi wani sabon al'amari mai wuyar faďuwa, hannunshi ya daga sama yace Allah na gode maka daka sanar dani wacece ita a kallon da nayi mata na uku, Ya lumshe idonshi a hankali yana neman tsari daga sharrin shaidan dan yasan duk aikinshi ne wannan, cikin ikon Allah har bacci yayi gaba dashi.... Kuka sosai anty amarya keyi a gaban daddy, duk wanda ya ganta a wannan lokacin zai dauka daga can cikin zuciyarta take kukan, hankalin daddy ya tashi matuka, yace subhanalhi hadiza lafiya me ya faru, cikin muryar kuka tace babu komai, da sauri yace kamar yaya babu komai, fada min abinda ke faruwa mana, ta kara narke murya tace banason ace na fara kawo kara, duk abinda akeyi min a cikin gidan nan ina shanye wa na dauki yaya tamkar ita ta haifeni shiyasa kome zatayi min bana daukarshi da zafi, amma bazan jure gaba da ita ba, ina matukar shan wahala saboda rashin kulani da bata yi kwata2 bata amsa gaisuwata, haka ta hana su jalila gaisheni, yau kwanan farouk hudu a gidan nan ko sau daya bai je inda nake ba bare yayi tunanin gaisheni, dan Allah ka bata hakuri in nayi ma wani l-a-i-f-i ta karasa fadi tana sheshshekar kuka kamar da gaske, ran daddy ya baci sosai yace ita Aishan ce bata kulaki, anty amarya ta gyada kai tana share hawaye, yace me kikayi mata to, cikin sanyin murya tace babu abinda na mata,, daddy ya mike a fusace zai fita tayi maza ta riko shi, tace kayi hakuri daddy bazan juri inga kana ma yaya fada ba dan Allah karka mata magana zata ce kararta na kawo gurinka kuma zai kara zame mana matsala, nidai inason ka lura da kanka idan kaga yadda muke tafiyar da alamuran mu sai kayi mata magana, amna yanzu in ka sameta ay komai baci zaiyi, Daddy yayi ajiyar zuciya yace wallhy da kin barni naje na sameta, suma su farouk din sai naci mutuncinsu, anty amarya tace kayi hakuri yara ne, kuma ni duk abinda zasu min bazan taba rikeshi ba saboda son da nake musu ko da dan da na haifa banajin zan iya mishi irinshi, ta dangwabe a jikinshi tace ina matukar kaunar jininka fiye da yadda nakeson kaina ma, dadi daddy yaji har cikin ranshi ya rungumota sosai yana rarrashinta nan ta kasheshi da kissarta mai zafi wacce take ma mummy zagon kasa da ita.... Mrs tijjani shattima.... [7:12PM, 20/01/2016] Mrs Tijjani shattima💏: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 1⃣9⃣ By Aysha Ya'u Kurah Zaune suke kewaye da mummy a parlor bayan isha'i, farouk na zaune yana latsa waya, jalila da zulfah suna duba wani littafin adduo'i suna musu akanshi, Anty amarya ta fito cikin daguwar riga mai kyau da tsari, ta gabansu tazo ta wuce duk suka gaisheta daya bayan daya, ta amsa tana yatsina mummy ko kallon inda take batayi ba, fridge din palour ta bude ta dakko juice ta koma daki, tana jin hon ďin motar daddy tayi maza ta mike ta kara gyara jikinta ta feshe jikinta da ni'imtaccen turare, sai da taji ya shigo sannan ta fito tana tafiyar hawainiya, ta karaso cikin parlon ta dan durkusa tace sannu yaya, mummy da mamaki ya isheta ko kallon inda take batayi ba, daddy ya lura tsaff da mummy sannan yabi dukka yaran da kallo dan baiji sun gaisheta ba, haba nan da nan ranshi ya baci sosai ya kalli mummy da ta haďe girar sama da ta kasa yace Aisha bakiji ana gaisheki bane, mummy tace banji ba ta cigaba da kallon tv, daddy ya kalli farouk yace kai dan ubanka baka iya gaisuwa bane, cikin rashin fahimta yace dad-- bai bari ya karasa ba ya shiga surfa musu ruwan bala'i anty amarya na gefenshi tana kukan munafurci tana bashi hakuri, ya kalli zulfah da kanta ke sukunye yace harda ke zuwan jiya har an koya miki rashin kunya an nuna miki karki daraja matata to wallhi babu wanda ya isa ya taka min mata ina kallo haka ya dinga masifa mummy bata kalli inda yake ba bare tasan abinda yake fadi, zagin da taji anty amarya tayi ma zulfah ne yasata mikewa a fusace, kuma dama tayi hakan ne dan ta harzuka mummy, Cikin fushi mummy ta janyo zulfah dake rakube a kusa da jalila duk kuka sukeyi, tace Hadiza kika mata ce yar matsiyata, kinsan waye matsiyaci, to ki bude kunnenki dakyau kijini,, matsiyaci shine wanda duk abinda ake bashi baya isar shi sai ya hada da haram, matsayaci shine wanda yake siyar da mutuncinshi dan ya samu kudi a kirashi da mai arziki, matsiyaci shine mai arzikin dake nuna halin tsiya kamar yadda kikeyi, kuma yanada daga cikin siffofin matsiyaci mutum ya zama munafuki algungumi kamar yadda kike, sai kiyi alkalanci tsakanin ke da ita waye matsiyaci? kinga wannan yarinyar, ta fi min ke da duk wani wanda ya rabeki, haushi kikeji saboda na aurawa abba ita ko, to bari kiji ko bayan raina jinina bazai taba haduwa da jinin fasikai irin---- wawan marin da daddy ya dauketa dashi ne ya hanata karasa maganar da takeyi, farouk ya mike da sauri jikinshi na rawa ya fita daga gidan gaba daya idonshi jawur, daddy yace a gabana kike fifita wata banza akan matata, a gabana kike kiran matata fasika, lallai Aisha kin cika marar mutunci me manta alkhairi, duk irin biyayyar da hadiza take miki baki gani, yanzu dama akan wannan yarinyar gidana yake neman kamawa wuta, wallhi badan nasan darajar aure ba da a yau sai yarinyar nan ta bar min gidana, amma kisa a ranki, duk ranar da abba ya dawo yace baya son yarinyar nan, wallhy tallahi zan goya mishi baya dari bisa dari ya auri wacce yakeso, dan kinga na kyaleki kina yadda kikeso da ya'yana to komai yazo karshe, ya cigaba da masifarshi mummy dake tsaye rike da kunci hawaye na zuba akansu ta juya ta barshi a gurin yanata masifa, daki suka wuce ita da jalila da zulfah, dukkansu kuka sukeyi,, Daddy ya zauna bayan yayi masifar mai isarshi muryarshi har ta fara dashewa saboda bai iya masifar ba, ya shiga rarrashin anty amarya dake kuka sosai, yace ya isa hadiza, cikin kuka ta tureshi tace me yasa zaka mareta, wallhy zafin marin a jikina najishi, wata rana zata gane kuskurenta tasan ni mai kaunarta ce, amma yanxu ka kara goga min bakin jini, yaya ta kasa gane irin son da nake mata, amma da sannu zata gane ""ta kara rushewa da kuka, ya dinga rarrashinta yanajin tausayinta a zuciyarshi dan yasan tana kaunarsu dukkansu har cikin ranta, to me ya canza Aisha ta tsaneta lokaci daya, me ya canzata take neman rushe farin cikin gidanshi magana yakeyi a zuci baisan ta fito ba, anty amarya tayi saurin mikewa tace Zulfa'u, shigowar Zulfa'u gidan nan yana neman rusa da farin cikin daya ginu lokaci mai tsaho, irin yaran nan burinsu su auri mutum ya mutu suci gado amma yaya ta kasa ganewa, ni tausayi ma take bani saboda makashinka yana jikinta,, daddy ya gyada kanshi ya daura duk akalar tunaninshi akan Zulfa'u baiwar Allah (kissa tafi magani sunan wani littafi) Mrs tijjani shattima... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 2⃣0⃣ By Aysha Ya'u Kurah A daren ranar bacci ya kauracewa idanuwan bayin Allahn musamman zulfah dake kuka kamar ranta zai fita, daddy kuwa yana can gurin anty amarya itama kukan takeyi yana rarrashinta sam baiyi tunanin mummy ba dan gani yakeyi duk laifin nata ne, Haka gidan ya kasance har tsawon kwana hudu mummy sam bata fitowa daga ďaki, bata kaunar abinda zai haďata da daddy bare anty amarya, Kullum nurain da farouk ke zama su tausheta da kalamai masu dadi, abinci ma a daki suke zama suci duk da ba wani cin kirki suke ma abincin ba, alamarin mummy ya fara damun daddy dan yasan halinta sarai in tana fushi bata ki sufi shekara a haka ba, ranar kwana na biyar ne daddy ya yanke shawarar zuwa ya sameta su sasanta kansu dan Aisha itace shi itace rayuwarshi baki ďaya duk wani ci gaba da yasamu a sanadiyyarta ne, Zaune ya sameta a kan dadduma tana karatu,, jalila da zulfah suka gaisheshi suka fita da sauri, a gefenta ya zauna yana jiran ta idar, , ya kusa awa zaune bata idar ba yasan da gayya ta kara janyo sura mai tsaho, rufe al Qur'anin yayi ya daukeshi a gabanta, bata ďago kai ta kalleshi ba ta cigaba da karatunta da ka, cikin muryar lallashi yace kiyi hakuri Aisha, dan Allah ki saurareni, ko kallon inda yake batayi ba ta fara kokarin mikewa, rike hannunta yayi yace mu ba yara bane Aisha, cikin fushi tace kace ni ba yarinya bace, dan kai yarone karami ma, ka sakeni kar in fada maka maganar da zata sa Allahna yayi fushi dani, banason hakurinka ka koma can gurin matarka ka cigaba da rarrashinta, janyota jikinshi yayi sosai yana murmushi yace kece matata uwar ya'yana, kece silar cigaban Hasheem, ke kika zauna dani daga ba kowa ba har na zama wani, bai kamata mu dinga samun sabani ba in kikayi la'akari da shekarun da muka dauka muna tare, kinsan duk duniya bani da wata sama da ke, ta katseshi da sauri tace kanada hadiza, dan hadiza tafimu daraja dani da ya'yana tunda har akanta zaka iya daukar hannu ka mareni, ka bani mamaki hashimu, babu ranar da zan manta wannan cin mutuncin, Cikin damuwa yace ki zama mai yafiya Aisha, so nakeyi gidana ya dauwama cikin farin ciki, banason yarana su raina hadiza dan zataga kamar dan bata haihu bane, in zakuyi fada kuyi tsakaninku amma banason yara su dinga shiga, cikin fushi mummy tace wai wane fada kake magana,, yace ki fadamin me ya hadaki da hadiza da bakya kulata, ko ta gaisheki baki amsawa, meyasa su farouk basa gaisheta, mamaki ya hana mummy magana kallonshi kawai ta tsaya yi, ya cigaba da cewa kinga ko ranar a gabana ta gaisheki baki amsa ba, kuma babu ko daya a cikin yaran nan da ya gaisheta, kinga bazanji dadi ba, kuma naga ba haka kuka saba ba, tun zuwan yarin--- mummy da ta gama gano makirci ne shiryayye ta katseshi da sauri tace dakata kar ka kira min zulfa cikin maganata, naji na dauki laifi kuma yara ma zan musu fada, in shaa Allahu komai zai daidaita, cikin jindadi daddy yace kin hakura kenan, tayi murmushi tace ay kasan ni da kai bama iya fushi da juna kuma wanda ya shiga tsakanin mu shi zaiji kunya,, yayi dariyar jindadi yace kwarai kuwa Aisha abin alfaharina,, nan suka cigaba da hirarsu cikin hikima ta cire mishi duk wata damuwa da kokwanton da yake da shi akan zamansu da zulfah, ya dade a dakinta kafin ya fita ta mishi alkawarin yanxu zata fito ta sameshi, Dariya tayi da gama nazarin duk kalaman daddy, tace kinyi kuskure hadiza, zaki gane kissar bariki kadai kika iya, yanzu ne za'a fito salon kissa kala2 muga wanda zai ci riba.... Mrs tijjani shattima... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 2⃣1⃣ By Aysha Ya'u Kurah Sati ďaya bayan wucewar wannan, mummy a gaban daddy tana nuna ma anty amarya kulawa ta musamman wacce take bata mamaki ita kanta dan in daddy baya nan ko A bata ce mata, duk yadda taso ta kara samun wani gurbi na haddasa fitina mummy ta toshe shi, kullum ran anty amarya a bace yake musamman yadda taga mummy da daddy nayi a gabanta, Zaune take a daki tana tufka da warwara dan da a tunaninta ta samo kan daddy saura abba yanzu gashi kwabarta tayi ruwa, tunanin hanyoyin da zata kara bi cikin hikima ba tare da daddy ya gano ta ba takeyi, wayar daddy ce ta shigo wayarta ta daga bayan ta gama hararar wayar, a hankali take magana kamar wacce taci kuka ta koshi, daddy yace lafiya hadiza, ta kara kwantar da murya tace lafy lau, daddy bayason yawan zurfafa bincike saboda bayason jin abinda ke faruwa har ya dame shi ko ya harzukashi ya aikata ba dai2 ba, dan haka yace to alhamdulillah tunda lafiya lau, yau zan dawo na kira wayar Aisha bata dauka ba dan Allah kice tayi min danwake da kunun gyaďa dan zan kashe wayata yanzu ne, anty amarya tace to zan fada mata, sukayi sallama ta kashe wayar, kwanciya tayi a kan gado tana dariyar mugunta dan tasan ya tsani yace ayi mishi abinci aki yi musamman danwake, ta riga ta gama haďa plan dinta ta dinga murmushi bacin rai ya ragu sosai a zuciyarta.. Farouk tsaye a kitchen yana hira da su zulfa dake kwashe tuwo jalila na fere dankali dan bata cin tuwo, cikin tsokana yace amaryar yaya ni fa bana cin tuwo, tayi murmushi tace to me kake ci, jalila tace wahala kawai zai baki dan yanzu zaice danwake da kunun gyada daddy ya koya musu cin danwake na tsaneshi walhy tayi tsaki ta cigaba da fere dankali, farouk yace ina ruwanki ko kinji na fadi abin da nakeso, nidai bazanci tuwo ba kuma bazanci dankali ba, asan yadda za'ayi dani ya fadi kamar karamin yaro, zulfah tayi dariya sosai tace to kayi hakuri yanzu zanyi maka abinda kakeso, yayi murmushi ya kalleta yace wasa nake miki ki dafa min ko indomie ne dan nasan kin gaji, tace kai dai jeka zanyi maka abinda kake so, yaji dadi sosai dan ya dade baici danwake ba, yace to amma karki sha wahalar yin kun--- kai dai jeka tunda yi maka za'ayi bamason iyayi jalila tafadi tana dariya, yace kin raina ni fa jalila wallhy zan murde shegen bakin nan naki, ya kalli zulfah dake daura ruwan zafi yace zanje u/dosa in dawo kinji tace to adawo lafiya ta wuce store ta debo flour, cikin mintuna talatin ta gama danwaken da kunun gyadan saukinta ma akwai nikakken gyada irin na maiduguri a fridge, a cooler tasa danwaken ta diban mishi miyar alayyahu da yaji kayan ciki da naman rago, ta zuba kunun a flask ta deban ma amrah da afrah dan suma suna son kunun gyada, Mummy ta kalleta da ta kai ma su afrah tace kunu kika dama, tace eh yaya farouk yace a dama mishi, tace lallai kina shagwaba yaran nan, laila ta baki kewa da tare zakuyi sannu kinji Allah ya miki albarka ameen tace cikin jin dadi ta fita ta koma kitchen ta tadda jalila na shan kunu, tana ganinta ta ajiye kopin da sauri tace ko iya damawa ma bakiyi ba da kyar na iya shanye wannan, zulfah ta kure ta ido tace ance dole kisha ne, ko danneki akayi akace sai kin shanye, jalila ta juya tana murmushi tace ay dan nasan bazaki ji dadi bane idan bansha ba shiyasa, zulfa ta kwashe da dariya tace walhy baki da dama, ta cigaba da aikinta.. Bayan isha'i daddy ya dawo lokacin mummy na daki ta idar da sallah tana addua, a gajiye ya shigo parlon ga matsananciyar yunwa yanaji anty amarya ta fito ta taryeshi tana mishi sannu da zuwa, ya zauna ya amsa yana maida numfashi, tace sannu kasha hanya, yace wallhy kuwa yunwa ma nakeji sosai, ina Aisha kin fada mata sakona, tayi murmushi tace kwarai na fada mata kace ayi maka danwake da kunun gyada, dai2 lokacin mummy tafito kuma taji duk abinda anty amarya tace, abin bai bata mamaki ba saboda tasan iya bariki irin na hadiza, to yanzu a ina zata samu danwake, dan tasan zulfah ta dama ma farouk kunu kuma bai dawo ba, addua tayi a zuciyarta sannan ta karaso cikin parlon tana murmushi ta zauna gefenshi tace sannu kunsha hanya, yayi murmushi yace kedai bari tafiya yankin azaba, tayi dariya tace sai kace wanda yayi tafiyar kasa bari a kawo maka abinci, yace yauwa Aisha ta mike tayi hanyar kitchen tana ma anty amarya murmushi mai alamar baki da wayau, itama anty amarya ta mayar mata da murmushin yau zaki sani, kitchen mummy ta shiga ta dauko flask din kunu, tasan zai fara shan kunu har agama dan waken, jalila da zulfah ta kwala ma kira da sauri suka shigo kitchen din, mummy tace kuyi sauri ku kwaba garin danwake ku daura ma daddy, jalila tace mummy har zai jira ga wanda zulfah tayi ma yaya farouk a kai mishi sai ayi ma yaya farouk wani, ajiyar zuciya tayi da taga kulolin ta bude taga danwake yana turiri da miyar da daddy keso, da sauri tace ma jalila dauka ki kai parlor ta mika ma zulfah flask din kunun suka kai komai na bukata anty amarya na murmushi dan ta dauka tuwo ne, mummy ta zauna a kasa ta zuba mishi kunun sai kamshi yakeyi, ya amsa yana sha yana lumshe ido, ta bude kular danwakn nan anty amarya ta kirne fuskarta ta dinga bin danwaken da kallo, mummy ta gama ta zuba mishi miyar da kayan ciki kamshi ya cika ko ina daddy ya fara cin danwake cikin jindadi dan ya samu abinda yakeso, har yagama ci anty amarya bata kara cewa komai ba, to ya akayi tasan abin da yace yanaso, kodai ya kirata ne? To ay da ya kirata bazai tambayeta ba da ya dawo, daddy ya wanke hannunshi bayan ya gama yanata shi ma mummy albarka, suka yi yar hira kadan sannan ya mike yace tazo ta taimaka mishi yayi wanka, tace to, ta kira su zulfah suzo su gyara gurin, saida ta tabbatar ya shiga daki, sannan ta kalli anty amarya, tace "nace Allah hadiza" babu mai cin galaba akaina, kina kuskuren ja dani, baki san Allahna ya tsaya min ba, bakiyi mamakin yadda danwake ya fito nan da nan ba, Allah nagode maka da ka shigo da zulfah cikin rayuwata, da bansan me zai faru ba yau saboda makircin makirar mace, dama kin yarda makaman ki da yafi maki dan bazaki taba cin galaba akaina ba, tayi murmushi mai kyau ta wuce side din daddy ta bar anty amrya kamar zata kurma ihu dan takaici.. Mrs tijjani shattima.. [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 2⃣2⃣ By Aysha Ya'u Kurah Wata daya sadeeq yayi baiji muryar sanah ba, hankalinshi a tashe yake matuka, ya rame sosai saboda ba karamin so yake mata, ya riga ya gama shirye shiryenshi na dawowa gida, ranar lahadi da safe jirginsu ya ďaga zuwa nigeria bai sanar ma kowa a gida zai zo ba dan ba kiransu yakeyi ba ko sun kira ma ba dagawa yakeyi ba, Karfe 3 jirginsu ya sauka a abuja, yayi niyyar fara biyawa gurin sanah amma baisan takamaimai adress dinsu ba, drop ya dauka zuwa kaduna, sai 5 suka iso ya kaishi har kofar gida ya biyashi ya dauki yar karamar jakar kayanshi ya fito, Masu gadi na hangoshi suka maza suka bude mishi kofa suna gaisheshi ya amsa babu walwala a fuskarshi, ciki ya shiga babu kowa a parlon direct ya wuce dakinshi yayi wanka, Zulfa'u na zaune a parlo tana gyarawa ayda kanta, jalila na skool dan ta fara zuwa "kasu" sati daya kenan, twins na gefenta suna mata surutu,, karar rufe kofar dakin da ba'a taba budewa ba taji tayi maza ta daga kanta sama taga mutum tsaye cikin kananun kaya da bakin glass a idonshi, wannan ba farouk bane dan yafi farouk jiki da tsaho, ihun twins ne ya katse mata zancen zucin da takeyi, yaya abba oyoyo suka ruga da gudu suna rige rigen zuwa gurinshi, ya rungumesu ya daga ayda yace mummyna kece kikayi katuwa haka fada min me ake baki kici, ta kwanta a jikinshi tana dariya, ina wuni yaji an fadi a bayanshi ya kalleta daga sama har kasa ya maza ya dauke kanshi ya wuce side din anty amarya yana adduar Allah yasa ba wannan kucakar yarinyar mummy ta dauko mishi ba, waya takeyi sanda ya shigo tana jin muryarshi ta katse wayar ta fadada fara'arta tace ango ango, yaushe a garin, yayi tsaki yace dan Allah ki bari anty, tayi dariya tace kamar yaya in bari, baka hadu da amaryar taka bane, yace ohh my God ban shiga dakin kowa ba sai nan babu ma wanda yasan na dawo sai wata yarinya may be ma yar aiki ce, anty amarya ta kirne fuska tana kallon twins dake kallon fuskar abba, tace ban san iskanci wace irin yar aiki, afrah ku da waye a parlo, afrah tace anty zulfa'u ce, tayi murmushi tace to ku tashi maza kuje kuyi wasa, suka tashi suka fita, anty amarya tace amaryarka ce ai, da karfi yace wattt? Ta gimtse dariyar da tazo mata Ta hade rai tace meye na ihu, kyau ne bata da ko me, innalillahi wa inna ilaihir rajiun abinda sadeeq ke fadi kenan, lokaci daya yaji muguwar tsanar yarinyar daya gani a parlor wacce aka kirata da zulfa'u, Yace haba anty wake maganar kyau anan, ay persnlty din zaki duba, kamar ni a dauko wannan kwailar yarinyar ace matata ce, meyasa mummy zata min haka, yanzu ta ina zan fara nuna wannan yarinyar a matsayin matata , wayyo Allah na, ya fadi yana matse hannunshi, Anty amarya tace hmmm gata munafuka abba ga shegen hada fada, ko kasan rannan saboda ita mukayi fada sosai da yaya, ta fara share kwallar gulma tace yaya harda mari na a gabanta, yanzu haka bama gaisawa da ita kuma duk saboda yarinyar, saukin da zaka samu shine daddy yace in baka sonta zai goya maka baya ka saketa, nan ta cigaba da kitsa mishi karya da gaskiya, bai bar gurin ba sai da tsanar zulfa mai tsanani a zuciyarshi kuma zuciyarshi ta kangare akan kome zai faru sai dai ya faru amma bazai zauna da zulfah ba.... Mrs tijjani shattima... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH◆◆ 2⃣3⃣ BY Aysha Ya'u Kurah Da gudu su afrah suka fada kan mummy tace wayyo yaran nan Allah ya shirya, suna haki suka hada baki dukansu sukace mummy yaya abban daddy ya dawo yana can dakin anty amarya yace wai anty zulfa yar aikin mu ce shine mukace mishi a'a sunanta anty zulfa kuma naji anty amar--- shigowar laila ce ta katse su tare suka shigo da sadeeq itama a hanya suka hadu, mummy tace to naji kyautar Allah kuje maza kuyi wasa suka fita da gudu, sadeeq ya zauna gefenta a kasa yace ina wuni, da kamar bazata amsa ba sai taga kar ta biye mishi ya kara dilmiyewa, tace lafiya lau, yayi shuru anty laila tace mummy na gama dambun yanzu zaki ci ko sai anjima, mummy tace zuwa anjima sannu kinji, tace yauwa mummy, har ta kai kofar fita mummy tace ki turomin zulfa'u,, jin haka yasa sadeeq ya tashi ya fita da sauri dan baiso yaji ma mai zata ce,,, tayi murmushi tace duk ka gama yinka abba baka isa ka rabu da yarinyar nan ba, dan ina ji ajikina zata xame maka silar shiga aljanna.. Bayan isha'i duk suna parlor ana hira banda zulfah da tun ganin da tayi ma abba ta fara jin tsoron irin kallon da yayi mata, Nurain, farouk da daddy suka shigo duk suka zauna anata hira, sadeeq ya fito daga dakin anty amarya ya gama mata magiyar ta bashi adress din sanah sai gwarashi takeyi, ganin su daddy da yayi a parlor ne yasa shi karasowa parlon, daddy cikin murna yace babana yaushe ka dawo, ya zaune kusa dashi yace dazu daddy, Yace ikon Allah to ya skull din, yace lafiya lau daddy, ya gaida yaya nurain, farouk ma ya gaisheshi, daddy yace ka dan rame abba ko dai akwai wahala ne karatu, yace um um daddy kawai dai nayi missing dinku ne, daddy yayi dariya yace kai dai fadi gaskiya, sai kuma ka dawo ka tarar da abin farin ciki, sadeeq ya maida dariyarshi yace wane abin farin ciki, daddy yayi dariya ya kalli mummy yace au baki mishi albishir ba, tayi dariya cikin dabara tace ay mamanshi ta fada mishi, amrah kirah min zulfah, amrah ta mike da gudu taje ta kira zulfah, tare suka fito tana sanye da hijab har kasa, sadeeq fuskarshi kamar bata taba dariya ba ya kauda kanshi idonshi jawur, daddy yace abbana!!! wannan itace matar da aka daura maka aure da ita, da fatan bazaka bamu kunya ba zaka riketa tsakani da Allah, Sadeeq murya can kasa yace aure kuma daddy, gaskiya kuyi hakuri, Allah yasani bazan iya daukar alkawarin da bazan cika ba, haba daddy kalleta fa ya fadi yana nuna zulfa yace God forbid, gaskiya ni inada wacce nakeso sai dai kuyi hakuri ya fadi yana mikewa, Nurain ya daka mishi tsawa yace uban wa kake fada ma saidai yayi hakuri, dan ma kasamu ana lallabaka, meye aibun yarinyar da zaka tashi kana fada ma mutane magana, sadeeq yace dole kace meye aibunta saboda selfishness irin naka, wato kai saboda an aura maka wayayyar mace high class beb shiyasa ni ka yarda aka dauko min wannan kuchakar a matsayin matat--- wawan mari nurain ya kai mishi wanda ba sadeeq ba har wadanda ke gurin saida suka ji shi a jikinsu, zulfah da tunda sadeeq ya fara magana ta bishi da ido muryarshi nata mata yawo a dodon kunne, babu kalmar da ya fada da tayi mata zafi saboda dadin jin muryar da ta dade bataji ba, Sadeeq ya rike kuncinshi yace ni ka mara, mummy ta mike ta kara daukeshi da mari tace ya mareka nace ya mareka marar mutunci ko kanada abinda zakayi, idon sadeeq ya kada babu alamun fari a ciki yace wallhy bazan zauna da ita ba, narantse da Allah natsaneta, ya koma kusa da daddy da ya dafe kanshi yace daddy ka taimakeni wallhy inada wacce nakeso, dan Allah karka bari su ruguza min farin cikina, kuka sosai yakeyi saboda zafin da zuciyarshi takeyi, daddy ya dafa shi yace kayi shuru ya isa haka komai zaizo da sauki, farouk dake gefe ya kalli zulfah dake kuka yaji tausayinta sosai a ranshi yace wannan wace irin muguwar tsana ce, ya kalli mummy da idonta ya ciko da kwalla yace mummy kiyi hakuri dan Allah ki barshi ya auri wacce yakeso din ko ya zauna da zulfah cutar da ita zaiyi, mummy cikin kuka tace wallhy na rantse ko bayan raina abba ya saki zulfa'u ban yafe mishi ba, Daddy ya daka mata tsawa yace wai Aisha meyasa kike da taurin zuciya ne, meyasa baki da feelns ne ki duba kiga yadda yaron nan ke kuka kinsan ba karamin abu kesa shi kuka ba, ki daina saurin yanke hukunci kai tsaye har ya kaiki dayin mummunan furuci irin wannan, Nurain cikin fushi yace daddy ka daina biye mishi iskanci ne yasa shi kuka saboda ya raina mutane sakarai kawai wanda ko kadan baisan kanshi ba bare yasan inda yake mishi ciwo,, ya kalli jalila da zulfah yace su tashi su wuce daki, ya kama mummy dake kuka suka wuce daki yana rarrshinta, daddy ya shiga rarrashin abba yace ya kwantar da hankalinshi zai aura mishi wacce mishi wacce yakeso, anty amarya ta fito itama tasa baki cikin kissa ta nuna batasan me ke faruwa ba kuma ta rufe abba da fada kamar da gaske tace ya tashi maza yaje ya bawa mummy hakuri, suka dinga tausar shi da alkawarin duk randa yake so za'a aura mishi sanah, daddy Allah yasani bai so jin sanah danshi ke so ba, amma saboda kunyar idon anty amarya yasa ya amince amma sam dabi'uta da rawar kanta basu mishi ba.... Mrs tijjani shattima.... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 2⃣4⃣ By Aysha Ya'u Kurah Daren wannan ranar ya zama dare mai zafi a gurin zulfa'u, ko kadan bata runtsa ba, in ta tuno kalaman mutumin da ta dade cikin kogin sonshi da son ganinshi sai kuka mai tsanani ya kufce mata, da taga zuciyarta na neman bugawa ta mike ta shiga bayi tayi alwala tayi sallah ta dinga adduar neman zabin Allah... Bayan sallar asuba ta fito ta nufi kitchen dan hada ma twins breakfast da lunchbox, ta zauna tana fere dankali, farouk ya shigo kitchen din, tsugunawa yayi agabanta, ta dago kumburarrun idanuwanta tace ina kwana yaya farouk, ya kafeta da ido yace lafy lau, ya kwanan kuka? tayi murmushi tace ni banyi kuka ba, yace nasan bakiyi kuka ba, bacci kikayi ya maida fuskarki haka ko? ta sunkuyar da kanta idonta ya ciko da kwalla, Cikin tausayi yace kiyi hakuri zulfah, komai zai wuce, wata rana sai labari, komai ya faru dake rubutacce ne bazaki taba tsallakeshi ba, kiyi ta addua idan aurenki da abba akwai alkhairi Allah ya daidaita ku, idan babu alkhairi Allah ya kawo rabuwarku cikin sauki ba tare da wata fitina ba, ""AMEEEEEN'" sukaji an fadi da karfi, suka daga kansu suka ga sadeeq da ya dawo daga masallaci a bakin kofar kitchen, zulfa'u ta sunkuyar da kanta da sauri ta cigaba da fere dankali, ya harareta cikin tsana da kyama yace da ko kin kyautawa kanki in har kikayi wannan adduar dan ko kadan aurena dake babu alkhairi, kema kinsan a yadda nake dinnan ban kamaci mace irinki ba, ki taimaki kanki kije ki samu mummy ku warware duk wani kullin da kukayi dan wallahi bazan taba sonki ba yaja dogon tsaki ya fita, Kukan dake makale a makoshin zulfah ya fito da karfinshi, zuciyarta ta kasa jure muggan kalaman sadeeq, tabbas da wani ke bata labarin cewa sadeeq din da take matukar kaunar ganinshi zaiyi irin wannan halin bazata yadda ba, kuka ta dingayi,, farouk ya kasa jurewa idonshi ya ciko da kwalla ya tashi ya fita da sauri,,, Saida tayi kuka mai isarta sannan ta cigaba da aikinta.... Mrs tijjani shattima... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 2⃣5⃣ By Aysha Ya'u Kurah Tunda ya shiga daki ya kwanta bacci ya daukeshi sai after 12 ya tashi yayi mika ya shiga wanka, yana fitowa ya dauki wayarshi dake ta faman ruri tun yana bayi, ya daga yace mutumina ya akayi ne, daga daya bangaren yace baka da kirki marafa ashe dama da gaske ka shigo gari, jiya zabba'u ke fada min ta ganka ban yarda ba saboda I clld u a kashe ashe da gaske kai din ta gani, sadeeq yayi dariya yace Hilal complainer, walhy shigowar yamma nayi kuma banje ko ina ba ina gida dama ina shirin kiranka zaka dan rakani abuja, hilal yace ok gurin karfe nawa, sadeeq yace gurin 4 haka dan acan zamu kwana, hilal yace kwana marafa, sadeeq yace yess please karka ce bazaka je ba gobe zamu dawo in shaaa Allah, hilal yace to bari in gani zanzo arnd 3, sadeeq yace yauwa abokina ko kaifa sai kazo akwai gist, suka dan taba hira kafin su aje wayar... Karfe uku da kwata hilal yaxo gidan lokacin sadeeq na zaune yana shan farfesun da anty amarya ta mishi, yana ganin hilal ya mike cikin farin ciki yace dadi na dakai cika alkawari suka tafa, a tare suka zauna cikin jindadi dan sunyi missing juna, hilal yace mummy na ciki ne, sadeeq yace eh tana ciki bari in gama muje ka gaisheta, saida suka gama sannan suka mike sukayi hanyar dakin mummy sadeeq yana adduar Allah yasa kar ta mishi abinda ta mishi dazu da yaje gaisheta,, yana murda kofar sukayi karo da zulfah bowl din farfesu ya fadi kasa romon ya dan fallatsan ma hilal, ta ja baya da sauri ta tsuguna tace dan Allah kuyi hakuri wallahy bansan zaku shigo ba,, sadeeq yayi tsaki a hankali saboda idon mummy, hilal yayi murmushi yace babu komai tashi kije ta mike da sauri ta fita hilal ya bita da kallo ta gefen idonshi, mummy ta kalli hilal tace kayanka sun baci sosai ko hilal, yayi murmushi yace a'a mummy kadan ne zanje in canza wasu, ina wuni? Tayi murmushi tace lafy lau ya ummanka, yace tana nan lafiya tace in gaisheki, tace ina amsawa zabba'u ta guje mu kwana2, yace wallhy makaranta ce ta boyeta, tace ayya Allah ya bada sa"a, yace ameen mummy,, saida shuru yadan ratsa na tsawon minti biyu sannan sadeeq da kanshi ke kasa tun shigowar su ya dago kai yace mummy zanyi tafiya xanje abuja, saida ta dau lokaci dan kar hilal ya gane wani abu ta maida kallonta gurinshi tace hilal da kai xa"ayi tafiyar kenan yace eh mummy, tace to Allah ya tsare a dawo lafiya, sukace ameen dukansu sannan suka tashi suka fita,, Sadeeq ya kalli hilal yace muje ka canza kaya wadannan sun baci, hilal yace no muje sai in biya ta gida in canza mu wuce, amma bansan yarinyr nan ba marafa yar uwarku ce, sadeeq ya harareshi yace yar aiki ce, hilal yace kaiii haba, amma tanada kyau ni da zaka shige min gaba a bani ita in aura ai da naji dadi, sadeeq da karfi yace wannan karamar yarinyar hilal yadda kake dinnan, hilal yace kaifa banza ne, irinsu ake aure ay, wallhy wannan nan da 2yrs bazaka ganeta ba, ay ni nafison irinsu, da wayayyun matan nan na zamani wanda suka gama zama fanko, gara in auri sweet16 muyi zamanmu lafiya batasan wani ba in ba ni ba,, Sadeeq yaja dogon tsaki yace lallai abincin wani gubar wani ni banga abinda zanyi da wannan kwailar ba wallahy, hilal yace kai kace ay, kai ay dama daban ne kafi dealn da manyan mata niko irin wadannan sun isheni in mori kuruciyata a gurin mai kuruciya, sadeeq yace dalla tafi can ni wuce muje kar muyi dare, hilal ya dan waiga yace to dan kirata mana in ganta da kyau, sadeeq yaja tsaki ya dauki keyn mota ya fita yace ka shiga ka kirata da kanka, hilal ya fito yana dariya suka shiga mota suka wuce.... Mrs tijjani shattima... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 2⃣6⃣ By Aysha Ya'u Kurah Tun bayan isha'i suke kofar gidansu sanah har gurin tarah sanah bata dawo ba, hilal cikin kosawa yace nagaji da zama anan marafa, ko yar gold ce wannan ay sai ka bari gobe ka dawo ko, wace macen kirki ce zata kai wannan lokacin a waje, ni dai na gaji wallhy!! Sadeeq ya kalli agogon hannunshi yace kayi hakuri mu kara mata 5mins in har bata dawo ba sai mu wuce, hilal yayi tsaki yace yau zanga wannan yarinyar da ta ruda min marafa, sadeeq ya lumshe idonshi yace aiko zaka ganta abokina, ta hadu karshen haduwa, ni kaina na kagu in ganta, hilal zaiyi magana ganin wata bakar land crusher da tayi parking a kofar gidan ta hana shi, Sanah ce ta fito daga cikin motar da wani matsatstsen wando da rigar da dakyar ta kai mata cibiya, saida ta tsaya ta gama magana da mutumin dake motar sannan ta dago tana dariya tana daga mishi hannu, Fulll light sadeeq ya saki cikin kunan rai ya haskata sosai, hilal ya kalleta sosai yace subhallahi marafa badai wannan bace sanah?? Sadeeq bai bashi amsa ba ya bude motar ya fita cikin bacin rai, sanah ta karaso gurin cike da masifa, tace malam wani irin iskancine wannan zaka has--- maganar ta makale a makoshinta saboda ganin sadeeq, taji tsoro a can cikin zuciyarta saboda ganin da yayi mata da wani, amma da ta tuna abinda ke tsakaninsu sai ta dake taja tsaki ta juya tayi hanyar shiga gida da sauri har yana tuntube yabi bayanta, ta kara sauri ta shige gida, har ta kama kofar parlor zata bude ya cimmata, ya janyota da karfi kamar zai cire mata hannu, tayi yar kara tana ture hannunshi, ya kara matse hannunta yace uban waye ya saukeki a wannan lokacin, ta harareshi tace ban sani ba, ni dalla malam ka sakeni, zuciyarshi kamar wuta yake jinta ya kalleta daga sama har kasa yayi tsaki yace kalli yanda kika fita duniya suka gama ganinki a haka wasu irin matsiyatan kaya ne wannan,, ta daka mishi tsawa tace nasa din in ma nayi yawo tsirara Ina ruwanka, dan Allah ka sakeni kafita harkata kaje can ka zauna da zabin mahaifiyarka ka barni in auri wanda zai soni familynshi ma su soni, ya murde hannunta cikin fushi yace ni kike fada ma wannan maganar, ta fashe da kuka sosai tace na fada maka din, dan Allah ka rabu dani karka fama min ciwon da ya fara warkewa a zuciyata,, kayi nesa dani ko zan samu saukin abinda nakeji game da kai, jikinshi yayi sanyi ya rungumeta sosai a jikinshi, murya kasa2 yace haba sanah ya kike so inyi da raina, kinsan irin wahalar da nake sha a kanki, kinsan irin matsalar da nake fuskanta yanzu a gida kuma duk a kanki, plss karki kawo karshen soyayyarmu saboda auren da ban daukeshi aure ba, kinsan ke nakeso kuma bazan taba iya hada sanki da wata ba,, ajiyar xuciya tayi saboda dadin jinta jikin sadeeq, wani irin sonshi takeji yana ratsa ko ina na jikinta, amma dole ta dan wana shi kadan, cikin muryar kuka tace nidai na fada maka ka rabu dani bazan iya aurenka ba, bazan iya kallon wata mace na amsa sunan matarka ba bare har in iya sharn dinka , na rokeka ka kya--- da sauri ya katseta yace karki min haka sanah, wallahy zuciyata zata iya bugawa, dan Allah kar kiya punishn dina da laifin da bansan dashi ba, ta dago kanta tace amma ay kasan yadda zakayi dashi, cikin rashin fahimta yace ban gane ba, tace ay ba daura maka ita akayi a kafa ba, kana da ikon sakinta tunda ikon a hannunka yake, cikin rawar murya yace "saki "fa kikace, ta daure fuska tace kwarai kuwa, ko bazaka iya bane, ya kara matseta ajikinshi, yace zan iya mana baby, lokaci nake jira, dan yanzu mummy na cikin fushi zata iya aikata komai in na sake ta, amma kisa aranki bani da aure dan ban dauki auren nan a bakin komai ba wallhy, taji dadi sosai, ta dago kanta tace haka dai kace, yace I mean it "sajna", "kasam se!" Ki yarda dani, ta dan bugi kirjinshi tace ni ban iya yaren india ba, yayi murmushin jindadi yace dole ki koya cwthrt, nan suka cigaba da soyayyarsu ta mantar dashi bacin ran da ya shiga na ganinta da wani, Hilal da ya gaji da zaman jirah ya bude motar ya fito yana tsaki yace lallai wannan dan iskan ya raina min hankali, kofar gate din ya shiga ya hango su manne da juna, ya karasa ranshi a bace, saida yayi magana kusan sau uku sannan suka dawo hayyacinsu, yayi tsaki cikin kyama ya kalli sadeeq yace wani irin iskanci ne zaka barni a waje kamar wani driver, wallhy inda nasan haka zaka min da babu abinda zaisa in baro abubuwa masu muhimmaci in rakoka, sadeeq ya matso kusa dashi yace sorry friend, wallhy na manta ma kana waje, ay dole ka manta, bani mukulli hilal ya fadi yana hararar shi, sadeeq yace calm dwn abokina baku gaisa da gimbiya ba, yayi tsaki ya waiga ya kalli sanah da ke kallonshi itama, zaro ido hilal yayi sosai ya maida kallonshi gurin sadeeq, yace marafa wannan ce sanah, sadeeq yace yess itace rabin raina, ita nake burin ta zama uwar ya'yana, hilal yayi ajiyar zuciya yace to Allah ya taimaka sannu amarya, murya can kasa tace yauwa ina wuni, lafiya lau kawai yace, ya kalli sadeeq yace bani key in wuce sai kazo, sadeeq ya mika mishi key yace okk sai na taho, hilal bai kulashi ba ya sa kai ya fita yana tausaya ma abokinshi.... Mrs tijjani shattima... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 2⃣7⃣ By Aysha Ya'u Kurah Hilal tsaye jikin window a hotel din da suka sauka, ya kalli agogo a karo na uku 11:43 ya maimaita da bakinshi, yace lallai marafa ya fada tarkon yarinyar nan, dole in taimaki abokina bazan yarda tayi destroying rayuwarshi ba, bazan yarda ya aureta har ta haifa mishi gurbatattun ya'ya ba, yana ta "safah da MARWAH" a cikin dakin, ko abinci kasa ci yayi, sai after 12 sadeeq ya shigo, hilal ya dago kai ya kalleshi, sadeeq yace bakayi bacci ba, hilal yace umm banyi ba, sadeeq ya daga kafadunshi ya shiga toilet saida yayi wanka sannan ya fito, spray kadai ya fesa ya kunna tv, Hilal yace marafah inada magana da kai, sadeeq ya hade rai sosai yace ina jinka, ya dawo kusa dashi yace akan yarinyar nan da kakeso ne marafah, sadeeq yace uhumm ina ji, yace yarinyar nan bata dace da kai ba abokina, nasan yarinyar nan wallhy bata da kamun kai ko kadan, bai dace ka dauko ma familynka wannan yarinyar ba, wace irin amsa ka tanadan ma ya'yanka in suka taso suka ga mace kamar wannan a matsayin mahaifiyarsu, kayi tuna'--- enough sadeeq yace da karfi, I hv hrd enough hilal, nasan kasanta ta fada min komai, hilal baki bude yace ta fada maka komai kuma kake sonta a haka, sadeeq yace yess me zai hana, ka bani kunya hilal, dama ashe yadda kake nuna kai ustaz ne ba haka bane ashe green snake ne kai, ashe ma gara ni duk iskanci na bazan taba neman yin sex da mace ba, wallhy ka bani kunya hilal, Hilal cikin rashin fahimta yace ban gane ba fa, me kake nufi, sadeeq yace sanah ta fada min komai, ta fada min ka nemeta har ka dauketa ka kaita wani guri kana neman raping dinta Allah ya kwaceta a hannunka, ta fada min komai kuma nasan bazata min karya ba kuma bazata taba zubar da mutuncinta a waje ba, dama ta fada min kace zakayi komai dan ka bata mata suna tunda taki yarda da kai, shine zaka zo ka tsara min karya da gaskiya dan in yarda da kai, mtsww yaja tsaki ya juya cikin bacin rai, hilal ya dafe kanshi dan baida mafita a cikin maganar nan, lallai yarinyar nan ta kware sosai a iya sharri, ya kalli sadeeq cikin damuwa yace ka yarda da abin da tace maka kenan ni baka yarda da abinda nace ba, tun muna yara muke tare da kai marafa, kasan komai nawa nasan naka, kasan abinda zanyi nima haka, kasan bana maka karya bama taba boye sirrikan junanmu, amma a yau ka yarda da maganar macen da baku wuce wata biyu tare ba, ka bani mamaki marafa, ba wani mamaki dalla malam sadeeq ya fadi da karfi yace mutum na iya canzawa lokaci daya, kai da bakinka kace min kasanta kafin ma in fada maka komai, saboda haka babu abinda zaka fada min in yarda, hilal idonshi yayi ja sosai yace lallai marafa ka hadu da makirar mace, wallhy wannan zata rabaka da kowa naka ciki harda mummy da daddy, nagode sosai da maganganun da ka fada min, Sadeeq yaja tsaki ya cigaba da kallonshi yana fadin maganganu marasa dadi, hilal ya koma gefen gado ya dafe kanshi, yayi alkawarin gobe da wuri zai tafi, zai rabu da sadeeq duk ko da irin shakuwar da sukayi zai cigaba da mishi addua har Allah dawo dashi kan hanya, kalmar "fasiki" da sadeeq ya ambatawa hilal ita tafi bata mishi rai, a ranar hilal bai runtsa ba saboda bacin rai, ana idar da sallar asuba ya wuce tashar mota ya hau ya taho kaduna.... Sadeeq na tashi yaga baiga hilal ba, yayi tsaki yace wannan kuma shi ta dama, son sanah ya rufe ma sadeeq ido ya dauki yarda ya bata, ta fada mishi karya da gaskiya akan hilal da dan uwanshi Nurain, tasan dole in nurain yaji zai aureta ya fada mishi abinda ya faru ita kuwa zata iya komai dan taga bata rabu da sadeeq ba, zuciyar sadeeq cike take da tsanar hilal da Nurain, ya tsani namijin da bazai iya kama kanshi har ya auri mace kafin ya nemi biyan bukata a gurinta, godiya ya dinga wa Allah da ya hada shi da sanah, mace kyakykyawa ga aji, gashi bata zubar da mutuncinta gurin wani ďa namiji ba, (tabdijam), Jalila je ki kiramin farouk, Kuma kice ma zulfah ta shirya kafin ya fito, jalila ta rufe laptop dinta tace mummy ni wallhy kinsan nafi son a kaita boarding, kinga gara a kaita ko Dambo ne zata fi maida hankali akan karatu kuma hankalinta zaifi kwanciya, amma anan ga anty amarya ga yaya abba in ya dawo damuwa zata hanata karatu, acan kuwa zata hadu friends ta mance damuwa ta yi karatunta ko ya kikace, mummy tace umm kuma maganarki haka take, ni matsalata da dambo wannan ďangalallen uniform din, kinga ita matar aure ce, jalila tace zata iya sa tyt har kasa mummy, dan Allah a kaita can zan hadata da juniors dina wallhy zataji dadin makarantar sosai,, mummy tace to shikenan bari nurain ya shigo inji ta bakinshi, je ki kirata suje capital school anso result, tace to mummy, ta tashi ta fita cikin jindadi.... Mrs tijjani shattima... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 2⃣9⃣ By Aysha Ya'u Kurah Ranar monday da safe suka yi shirin kai zulfah makaranta, tayi kyau sosai cikin uniform dinta white long sleeve top da blue burberry skirt dan karami, ta daura blue suit akan rigar da necktie irin skirt dinta,, mummy tayi mata nasiha sosai wanda tace tuni ne dan nasan zaki kama mutuncinki, ki kula sosai da karatu, ba ruwanki da kawayen banza, jalila tace mummy karki damu akwai yaran da zan hadata dasu kuma basu da matsala, mummy tace to Allah ya bada sa'a sai munzo visitn, suka fito parlour mummy na daga musu hannu, anty amarya na zaune a parlon tayi tsaki da taga sun fito, suka gaisheta ta amsa da kyar, suka wuce dakin daddy, nan ma nasihar yayi mata sannan ya kara bawa jalila kudi in taje skull ta canza mata, jalila tace lallai kudi sun miki yawa, ga na yaya nurain inga ticket din kudin,, ta bude jakarta tana dariya ta fito mata dashi, jalila tace wuu kudin sun miki yawa bari in ajiye maki wannan a account saboda wasu bukatu, zulfah tace to amma wadannan takardun sune kudi a makarantar, jalila tace eh ki ajiyesu da kyau duk abinda zaki siya ki tafi dashi zasu baki, zulfah ta kara boye shi a jakarta suka wuce, Admin block sukaje nan aka bawa zulfah class da hostel, ss1 science suka bata da kyar dan nurain ya roka da art zasu bata saboda performance dinta a interview is poor, class din suka nufah da wani teacher wanda naji jalila na kiranshi da mr Samuel, sun tarar da physics teacher a class din mr samuel ya shigo dalibai suka gaisheshi, Ya amsa, ya gaisa da mr badore sannan yayi introducing new student a gurin sauran daliban, sit din kusa da wata kyawawar yarinya a ka zaunar da ita, Yarinyar ta yafito hannun jalila tace anty jally ya kike, ta shafa fuskarta tace am fyn Rolex,, ga kawa nan na kawo muku, ina frisky, Rolex tace tana commerce, jalila tace zan bi ta class dinsu ku riketa amana kinji, rolex tayi murmushi tace karki damu anty jally hostel dinmu daya, jalila tace eh, rolex tace to babu komai Allah ya zaunar damu lafiya, ameen jalila tace sannan ta fita tana daga ma zulfah da idonta ya ciko da kwallah hannu, Physics teacher ya gama koyar dasu sannan geography ya shigo, daga shi sai break, ana fita break rolex ta koma kusa da zulfah tace hii, am Habiba Usman by name nd uu, zulfa tace Zulfa'u Adam, rolex tamika mata hannu tace wow nyc name, nyc to meet u, da fatan zamu zama kawaye, zulfah tayi dariya ta mika mata hannu itama tace in shaa Allah, da gudu frisky ta shigo class din ta zauna kusa da rolex, ta kalli zulfa tace rolex wannan itace new comer din da anty jally ta kawo, rolex tace eh mana, frisky ta mika mata hannu tana murmushi tace am Farida yakubu da fatan mun zama kawaye, zulfa tayi murmushi tace eh, rolex ta amshi skul bag dinta ta ajiye a locker suka fita yin break.. Ana tashi suka tayata kwasan kaya suka wuce hostel, cornersu suka shiga duk suka zazzauna suna maida numfashi, tare suka shirya kayan, kawayensu duk in zasu wuce sai sun shigo sun gaisa da newcomer, saida suka shirya komai sannan suka kwanta dan su huta kafin la'asar tayi, zulfah dai na kallonsu itama ta kwanta tana tunanin irin rayuwar kuma da zatayi a skull, gashi sam bata gane yadda malaman suke koyarwa, tunanin su jalila ta dinga yi tasan yanzu yan biyu sun dawo gida ta share hawayenta ta runtse idonta ko zatayi bacci... Mrs tijjani shattima.... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 2⃣8⃣ By Aysha Ya'u Kurah Satin sadeeq biyu, duk inda zulfah tasan zasu hadu bata binshi, shi kuma gareshi hankalinshi kwance yake saboda sun shirya da abin sonshi, soyayyarsu sukeyi baya tuna kowa sai ita, damuwarshi daya yadda mummy ko kallon inda yake batayi a gurin daddy, anty amarya da anty laila kadai yake samun sauki, yadda mummy da nurain ke mishi abin na matukar damunshi amma wani bangare na zuciyarshi ya kitsa mishi gara hakan saboda yana free lyf dinshi ba'a mashi maganar wannan kucakar yarinyar,, duk bayan two days yake zuwa abuja gurin sanah har ya koma da matukar kewarta, dan shi da ta yarda ma da anyi aurensu tun yanzu ya tafi da ita amma sam taki yarda, tace sai nan da 1yr in ta gama makaranta haka ya yarda badan ranshi yaso ba... Cikin kwanaki Nurain ya gama ciku cikun nema mata makarantr dambo international school dake barnawah kaduna, ya gama mata komai har uniform da sport wears sun bata, ranar saturday suka tafi shopping ita da jalila, provision jalila tayo mata kamar hauka, babu abinda bata siyan mata ba wanda tasan zata bukata na amfani, haka suka je ta siya mata tyt milk, ash nd white saboda uniform dinta, sai gurin yamma suka dawo gida, anty laila ta tayasu shirya kayan suna hira dukansu, mummy ta shigo tace ma zulfah gobe ki shirya kije ki gaida mahaifinki kinji, zulfah cikin farin ciki tace to mummy,, murna zulfah ta dinga yi zata je taga babanta, ta rasa abinda zata rike ta kai mishi yaji dadi.. Karfe biyu driver ya dauko su ya kawosu babbar saura, zulfah kamar zata balla kofar ta fito saboda murna, dai2 gidansu motar tayi parking, suna fitowa suka fara jin hayaniya a zaure, marka ce ta fito ita kadai take masifarta tana ganin zulfah tayi turuss tana kallonta, zulfah ta tsuguna har kasa tace ina wuni goggo, marka tabi zulfah da hararar bakin ciki, tace da ban wuni ba zaki ganni, uban me ya kawoki gidana, ko matsiyacin ubanki bai fada miki karki kara zuwa gidan nan ba, idon zulfah ya ciko da kwalla, jalila tayi ma goggo kallon rashin kunya tace ke kuma baiwar Allah me yayi zafi haka, daga magana sai zagi sai kace wacce take jira, marka ta harari jalila tace na zaga din dan uwarki, kema na zageki ko kina da abinyi, jalila cikin bacin rai tace banda abinyi amma zaki gane ba'a zagan min uwa a kwana lafiya, "Isah" ta kirah drivern da ya kawo su, ya fito da kakin sojoji ya sara mata, tace maza ka kama min matar nan mu tafi da I--- ay goggo bata jira jin karashen ba ta ari na kare da gudu tana ihun neman dauki, jalila ta dago zulfah tace sorry sis kar dan wannan abun yayi spoiln mood dinki, kin fita har abada shiyasa take bakin ciki, yanzu ina ne kike ganin zamuga baba, zulfah ta share hawayenta tace mu shiga gidan goggo ameena in tambayeta, jalila tace ma isa suna zuwa, suka shiga gidansu fa'ee da sallama, fa'ee na daga baya tana wanki ta amsa tana goge hannu, tace waye, zulfah ta karasa bayan ta dafa bayanta tace fa'ee ni ce, da sauri fa'ee ta waigo suka hada ido ta kurma ihu ta rungume zulfah, tana fadin goggo ki fito ga zulfa'u, goggo amina da ta gama suyar gyada marau, ta kashin gida dan ta huta ta mike da sauri tace wace zulfar, fa'ee tace zulfar inna saude ta gidan su marka, da sauri ta fito itama ta rungumeta harda yar kwallar farin ciki, suka ce zulfah ke ce kika zama haka a cikin wannan dan lokacin, kai Allah na gode maka da ka nuna min wannan ranar da zulfah ta fita daga kangi, Allah ya jikan saude da rahama goggo ameena ta fadi tana share hawayen da daga gani na farin ciki ne, zulfah tace ameen, tare muke da bakuwa, goggo ameena tayi sauri ta kalli jalila, tace yi hakuri yar nan, zo muje ciki ku huta, suka shiga daki dukkansu, goggo ameena ta basu mafici ta fito ta kira fa'ee ta kwance bakin zaninta ta bata dari biyu tace ta siyo musu lemon kwalba a shagon tanimu,, sannan ki dauki kular babanku ki amso min bashin alalen gwangwani na naira 100 a gidan atine kice gobe zan kawo kudin kuma tasa miki manja da yaji da yawa, kiyi sauri fa,, fa'ee ta fita da sauri tana murna, cikin minti biyar ta dawo da fanta mai sanyi da alalen gwangwani mai kyan gaske (ni kaina ya bani sha'awa) cokula goggo ta debo musu da kyar jalila ta fara ci, tana fara ci taji da dadi suka cinye duka dan atine alalenta baya kwantai saboda yadda take gyarashi, suna gamawa suka kora da fanta, goggo ameena taji dadi da sukaci abincin saida sukayi sallah sannan suka fara hira, ta tambayi goggo ina babanta, goggo ameena ta gyara zama ta bata labarin duk abinda ya faru ranar aurenta da auren salaha da kuma tafiyar babanta da kabiru kano, tace ki kwantar da hankalinki babanki na cikin koshin lafiya, dan suna haduwa da malam kuma yana kewarki kema, ita kuma marka tana ganin sakamakonta amma har yanzu bata san annabi ya faku ba, dan babangida ya auri hanne bayan ya auri salaha, kullum cikin fada suke basu da wani kwanciyar hankali, yanzu haka delu ta tafi rabon fada itama marka nasan can ta nufa yanzu da kuka ganta, in kikaga salaha da hanne bazaki ganesu ba saboda masifa da bala'i ke abin dai babu dadi, zulfah tayi ajiyar zuciyar jin lafiyar babanta kalau tace to alhamdulillah goggo dan Allah kice ma baban garbati in yaje yace ina gaisheshi sosai, goggo tace in shaa Allah zan fada mishi, an sa ranar kawarki fa'ee nan da wata uku, zulfah tace iyye, fa'ee wa zaki aura, fa'ee ta ruga waje da gudu cikin kunya, goggo ameena tace malam labaran,, zulfah tace Allah sarki yayan malam saleem aiko na mata murna wallhy, waiko goggo kinajin labarin malam saleem, fa'ee ta shigo tace eh mana ai tun tafiyarki da sati daya ya koma makaranta yanzu naji ance yana Singapore, jalila tayi murmushi dan tasan mummy ce tayi sponsoring dinshi da ya samu school a can, sun dade suna hira sai 5 suka tashi tafiya, jalila ta bawa goggo dubu goma da alkawarin in biki ya zo zasu zo in shaa Allahu, zulfah ta ja hannun fa'ee ta bata dubu biyar cikin kudin da farouk ya bata kafin ya tafi school, tace koda bana nan zakiyi aure ki siya wani abun dashi, fa'ee tace ina zaki je, zulfah tace makaranta zan je, ta zaro ido tace a ina, Zulfa tayi dariya tace anan garin mana, fa'ee tace kinji dadinki nima malam yace zan cigaba da makaranta, Allah ya bada sa'a zulfah nayi matukar kewarki wallhy, zulfah tace nima haka fa'ee Allah ya sanya alkhairi, suka fita ta shiga mota kamar kar su rabu, a cornerr shiga layinsu ta hango delu da marka suna tafe suna masifa kamar karnuka, wasu mata na binsu a baya suna kallonsu, ta runtse idonta tayi hamdala ga Allah da ya cireta a cikin wannan rayuwar, Allah ya bata sa'a a karatunta ya daurata akan malamai da ďaliban makarantar.... Mrs tijjani shattima... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆3⃣0⃣ By Aysha Ya'u Kurah Satin ta uku a makaranta ta fara sabawa da komai na makarantar da taimakon Allah da taimakon kawayenta da basu barinta ta taba komai a provision dinta, komai da nasu ake amfani a corner, haka a class duk abinda da bata fahimta ba rolex na koya mata, wanda itama rolex bata gane ba sai suyi gruo discussion da su charity Ameh da wani ibrahim Adam, yaron nada kokari sosai, a haka har Allah ya taimaketa ta gane duka subjects din musamman chemistry tafi jin dadin shi.. Rayuwarsu sukeyi gwanin sha'awa su uku gasu dukkansu kyawawa, kuma suna girmama malamai da seniors dinsu, wannan dalilin yasa ake kaunarsu duk inda suka shiga, zaman zulfa'u dasu rolex yasa ta kara wayewa, tazama yar gayu sosai duk ranar saturday da daddare suke yin social nyt, ranar sunday kuma su zauna suyi hirar gidajensu cikin nishadi da kawaye, rayuwar danbo tanada bambanci da sauran boarding skull saboda babu takura in dai ba a bangaren karatu ba, kasancewar ta mixed school baisa yaran cikinta lalacewa, kuma duk yaran masu hannu da shuni ne a ciki, zan iya cewa zulfah nada sa'a a rayuwarta domin wani dan mai kudin ma bai samun damar shigowa makaranta irin danbo, shiyasa takema mummy da duk zuriarta adduar samun aljanna, ta cire tunanin sadeeq a ranta duk da sonshi na nan makale cikin zuciyarta, kullum tana adduar Allah ya fitar mata dashi ta huta, tasan Allah maji rokon bawa ne wata rana son zai fita in shaa Allah... Kwanaki, watanni, sun shura an tasan ma shekara, daga anyi hutu ake zuwa daukarta a makaranta, haka suna ziyartar junansu da rolex da suke zaune a malali, sai frisky dake zaune a kinkinau, Bangaren sadeeq kuwa saura kiriss ya kare karatun shi, duk hutun da yake dawowa baya ganin zulfah hakan yafi mishi dadi, kuma bai taba tambayar ina take ba, haka babu wanda yace mishi ga inda take, yasan dai anty amarya tace makaranta aka kaita, duk tunanin anty amarya sadeeq ya saki zulfah shiyasa aka kaita makarantar kwana, shiyasa suke kulle kullensu ita da kanwarta Aneesah da kuma maman sanah, zaunar da sanah sukayi suka sata a gaba akan ta yarda suyi aure da sadeeq tunda ya matsa, kar hakurinshi ya kare ya hakura ya nemi wata, nan dai suka ingizata ta kirashi tayi mishi kissarta da ta saba, sannan ta mishi maganar aure, kamar jira yakeyi ya mike tsaye yanata murna yace zaizo gida nan da 2wk in sun gama final training, ranar sadeeq saboda murna har party ya hada a makaranta, farin cikin da yake ciki ba mai misaltuwa bane, sai gurin 2 yayi bacci saboda farin ciki.. Ranar da suka gama bai jira komai ba yayi airport dan baiso ko kadan ya bata lokaci, suna isowa ya dauki drop ya taho kaduna, sai bayan isha'i ya shigo gida, da murnarshi ya karaso cikin parlon inda daddy ke zaune, ya durkusa ya gaida mummy, ta amsa mishi ba yabo ba fallasa, ya juya gurin daddy ya gaisheshi, daddy yace shine ko ka kira kace kana tafe, yayi murmushi yana sosa keya, nurain ya shigo parlon sadeeq ya gaisheshi ya amsa ya cigaba da magana da mummy, daddy yace aje ayi wanka a huta ko babana, sadeeq ya sunkuyar da kanshi dan baijin zai iya barin gurin bai fadi abinda ke ranshi ba, anty amaryace ta shigo, tana mishi sannu da zuwa fuskar nan tata kamar gonar auduga, ta nemi guri kusa da daddy ta zauna, sadeeq yaji dadin zuwanta kuma ya samu kwarin gwiwa, amm ummm dama--- daddy yayi dariya yace fadi mana babana, menene, yace umm daddy dama inaso ka nema min auren sanah ne iyayenta sun ce a turo, SANAHHH nurain ya fadi da karfi hade da mikewa tsaye.... Mrs tijjani shattima... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆3⃣1⃣ By Aysha Ya'u Kurah Anty amarya ta saci kallon mummy da daddy dan taga rction dinsu, basu ce komai ba amma farar fuskar nan ta mummy ta canja tayi jawur saboda bacin rai, Nurain ya kalli sadeeq cikin daga murya yace wace sanar, sadeeq wit his fl confdnc yace sanah dai da ka sani, Nurain zufa ta keto mishi yace kana cikin hankalinka kuwa abba, to in ma hankalinka baya jikinka kayi maza ka nemoshi dan wallahy bazaka auri wannan yarinyar da ita kanta bata san adadin mazan da tayi mu'amala dasu ba, anty amarya ta rushe da kuka tace sharrin da zakayi ma sanah kenan, wato dan ta rufa maka asiri shine ita zaka bita da sharri ta mike tayi daki tana kukan munafurci, daddy hankalinshi ya tashi dan baya son hayaniya ko kadan, yace zunnurain me kake fadi haka, yace wallhy daddy yarinyar nan bata da maraba da karuwa, cikin bacin rai sadeeq ya tashi yace sai dai in kaine bakasan yawan matan da kayi mu'amala dasu ba, amma wallhy sanah kamamiyya ce, haba yaya nurain dan ka nemeta da fasikanci taki yarda shine zaka bita da sharr--- cikin bacin ran maganarshi nurain yayi kanshi ya dinga marinshi yana dukanshi ta ko ina, da kyar daddy ya iya janye sadeeq, fuskar nurain ta canza gaba daya jikinshi sai rawa yakeyi yace ni kake fada ma wannan maganar, wace mace ce ta isa in nemeta da faskinci, babu ita har duniya ta nade, sadeeq murya a dashe yace karya kakeyi wallhy ka nemeta bazata maka karya ba, kuma sanah ta isa ka nemeta saboda har ka mutu bazaka samu mace kamarta ba, Nurain cikin fushi ya kara yin kanshi, mummy dake kuka ta rikeshi tace barshi nurain, ranka ya daina baci nasan abinda zakayi nasan kuma wanda bazaka yi ba, yaje na yarje mishi aurenta yaje ya aureta ta zame mishi uwa wuce muje, ta kama nurain suka wuce daki tana kuka, daddy ya zaunar da sadeeq ranshi a bace yayi mishi fada sosai akan abinda yayi ma nurain, sadeeq da zuciyarshi ta kangare yace wallhy daddy da gaske ne abinda na fada bakaji anty amarya ma ta fada ba, daddy yace ya isheni nace, gobe zanje nema maka auren kowa ya huta, tashi kaje kaci abinci ka huta, sadeeq hankalinshi ya kwanta ya mike yayi dakinshi yana jin dadi, daddy ya runtse idonshi zuciyarshi na tafarfasa, baya kaunar wannan auren amma haka zai yarda ayi kuma yasa a dagema danshi da addua saboda yana cikin halaka, A dakin mummy kuwa nurain na zaune yana rarrashinta shima idonshi jajur, da kyar ya lallabata ya tashi ya tafi daki yana tunanin yadda sanah ta maida mishi sadeeq wawa, babu abinda ke mishi yawo a kwakwalwa kamar sharrin da sanah ta mishi, wato shi bai fadi abinda tayi mishi ba, shine tayi saurin yin rigakafin sharri, abubuwan da ta mishi ya shiga dawo mishi, Tunani*** a ranar da abun ya faru ya dawo gida lokacin duka yan gidan basu nan suna asibiti gurin maman anty laila, yana shigowa ya tarar da sanah da skirt da brazia, babu ko riga a jikinta kuma jin parking din motarshi ne yasata saurin ciresu, ta mike a kan doguwar kujera, yana shigowa ta tashi ta matso kusa dashi ta shigeshi sosai tana shafa kirjinta tana magana kasa2, ya kalleta cikin kyama yace kee meye haka, tace wallhy zafi nakeji yaya muje in tayaka hutawa, nasan ka kwaso gajiya ta fara goga kirjinta a jikinshi, runtse idonshi yayi ya turata ta fadi sosai, yace kina da hankali kuwa, ni kikeso in fadawa tarkonki in sabi Allahna, to ki canza taku dan baki da jikin da zaki yaudareni dashi Allah na tsareni daga kaidin fajiran mata irinku, yayi tsaki ya wuce daki ya barta a gurin, cikin kunan rai ta mike tana huci tace wallhy yau saina nuna maka ni din nan jikina ya isa in yaudareka, saida ta kusa minti 2, sannan tayi side dinshi, a parlonshi ta cire komai na jikinta, ta fada dakinshi da gudu tsirara, lokacin yana daure da towel zai shiga wanka ta fado jikinshi tana fadin yaya ka taimekeni bera ne ya haumin jiki, ta kankameshi sosai, auzubillahi minal shaidanir rajim ya fadi ya hankadata lokaci guda duk da taso yaudararshi da laushin jikinta da yaji a jikinshi, mari yakai mata zafafa guda biyu, yace wallahi ko ki fita ko in fasa kanki da bindiga, ta mike jikinta na rawa ta fita tana kuka, dafa kanshi yayi yana maida numfashi saboda gaba daya ta hargitsa mishi kwakwalwa, saida yayi minti biyar yana addua sannan ya mike ya shiga bayi yana hamdala ga Allah da ya haneshi aikata alfasha, Ajiyar zuciya yayi da ya gama tuno wannan ranar sannan yayi tsaki ya shiga bayi yayi wanka... Mrs tijjani shattima.... [[ ◆◆ ZULFAH ◆◆ 3⃣3⃣ By Aysha Ya'u kurah A mota hira suka dinga yi da farouk da shima jiya ya dawo gida, kallon mamaki ya dinga yi mata yadda ta zama wayayya, kyanta mai sanyi, fatarta ta murje kamar wacce tayi wankan inji, ga uniform din jikinta ya karbeta sosai, shi dai da a hanya ya ga zulfa bazai ganeta ba, ya kalleta sosai yace wai kece kuwa, kinga yadda kika koma, anya kina karatu a school kuwa, tace kai yaya farouk tsokanata kawai kakeyi amma in banda haka ji fa yadda na rame saboda tunanin su mummy, yace umm I c, amma mu baki tunanin mu ko, ni tunda na tafi skool ma bamu taba waya ba, anya kuwa zan cigaba da matar dake, tayi dariya sosai tace kayi hakuri nima fa ina skool, yace bawani nan, anty laila ta gama kwaceni kuma babu kishiya, ta harareshi cikin wasa tace kai kama isa, yace har nayi yawa ma tunda kin manta dani, tace wallhy kuna raina dukkanku ya za'ayi in manta da na katakon, yayi dariya dai2 lokacin da suka karaso gida, gate aka bude musu suka shiga yayi parking dinta gurin ajiye motoci, ko kadan bata hango sadeeq cikin abokanshi su biyu tsaye a hanyar shiga parlon ba, ta bude motar ta fito farouk ma ya fito, twins ne suka fito da gudu da ihunsu sukayo gurinta ta yarda skull bag dinta itama da gudu ta rungumesu hular kanta ya fita saboda irin rikon da sukayi mata, gashinta ya zubo har gadon bayanta, wani irin shuku akayi mata a skull wanda yakara ma fuskarta kyau, rike hular tayi a hannunta ta rikosu tana musu magana zasu shiga parlor, da karfi farouk yace waye bawanki da zai dauko miki skull bag, ta juyo da murmushi a fuskarta zatayi magana suka hada ido da sadeeq, da sauri ta fada parlon ba tare da ta bawa farouk amsa ba, ya dauko skul bag din yana dariya ya bita dashi,, Ahmed ishaq yace woww marafah wannan ma kanwarka ce, sadeeq da duk ilahirin jikinshi a mace yake yace umm, hafiz yace gaskiya tayi min ina kamu, ahmed ya harareshi yayi tsaki yace marafa wallhy na rigashi hafiz dan iska ne, kai ma kasani, suka dinga musu sadeeq dae binsu kawai yakeyi da ido, dan shi kanshi zai iya cewa bai santa ba, yadai san itace zulfa'un da mummy ta aura mishi wacce bai taba mata kallon da yafi sau uku ba, cikin 1yr yarinyar nan ta zama haka, kodai ba ita bace,? wayarshi ta katse mishi tunanin da yakeyi, ya dauka da murmushi a fuskarshi yace my sweet baby, cikin shagwaba take magana, gaba daya ta rikitashi ya mance da wata zulfa da kamaninta, yace yanzu kika dawo kenan, tace walhy kuwa I mssd u so much, yace misd u more baby komai dare zanzo abuja kinji, tace haba dear yau saurah 4dys in zama taka gaba daya ka bari kawai sai gobe tunda gobe za'a fara event, yace oooh bakisan yadda na kosa bane amma babu komai Allah ya kaimu goben, tace dama kudi nakeso saboda kayan da zan mana na dinner, yace okk dear kamar nawa, tace 500k zai isa saboda harda shoes da komai, yace to no problem zan turo miki yanzu, take care fa, tace I will sai na ga kudin, suka ajiye wayar, ta kalli wani fakirin saurayin da ta hadu dashi ya biya mata bukata tace bari ya turo in baka ko 300k, cikin murna yace duk ni kadai, tace kwarai kuwa ay ka biya min bukata ta, kuma kai cikakken namiji ne, zan yi maka fiye da haka ma indai zaka dinga amsa bukatata, cikin rawar murya yace me zai hana, ay mun zama daya ma daga kin ji kina bukata kirani zaki ganni ba bata lokaci, tayi murmushin jin dadi, ta shafi sajenshi ta manna mishi kiss ya tayata suka kara fadawa cikin sabon Allah, wa iyazubillah... Biki ne akeyinshi na masu naira, anyi events kala2, mummy ko mutum daya bata gayyata ba, haka ta hana su anty laila da jalila zuwa bikin, daurin aure kadai ta yarjema farouk da nurain zuwa shima dan tare da daddy ne, haka tace sai dai daddy ya ba sadeeq wani gurin su zauna amma sanah bazata zauna a cikin gidan da take ba, gayyar anty amarya ta cika gidan, da gidan amarya dake unguwar rimi, zulfa abin ya dameta ba sosai can ba, saboda yanzu a shirye take in sadeeq yaga zai rabu da ita bismillah in zai zauna da ita duk daya a gurinta, sonshi yayi mugun raguwa a zuciyarta, Karfe 9 aka kawo amarya gidan surukanta, rikakkun yan bariki ne kawayen mamanta suka kawota, zama sukayi a parlon mummy wai ga amarya nan ayi mata fada, mummy tace ay nasan anyi mata fada agida saidai ince Allah ya basu zaman hakuri, ameen sukace matan gurin suka tashi suka kaita dakin anty amarya anan suka dade sannan aka kai amarya gidanta, gidan su daddy yan kai amarya suka dawo nan zasu kwana, saida yar maiduguri ta kara gyare sanah kafin ta tafi, 10 : 30 abokan ango suka rako ango siyan baki, saida ko wanne a cikinsu ya bata 10k sannan ta bude musu kyakykyawar shaidaniyar fuskarta, Hafeez da bai halarci event ko daya ba sai daurin aure saboda aiki, ya kwalalo ido yana kallonta, tabbas itace yarinyar da suka hadu a govnr road..... Mrs tijjani shattima.. [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 3⃣2⃣ By Aysha Ya'u Kurah Haka kuwa akayi cikin satin daddy yaje aka gama maganar aure aka sa rana, wata biyu akasa saida mahaifin sanah ma yace yayi kusa, dakyar daddy ya nusar dashi akan wata biyun shine dai2 saboda babu alkhairi ajan lokacin aure indai duka bangaren a shirye suke.. Sai dare daddy ya isa gida, sai da ya huta sannan ya sanar ma da mummy, babu abinda tace mishi amma a zuciyarta ta nemawa danta tsari daga sharrinta da kuma cututtukan nan na zamani, addua ta dingayi a zuciyarta saboda bacin rai cikin ikon Allah zuciyarta tayi wasai suka cigaba da hira da mijinta cikin nishadi, lokacin da daddy ya fadawa sadeeq murna ya dinga yi ya dinga kiran abokanshi yana fada musu, ya kirah hilal da rabon da suyi waya tun randa suka rabu a hotel, hilal kamar bazai daga wayar ba, sai kuma ya daga, sadeeq yace hilal kenan sarkin fushi, har ka gama fushin, hilal yace hmm kawai, sadeeq yace kai ba wannan ba, an sa min rana on 12 oct, saboda haka ya kamata kazo mu fara shirye2 tunda kasan kaine babban aboki, hilal Allah sanya alkhairi kawai yace ya kashe wayar dan baijin zai iya zuwa gurin marafa, saboda iya tozarci marafa yayi mishi, ,, sadeeq ya kalli wayar yayi tsaki, a ranshi yace hilal bakin ciki kawai yake mishi dan shi bai samu sanah ba, saidai ka mutu hilal ya fadi hade ajiye wayar ya mike dan shi a ganin shi he's very lucky to hv sanah,,, Biki ya rage saura sati biyu, mummy babu abinda ta shirya na biki, haka nurain dan kwata2 ya daina kallon inda sadeeq yake tsakaninsu gaisuwa, anty amaryace ke kidin ta tayi rawarta ita da sadeeq, ba kananan kudi take karba a gurin sadeeq da daddy ba duk a sunan shirye2, sanah kuwa watanta daya a maiduguri tana gyaran jiki da shan magunguna, gaba daya a matse take dan bata iya yini ba tare da namiji ba, takunkumi aka samata a gidan wata kawar mamanta dake maiduguri, nan ake mata gyara ciki da waje, an hanata fita ko nan da can acewarsu daraja suke nema mata agurin mijinta, gyaran da akayi ma sanah ko budurwa albarka, gyara ne na musamman wanda ake ajiye kudi sosai kafin ayi shi, (anya akwai gyaran da zai ďinke leda ta koma yadda take kuwa, mata mu kula sosai a daina yaudararmu da mace na komawa virgin ta hanyar dinki ko magani, virginity kamar leda yake in ya huje babu wanda ya isa ya iya maidashi dai2, saidai ya matse a sha wahala, to bari muga sakaran namiji irin sadeeq zai gane pacin da akayiwa leda, ko kuwa wannan karan ma son zai rufe mishi ido).. Tsaye take tana duba agogon hannunta, duk wanda ya ganta yaga budurwa cikakka mai cikar zati da kamala, rolex da frisky duk anzo an daukesu ita kadai ta rage, kyakykyawar fuskar nan tata da koda yaushe cikin smiling take amma saboda kosawa azo daukarta ta hade ta kamar bata taba dariya ba, Smiling beauty taji an fadi a bayanta, ta waiga suka hada ido da uncle majeed, tayi murmushin da ya lotsa kumatunta ya bayyanar da kyaunta mai sanyi, yace har yanzu baki tafi ba, tace eh inajin suna hanya ne, ya karbi papers din hannunta yace wane subject kukayi last, tayi dariya tace can't recall saboda bana maida hankali akan subject din, yayi dariya sosai yace magana fa kika fada min, tace a'a gaskiya dai, dan kasan my fav subject ne shiyasa kake tambayata, yace ni bansani ba, tunda in kuna cafe bacci kikeyi, ta bude baki sosai tana kallonshi, yace banason jin komai dan ba karya na fada ba, wish u d very best in ur exams, wa yaga smiling beauty a ss3 next term, ta rufe fuskarta tana dariyar jindadi, ya duba agogon hannunshi, yace muje in kaiki gida, zatayi magana akayi parking din mota a gabansu,, farouk ta hango ciki ta fara murna tace gashi nan ma anxo daukata tnx 4d concern sir, anytime yace mata yana daga mata hannu, har saida ta shiga mota sannan ya juya ya koma office, tunanin zulfa'u yana hanama Abdulmajeed sukuni, hakuri kawai yakeyi saboda soyayya is outta bound a school din da babu abinda zai hanashi fada mata, yana shiga office ya tsura ma hoton da yayi mata ranar presentation ido, wani irin sonta yakeji yana ratsa ko ina jikinshi, computer da take amfani dashi a cafe nan ya hau ya zauna yanata bincika shirmen da takeyi a ciki yana dariya,,, Mrs tijjani shattima.... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ●● 3⃣4⃣ By Aysha Ya'u Kurah Gaban sanah ya fadi da ta hada ido da hafiz tayi maza ta sunkuyar da kanta kirjinta na tsananta da bugawa, ita yanzu ya zatayi in hafiz ya tona mata asiri, wannan karan tasan bata da mafita,, zufa sai keto mata takeyi ta ko ina, muryar hafiz ce ta dawo a ita cikin duniyar rudun da ta shiga, Yace gaskiya am happy 4 u marafa, Allah ya baku zaman hakuri, ameen sadeeq ya ke ta cema abokanshi yana musu godiya babu kakkautawa, hafiz a zuciyarshi yana mai tausaya mishi dan ya auri taxi no garage, abin da ya hanashi yi ma marafa maganarta a tunaninshi ta nutsu ne ta daina abinda takeyi kuma baya son silar raba auren sunnah shiyasa kawai ya bar abun a zuciyarshi, har suka fito sadeeq na musu godiya, hafiz yace marafa wai ina hilal, sadeeq ya tabe baki yace inaga yayi tafiya ne bari in shiga kar amarya ta gaji da jira, sukayi dariya dukkansu suka wuce hafiz na tunanin yadda akayi sadeeq ya auri wannan karyar, to wai hilal bai taba ganinta bane dan da ya ganta zai ganeta kuma ya fada ma sadeeq wacece ita, tunda sun hadu a tavern hotel da hilal ranar da ya fara ganin sanah, daga kafadunshi yayi, yayi musu fatan alkhairi a zuciyarshi sannan yaja mota ya wuce... Sadeeq ya shigo ciki cikin farin ciki ya kullo ko ina, kitchen ya shiga ya dauko plate da cup ya wuce daki, yana shiga ya tarar da sanah tayi rupp da ciki tana kuka, ya maza ya ajiye abinda ke hannunshi ya karasa kusa da ita yace lafiya me aka miki baby, ta kwanto jikinshi tayi ajiyar zuciya dan taga alamar hafiz bai fada mishi komai ba, tace nayi missn gida ne, ya rungumeta sosai yana shakar kamshin jikinta yace tink no more baby, zan maye miki gurbin komai a rayuwarki ki daina kuka ki sakko muci abinci, ya dauketa chak ya sauko da ita ya zauna yana bata kaza da nagari milk, saida suka koshi sannan yace ta tashi suyi wanka suyi sallah su gode ma, langwabewa tayi tace na gaji dear ka bari sai gobe muyi sallar plss, yace gobe kuma, tace eh sai mu hada ba isha'i kake nufi ba, yace isha'i kuma, u mean bakiyi sallar isha ba, tace eh har magrib ma saboda kar makeup dina ya goge dama nayi niyyar in zan kwanta inyi kuma gashi am tired saidai gobe in hada, sadeeq ya kallata cikin mamaki, ya fara magana cikin sanyin murya dan baya son ya bata mata rai yace baby yi hakuri muje in taimaka miki kiyi wanka kiyi alwala kizo kiyi sallah, ta bata rai sosai zatayi magana ya dauketa yayi bayi da ita, saida ya taimaka mata tayi wanka sannan yace tayi alwala, gefe ya koma ya tsaya yana kallonta tana alwalar da ita kanta akwai gyara a cikinta, kallonta kawai yakeyi dan ko ina a jikinta a sake yake, a tunaninshi new bride sunada kunya in an taba su amma wannan itace ma ke sarrafa shi, duk inda yasa hannunshi ita ke kara matseshi yadda zataji dadi, kauda tunani yayi a zuciyarshi, ya kalleta yace kin gama, tace eh, ya rikota suka fito, saida tayi sallar magriba da isha'i sannan ya mike sukayi raka'a biyu dakyar tana korafin ta gaji, zama sukayi yana mata tambayoyi akan wankan janaba, ko daya bata iya amsawa ba , dataga yana kokarin kureta ta mike ta cire hijab din jikinta ta fado jikinshi tana mishi magana kasa2, a kasalance yake zai fara magana ta tura bakinta cikin nashi, nan ta shiga gigita shi da salonta, da kyar ya iya dagata ya daurata akan gado ya shiga aika mata da nashi salon shima, sun dade suna cuda juna, sadeeq yasha bakar wuya a gurin sanah, ya kasa tantance dadin saboda wahalar tayi yawa, gashi taki rabuwa dashi har saida yayi ta maza ya mike yayi bayi yana maida numfashi wankan tsarki yayi zuciyarshi cunkushe da bakin ciki, amma duk wannan bakin cikin da yakeji baisa yaji son sanah ya ragu a zuciyarshi ba, ko kadan wannan daren baiyi ma sadeeq dadi ba, ya kasa gane me yasanya shi cikin tsananin kunci a daren dayake mafarkinshi dare da rana, tsaki yaja ya fito yaga sanah na baccinta babu abinda ya dameta, kauda kanshi yayi ya fita daga dakin gaba daya, kwanciya yayi a kan gado yanata juyi, ya rasa abinda zaisa shi farin ciki a wannan daren, dakyar bacci yayi gaba dashi cikin mafarkai kala2,, Da asuba ya tashi yayi sallah, dakin sanah ya nufa ya tarar da ita tana bacci kafarta a dage komai nata a waje, baccinta takeyi babu abinda ya dameta, tsaki yayi sosai ya shiga tashinta daga wawan baccin da takeyi, juyi tayi sosai tace oh my God pls kabarni inyi bacci, jiya fa ban wani samu baccin kirki ba, girgiza kanshi yayi hade jan tsaki ya fita ya bar dakin, parlor ya koma ya zauna ya runtse idonshi, ya tsani ya tuno daren jiya, bude idonshi yayi da sauri ya kunna TV yana kallo, karfe tara dai2 aka kawo musu kari daga gurin anty amarya har lokacin sanah bata tashi ba tana can tana baccin asara, kitchen ya shiga yayi serving kanshi ya hada tea ya fito ya zauna ya karya, Sai karfe sha biyu a da wani abu sanah ta tashi tana mika,, bayi ta shiga tayi wanka sannan tayi alwala, tana idar da sallah ta shiga caba kwalliya sosai cikin tsadadden leshi ruwan kasa, parlorn ta fito lokacin ya zaune cikin kananan kaya, kusa dashi taje ta zauna, yayi murmushi yace har kin tashi, tayi fari da ido tace ehh dear yunwa nakeji, yace akwai abinci a kitchen kije ki zubo, ta mike tana kwarkwasa ta karasa kitchen, tea kadai ta hada sai farfesu kadan da ta diba ta dawo ta zauna tanaci suna hira, Duk ranar sadeeq yana gida sallah kadai ke fitar dashi masallaci, Kwanaki bakwai sukayi suna gurzar juna ko kuma ince sanah na gurzar sadeeq saboda bata daga kafa ko da yaushe cikin bukata take har tsoro yakeji ta nuna bukatarta saboda baya iyama yawan bukatunta kuma ya rasa abinda take likewa wanda yake sashi jin azabar zafi in ya kusance ta, gashi ko dakin da take kwana ma ba gyara shi takeyi ba saboda a gida babu abinda takeyi daga ci sai yawo,, uzuri sadeeq yayi wa sanah ko zata gyara komai nan gaba saboda yana sonta amma badan haka ba Allah ya sani da tuni ya rabu da ita tun day 1 na aurensu.... hmmmmmmmmmmmmmmmmmmmmmmm Mrs tijjani shattima... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: . ◆◆ ZULFAH ◆◆ 3⃣5⃣ By Aysha Ya'u Kurah Smiley** smiley** smiley** sau uku kawayenta na kwala mata kira, tayi tsaki ta diro a gado ta deko ta kallesu tsaye a bakin cornersu, takalli Rukaiya salis (Neelam) dake gyara agogon hannunta tace meye kuke min irin wannan kiran, neelam tace uncle majeed yace a kiraki mu fito rehearsal tun dazu juniors ke tsaye a field mu kadai a ke jira, ta turo baki ta mike tace ni wallhy matchn dinnan ya fitan min arai, kullum babu hutu, frisky dake saman bng tana shan cornflakes tace ay ke kin fita sahun matchers queen naji ance za"a nadaki, zulfah ta kwalolo ido tace wace din za'a sa queen, Huris tace ke mana, kuyi sauri pls dan mrs ebalu tana field din kuma muna kara bata lokaci, zulfah ta zauna tace aiko kuce banida lafiya ina ni ina queen, yaushe ma zan iya yadda suke tafiya gaskiya kuje wallhy ban iyawa, ta shige bargo ta dukunkune, huris tace wallhy bazamuyi karya ba cewa zamuyi kince baki zuwa kuzo mu tafi, zulfah ta mike da sauri ta suri takalmanta tabi bayansu tana ma huris masifa, har suka kai field bakinta baiyi shuri ba sai masifa takeyi, huris tace yoo ay sai kiyi, na matsa miki ki fito ne ki koma ki kwanta jiki magayi, zulfah taja tsaki dai2 lokacin suka karaso kusa da teachers din, dukawa sukayi suka gaishesu, mrs ebalu ta dafa zulfah cikin harshen turanci tace wannan kake magana ko majeed, yace yes ma sai a samu princess nd prince, zulfah ta bata rai ta koma baya tabarsu sunata muhawara, aka ciro wasu kyawawan yara "mardiyah ishiyaku" da "Habeeb lamido Habeeb" sune p nd p, gefe guda suka zauna da zulfah da ko dariya takiyi tana kallon su huris suna matching suna mata dariya, saida aka gama da matchers sannan aka fara koya musu yadda zasuyi tafiya da kuma imettn din yadda zasu gaisa da baki da kuma gift din da zasu bawa principal, zulfah dukk yadda taso ta bata tafiyarta dan acireta abin ya gagara saboda duk yadda tayi sai tafiyar tayi mata kyau sosai, yaran ma sun iya sosai dan haka aka tsayar da sune zasuyi babu canji, cikin satin suka kware sosai daga su har matchers din komai suna yinshi gwanin ban sha'awa tun zulfah bata so har ta hakura ta maida hankali, ana gobe inter house sport suna final rehearsal uncle majid ya shigo da wasu kayan queen da na yaran, gown ce kalan hostel din purple me kyan gaske, sai takalmi silver mai tsini sosai da crown, sai wani abu da zasuyi crossing dinshi tsakanin kirjinsu an rubuta sunan hostel din da sunan queen, sai na yaron suit ne baki mai kyau dai2 shi itama yarinyar gown ce mai kyau fara da karamin crown, suna gama rehearsal kowa ya dauki kayan shi zai wuce hostel, kiran sunanta uncle majeed yayi lokacin da zata fita, ta juyo ta amsa mishi, ta karaso gurinshi tace gani sir, ya kalleta sosai yace zaki iya kuwa, tayi murmushi tace in shaa Allah uncle, yace sai kin daure kar kiga yawan mutane kisa muyi failn kinji, ki saki jikinki kiyi duk abinda ya dace, tace I wll in shaa Allah, yace good jeki Allah ya bamu sa'a, tace ameen sannan tasa kai ta fita. . . Shiri sukeyi tun safe, jalila ta gama shiryawa tana tsaye kofar anty laila dake shirya ayda da tsohon cikinta, jalila tace anty zaki iya xuwa kuwa, laila ta cije baki tace nima haka nake gani ku tafi kawai dan banjin dadi, jalila tace sannu Allah ya baki lafiya ta kamo hannun ayda suka fito parlor nan suka tadda mummy da kayayyaki a gabanta jalila tace mummy anty batajin dadi mu kadai zamu tafi ina su amrah, mummy tace sun fita duba drivr, kafin tayi magana sai gasu sun shigo da gudu suka ce mummy wai anty amarya ta aikeshi, mummy tayi tsaki tace to ku jirashi ya dawo, jalila ta turo baki tace ni wallhy mummy bazan iya jira ba waya san lokacin dawowarshi, mummy tace to ya kikeso inyi, kece ki koyi mota tuntuni kinki sai kisan yadda zakiyi ki tafi, zatayi magana aka turo kofar, sadeeq ne ya shigo cikin white suit masu kyau sun amshi jikinshi sosai ya tsuguna har kasa ya gaida mummy, ta amsa tana kallonshi cikin tausayawa dan duk ya rame, watanshi shidda kenan da aure tun suna wata daya dakin laila yake zuwa cin abincin rana da na dare wata rana har na safe ma, dan sanah bata bin hanyar da kitchen yake saidai ta fita restaurant taci ko tayi takeaway, ga yawon tsiya in ya tambayeta tace mishi tana gidan aneesah, ga bukatunta kullun kara yawa sukeyi, Mummy ta kalleshi cikin kulawa dan ta fara amsa gaisuwarshi kuma tana kulashi saboda ta jawo shi a jiki har ya fita daga jarabtar wannan kaddararen aure, tace daga ina kake, yace daga gida mummy, sanah tace in gaisheki, ta tabe baki dan tasan karya yakeyi tace to naji, jalila tace yaya plss kazo ka kaimu danbo babu wanda zai kaimu, mummy ta kureshi da ido taji mai zaice, ya saci kallonta sannan ya mike yace to muje, suka kwaso kaya cikin murna suka fito suna ma mummy bye2, mummy tace Allah ya tsare a dawo lafiya ta koma sama tana mai tausaya ma sadeeq duk da shi ya jama kanshi kuma abin takaicin shine har yanxu baya ganin laifin sanah,, tayi tsaki ta sa hijab ta tada kabbarar sallar walha... Mrs tijjani shattima.. [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 3⃣6⃣ By Aysha Ya'u Kurah Wow Wow Wow abinda yan hostel dinsu keta fadi kenan tunda ta gama shiryawa,, linda okoro tace smiling beauty u luk take awy, rolex tace kamar queen din gaske danyi tafiya muga, ta fara takawa a hankali anata ihu da tafi a hostel din, gashin kanta ya kwanto a bayanta yaji gyara da ribbons da wasu kyalkyali wanda aka watsasu a flowrs,, sai qamshi takeyi gashi makeup din da akayi mata babu wani hayaniya, tun 8:30 suka fito, Rolex da Abdulhi su suke rike da bannr, sai wata yarinya dake ma queen fiffita a bayanta prince nd princess na watsa flowers a duk inda queen zata taka, suna zaune dukkansu queens din, suma sauran sunyi kyau amma basu kamo kafar zulfa'u adam ba, sai kuma Wasila kamba da itama tayi sosai.. Tsaki yayi da yaji ringing din wayar jalila a motar shi dan ya saukesu in sun gama zai dawo ya maida su gida, juya kan motarshi yayi dan har ya wuce katsina rd, yana shigowa makarantar yayi hanyar field can gaba dab da su principal ya hango jalila tsaye kusa da uncle majeed, tsaki yayi yace shegen rawan kan tsiya, ya dinga kutsawa saboda cikowar mutane sam idonshi bai gane mishi masu matching ba, ya kusa da jalila yaji wasu maza tsaye hankalinsu na kan abinda akeyi dayan yace wayyo cizo mubarak kaga wata andar oh my God mubarak yace kaidai bari jamal tun kafin azo kansu nake kallonta wallhy ban taba ganin kyakykyawar mace kamarta ba, daga kanshi yayi yana son kwalawa jalila kira yaga sun kara matsawa gaba tana daga hannunta tana murmushi, daga kan da yayi idonshi yayi arba da kyakykyawar halitta, ganin abin yakeyi kamar gizo, murmushin dake kan fuskarta shi ya kara mata nuri, tafiya takeyi kamar batason taka kasa yaran na watsa mata flowers dai2 gurin principal ta tsaya idonta ya sauka akan jalila da uncle majeed, murmushi tayi musu mai kashe zuciya sannan ta fara taka step din table din, kidin band na tashi ko ina matchers na yin style din da aka koya musu mai ban sha'awa, ihu kawai kakeji lokacin da zulfah ta gaida principal da mutanen dake kewaye da ita sannan ta dauki flowern dake tray ta rataya mata a wuya ta mika mata hannu suka gaisa ta dan rungumeta, snow spray wani yaro dake tsaye bayanta a matsayin bodyguard ya fara fesawa, zulfah ta juyo tana murmushi zata fara sakkowa har lokacin yana biye da ita da spray din, juyowarta yayi dai2 da karasowar sadeeq gurin shima ita yake kallo ta kasa dauke idonta cikin nashi, gaba daya gabobin jikin sadeeq sun tsaya chakk basa aiki, wani abu yaji yana tsarga mishi a jinin jikinshi, dauke idonta tayi da sauri jikinta na rawa ta fara sakkowa a hankali takalmin kafarta ya gurde ta tafi da baya zata fadi ta runtse idonta hade da yar kara saboda ta sadakar zata fadi kasa kuma tabbas zata ji ciwo, jinta tayi jikin mutum ya riketa sosai, ta bude idonta a hankali tana kallonshi, uncle majid yayi ma bodyguard alamar ya cigaba da fesa spray din saboda kar suyi failn dan abin ya bada wani style na daban, da sauri ya cigaba yaran suka shiga watsa flowers, kida hade da ihu na tashi sosai, dagota yayi hannunshi na cikin nata har lokcin yana kallonta, Da kyar ta saita kanta ta cire hannunta ta koma ciki jikinta na rawa suka cigaba da matching har suka wuce idonshi bai daina kallonta ba, dafashi jalila tayi tace yaya abba baka wuce ba, yayi tsaki ya harareta ya kalli jakarta da ya yar a kasa lokacin da zai taimaki zulfah yace dauki jakarki, abinda ya kawoni kenan, ya juya ya wuce dan kar jalila ta fahimci halin da yake ciki,,, zama yayi a mota zuciyarshi cike tambayoyi, lumshe idonshi yayi ya dinga tuno abin da ya faru, oh my Goshh ya fadi hade da kifa kanshi, addua yakeyi akan Allah kar yasa sonta ne zai kamashi farat daya, wani irin abu yaji yana taso mishi yana nukurkusarshi, wayyo ya fadi yana girgiza kanshi, dole in yi nesa da duk abin da zai kara hadani da yarinyar nan, meyasa ma ya riketa da ya barta ta fadi abinda zuciyarshi keta kitsa mishi kenan, tada motarshi yayi ya tafi da niyyar bazai dawo ba dan baisan kara haduwa da ita, me yake shirin faruwa dashi, in ya tuna shock din da yaji sanda ya riketa sai ya runtse idonshi ya rage gudun motarshi, ya rike mata kala2 ya taba su sosai amma bai taba jin abinda yaji a gurin yarinyar nan ba, ko sanah da yake mutuwar so bai jin wannan abun akanta, gida ya wuce direct dan ya samu relief... Anya kuwa sadeeq hmmm.. mudai je zuwa... Mrs tijjani shattima... [15/12 14:47] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 3⃣7⃣ By Aysha Ya'u Kurah Yana isa gida ya tarar da mata cike da gidan anata ciye2 ko ina a hargitse, basusan ya shigo ba hirarsu sukeyi kuma duk akan samari, Beebah da tazo ma sanah hutu daga abuja tana kwance daga ita sai daurin kirji sai musu sukeyi suna mikewa suna girgiza jiki, dogon tsaki yaja ya wuce daki cike da kyamar halin sanah, nan ya tarar da wani bacin ran,, dan kuwa shiga yayi da niyyar ya watsa ruwa ya kwanta ko zaiji sanyi a ranshi ya tarar da dakin kaca2 anci abinci saman gadon plate din indomien ma na can gadon da gwangawanin kan juice, ranshi ya baci matuka ya fito parlorn yana kwalawa sanah kira, ta mike tana yatsina fuska ta karaso inda yake tace lafiya, ya harareta ya riko hannunta yana janta da karfi har suka kai dakin, yace uban waye yace ki shigo min daki ki batamin, ke kike gyara min daki? Ki bata naki ki bata nawa saboda ke kazama ce mara hankali , kallon mamaki ta tsaya tana ma sadeeq, tace iyyye kai har kanada karfin gwiwar yi mani masifa, kai har ka isa dan na shigo dakinka kace zaka daga min murya, ta nuna shi da yatsa tace wallhy ka maida hank--- mahaukatan mari ya kai mata a duka kuncinta zuciyarshi na tafarfasa da halin sanah, gashi duk abinda take mishi ya kasa daukan mataki akanta, kuka sosai ta fashe dashi tace ni ka mara, wallhy ka mari aurenka mugu kawai, ta fita tana kuka duk ta cika gidan da hayagaga, kawayenta suka taso suka rungumeta suna rarrashinta ta wuce dakinta ta dauko keyn mota tasa jallabiyya suka fita daga gidan ita da kawayenta, zama sadeeq yayi a kasa ya rasa me ke mishi dadi, idonshi nan da nan ya kada yayi jawur saboda damuwa, tunanin zulfah shi ya toshe duk wani lungu da sako na zuciyarshi, gani yakeyi ma kamar duk shakar numfashin da yakeyi hade suke tahowa da tunaninta, ya Allah karka horeni da abinda bazan iya ba akan laifuffuka na, tashi yayi ya shiga wanka ko zaiji sanyi a zuciyarshi da yakejin kamar dutse mai nauyi ne a cikinta yana fitowa ya kwanta yanata juyi da kyar ya samu baccin damuwa yayi gaba dashi.... Gurin alpha Demola suka nufa kowa na fadin albarkacin bakinshi akan abinda sadeeq yayi mata, suna shiga sanah ta fashe mishi da kuka, yace oooo me ya faru kuma sanah, ta rushe da wani kukan tace aiki ya baci alpha yau sadeeq har marina yayi yanata zagina, saida yayi min dukan tsiya ka taimakeni a daura wani aikin kan wancan dan banaso in rasa sadeeq plss alpha, demola ya kalleta yace aah bari muyi istahara inaga akwai wani da yake bata mana aikin da munayi, ya fara" "incantion" cikin yaren yarbanci yanayi yana kiran sadeeq, can ya gama, ya kalli sanah yace tashi kije wani gurin xai nemeki a gigice duk inda kike, ay sadeeq naki ne babu wata mace da zaiso bayan ke tashi kije, ta ajiye mishi damin kudi ta mike ta fita cikin jindadi dan tun aurenta da sadeeq take harka dashi bata taba samun failure ba, shurun da sadeeq yayi ya kasa mata magana akan daren farkonsu da yadda take juyashi da yadda yake tsoronta ma wannan duk aikin demola ne, ko anty amarya bata san tana zuwa gurinshi ba dan wata kawartace ta bata shawarar yanzu mata basa zama haka duk son da namiji yake maka wata rana sai ya juya maka baya bare ita da bata kai virginity dinta gidan aure ba dole ta mike tsaye,, wannan dalilin yasa ta fara zuwa gurin demola dan bata son rabuwa da sadeeq ko a mafarki bare a zahiri, ta ja motarta suka wuce sheke ayarsu ita da kawayenta, Firgigit sadeeq ya mike daga gajeren baccin da ya daukeshi, abin da ya faru tsakaninshi da sanah ya shiga dawo mishi, ya mike a firgice yace ya salam, meyasa na mareta meyasa ban taushi zuciyata ba,,, to yanzu in zan fara bi in nemota, wayarshi ya dauko ya shiga kiranta, ya kirata yafi a kirga tana kallon wayar amma taki dauka sai dai su sheke da dariya ita da kawayenta, kamar zaiyi kuka ya mike gaba daya ya manta da tunanin zulfah da abinda ya faru tsakaninsu dazu,, waje ya fita ya shiga motarshi ji yayi duk duniyar ma zafi take mishi saboda sanah bata kusa dashi, gidan aneesah ya fara zuwa tace bata zo ba,, yaje duk gidan da yasan tana zuwa amma bata can, dafe kanshi yayi da ya karaso kofar gidansu ya rasa me yake mishi dadi, kuka kawai yakeson yi dan shine toshe a makogoronshi, yanayin da ya tsinci kanshi dazu yake son tunowa amma kamar an shafe abin a kwakwalwarshi, saida ya kusan minti biyar sannan ya shiga cikin gida, jalila ya tarar a parlor tana zaune, tace yaya shine kaki dawowa sai kiranka nakeyi baka dauka ba,, kanshi ya sara mishi sosai yace ina zan dawo, tace au ka ma manta ko, shikenan ta cigaba da latsa wayarta, sama ya wuce dakin mummy, saida ta gama abinda takeyi sannan ta kalleshi tace me yake damunka abba, ya dago jajayen idonshi ya kalleta yace wallhy bansani ba mummy, zuciyata na min zafi sosai dan Allah ki taimakeni, tace dame zan taimakeka? Idonshi ya ciko da kwalla yace nima bansani ba amma ina cikin wani hali dan Allah mummy ki taimakeni, ya fashe da kuka mai ban tausayi dan zuciyarshi kamar zata buga haka yakejinta, tayi ajiyar zuciya ta karanto adduoi a zuciyarta, zata fara mishi magana afrah ta shigo dakin tace yaya abba wai kazo inji anty amarya, anty sanah ma tana can naga tana kuka, wai kayi mata duk-- mummy ta buge bakinta tace wa ya tambayeki ko abinda aka aikoki ki fadi kenan, ta turo baki fita tana kuka, mummy ta kalli inda sadeeq yake taga wayam babu kowa, bata san tunda afrah tace sanah na dakin anty amarya ya fita ya nufi dakin, mikewa tayi ta sakko ta nufi dakin anty amarya, Mummy ta gigita sosai da taga sadeeq durkushe gaban sanah sai zazzaga mishi masifa sukeyi ita da anty amarya yana bada hakuri muryarshi har rawa takeyi, da sauri ta karasa ta daukeshi da mari, ta juya ta dauke sanah ma da mari sadeeq ya mike da sauri ya rike sanah dake kukan marin da mummy tayi mata, , ran mummy yariga yagama baci, tace saketa abba, saketa ka wuce muje, jikinshi na rawa cikin muryar kuka kamar wawa yace mummy kiyi hakuri kinga kuka takeyi kuma ke kika sata kuka kalli yadda fuskarta tayi jaaa, mummy tayi salati idonta ya ciko da kwalla tace shikenan abinda nake gudar maka abba ya faru, Allah ya isa tsakanina daku hadiza, bazan taba yafe muku ba da kuka mayar min da ďa mace, in shaa Allahu bazaku ga da kyau ba, anty amarya ta kalleta shekeke tace saidai in kece bazaki ga da kyau ba tunda babu abinda muka ma danki, so ne yakeyi ma sanah na tsakani da Allah ba komai ba kuma ke baki isa ki raba abinda Allah ya hada ba, saboda haka ki fita harkar yara indai baso kikeyi kiji kunya ba, sanah ta buge hannun sadeeq tace wallhy bazan koma gidanka ba kaje ka zauna da mahaifiyarka, cikin gigita sadeeq ya rikota yace ki rufa min asiri wallhy zan iya mutuwa in har kika rabu dani, zan iya rabuwa da kowa akanki sanah, ya tsuguna yana kuka kamar karamin yaro yana rokonta, mummy da kukanta ya tsananta ta fita dasauri tayi dakinta tana kukan halin da sadeeq ke ciki... Mrs tijjani shattima.... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 3⃣8⃣ By Aysha Ya'u Kurah Duk sunah zaune a dakin shuru in banda gunjin kukan mummy babu abinda ake ji, Nurain da hankalinshi yake a tashe tun shigowarshi, ya dafa gwiwowinta cikin damuwa, yace mummy dan Allah ki daina kukan nan haka, in shaa Allah komai zaiyi sauki, cikin kuka tace yaushe zaiyi sauki, abba ya riga ya fada tarkon su hadiza, sun rabani da dana, sun rabani dashi nurain, ta kara fashewa da kuka, anty laila tace dan Allah mummy kiyi hakuri duk tsanani yana tare da sauki, in shaa Allahu zai fita daga cikin halin da yake ciki mu dage da addu'a komai zaizo mana da sauki, Nurain yace hakane mummy mu dukufa kai kukanmu gurin Allah da yardarshi komai zai wuce, yanzu zanje insa ayita sauke alqurani da adduoi akanshi, dan Allah ki cire duk wata damuwa aranki kar wani ciwon ya kamaki mu dage da addua, nan suka dinga rarrashinta har hankalinta ya kwanta sannan suka barta ta dan huta,,,, Gosshhh!! gaskiya bantaba ganin cool guy kamar wannan ba, Hmm walhy Rolex baki kare mishi kallo bane saboda kuna matching ba karamin cizo na yayi ba frisky ke magana rike da towel a hannunta, zulfah ta amshi towel din ta daura tace humm kawai ta bude drawer ta dakko bath cse dinta, rolex tace smilley yayan nan naki ya zama topic of d town a skull dinnan, duk inda ka wuce maganar shi kawai akeyi, zulfah tace wai bazakuyi wankan bane ko in wuce ne in kun gama muhawarar kwa taho, rolex tayi dariya tace wato muhawara ma mukeyi ko, suka wuce suna ta mata magana duk akan sadeeq ita dai jinsu kawai takeyi, dan tun dazu take kokarin yakice abun da ya faru a zuciyarta ko kadan bata tuno shi bare ya dameta, suna gama wanka suka dawo suka shirya cikin nyt wear kowa ya kwanta gurin kwanciyarshi suna jefo ma juna hira kadan2 har bacci yayi gaba da rolex da frisky, zulfah taja bargon jikinta har kanta, tiryan2 abubuwan suka shiga dawo mata kamar lokacin suka faru, runtse idonta tayi tana kokarin kawar dasu amma abin ya faskara, bazata iya cewa ga yanayin da take ciki ba a wannan daren, ita dai abinda ta sani shine tunani yaki barinta ta samu hutu har bacci ya samu damar sace kwayar idonta, to wai meyasa take tunanin mutumin da ya tsaneta fiye da komai a rayuwarshi, meyasa zuciyarta zatayi rinjaye gurin tunanin wanda baya kaunar ganinta, tambayarta ta karshe wacce ta samo amsarta nan da nan itace meyasa sadeeq ya taimaketa,? zuciyarta tace abinda ko wane musulmi zaiyi kenan in yaga dan uwanshi musulmi zai cutu, kwarai haka ne sadeeq ya taimaketa daga faduwa a gurinne saboda zuciyar musulnci amma badan komai ba, kuma ko baizo gurin ba tasan Allah zai turo wani ya taimaketa, da wannan tunanin ta kauda duk wani abu a ranta har bacci yayi gaba da ita... Watan sadeeq biyu ko hanyar gidansu baya bi, duk da ba mazauni bane saboda aiki duk wkend yake samun hutu, ya tare a gurin sanah dake cin karanta babu babbaka, gani yakeyi duk duniya babu mai kaunarshi kamarta, duk wknd in ya dawo bata barinshi yaje ko ina har wayoyinshi kashesu takeyi saboda kar a damesu a cewarta, duk wasu abokan shedancinta sun san ta daina fitowa wknd saboda sadeeq na gida, hakan yayi ma sadeeq dadi ya dauka ta canza ne ta daina yawo, ga gidan ta samo wata mai aiki da take gyareshi, matsalarshi daya gurin abinci, sai dai yaje restaurant yaci, ranar wata friday ya dawo da ciwon kai mai zafi sosai, rungumeshi sanah tayi tana mishi sannu da zuwa, dishi2 yake ganin idonshi dan haka suka wuce daki, kwanciya yayi a kan gado ko zaiji saukin kan amma juyawa kawai yakeyi kamar ana burga wani abu a cikinshi, da kyar ya mike ya shiga wanka, yana gamawa bai iya yin komai ba saboda azaba ya kwanta cikin ikon Allah bacci yayi gaba dashi a cikin baccin sai ya dingajin kamar ana buga mishi wani abun a cikin kwakwarwarshi, Tashi yayi da sauri yana salati saboda mummunan mafarkin da yayi, wai ga mummy nan tana kuka jalila da nurain sun riketa suma suna kuka, gefensu kuma gawa ce ta mutum kwance dayan gefen kuma wata yarinyace da bai gane kamanninta ba itama kukan takeyi da yan sanda akanta, sosai mafarkin nan ya ruda sadeeq, ya mike yayi sallah sannan ya fito parlor nan ya tarar da sanah tana kallo ya zauna gefenta ta shige jikinshi tace my dear har ka tashi ya kanka, , yace umm na tashi ya dan rage ciwo, wani mummunan mafarki nayi baby , sanah tace ya salam wane irin mafarki nan ya kwashe duk mafarkin ya fada mata, tayi murmushi tace wani abu sai mafarki, ka kwantar da hankalinka kowa na gida na lafiya, anjima ma ka shirya muje ka gaishesu tunda ka dade bakaje ba, ya kalleta sosai yace are u crious, ta gyada mishi kanta tace yess ka kusa three mnth fa ay ya kamata muje ko, yayi murmushi yace hope dai ba takura kanki kikayi ba, kinsan bana son abinda zai matsa miki kin yarda muje,, tayi dariya cikin jindadi tace eh ai ni nace muje so ba wani matsala dear, ya mike yana jindadi dan yau sanah ta barshi ya ziyarci mahaifanshi da ko waya tace kar ya kara musu, kuma shi a ganinshi dai2 tayi saboda duk so ne ya jawo hakan... Mrs tijjani shattima.. [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 3⃣9⃣ By Aysha Ya'u Kurah Tunda ya karyo kwanan gidansu gabanshi ke faduwa, ya rasa dalilin wannan faduwar gaban da yakeji,. horn yayi masu gadi suka bude mishi kofa suna sara mishi, yayi parking suka fito shi da sanah, amrah da afrah suna wasa a tsakar gida suna ganinshi amrah ta taho da gudu ta rungumeshi tana kiran sunanshi, afrah tayi tsaki ta wuce ciki tana gunguni ita a dole bata sonshi yanzu saboda kullum mummy na kuka tana kiran sunanshi ko cikin dare inta farka fitsari sai taga mummy zaune tana kuka kuma duk shi yasata kukan, da sauri mummy ta fito jin sunan da amrah ta fadi, haka laila da jalila dake rike da babyn laila dan wata biyu suka fito dan suga ta inda abban zai shigo, afrah taje gurin mummy tace mummy kinga amrah taje ta rungume yaya abba harda mishi dariya bayan tasan kullum sai kinyi kuka akanshi, karki kara mata magana tunda bata jin haushin abinda ke saki kuka, mummy da idonta ya ciko da kwalla ta tsuguna zata ma afrah magana sadeeq ya murda kofar suka shigo, idon mummy kyar akanshi shima ya kasa dauke nashi akanta, gurinta ya nufa yana tafiya kamar wanda bashi da laka, har ya kusa kaiwa inda take sanah ta daka mishi tsawa, ya tsaya chak bai waigo ba kuma bai daina kallon inda mummy take ba, sanah tace ina zakaje, kazo kawuce muje ka gaida anty dee tukunna sai ka dawo ka gaidata, ko ka manta da marin rashin mutuncin da tayi min a gabanka, jalila da anty laila zuciyoyinsu cike da adduoi, mummy ta runtse idonta hawaye na binsu a zuciyarta tace Allah kaine mai karfin iko ka nuna ikonka anan gurin, ya Allah kai kace duk adduar uwa karbabiya ce akan danta Allah ka dawo da hankalin dana gurina ka fitar dashi daga jarabtar da yake ciki ya zuljalali wal ikram, cikin fushi afrah ta matsa kusa dashi ta jawo hannunshi tace yaya abba meyasa kullum kake sa mummy kuka ne, meyasa baka jin zafi a jikinka in mummy na kuka, meyasa zaka dinga hana mummy baccin dare, saboda kai mummy bata cin abinci sosai kullum sai tayi kuka, kaje ka rarrasheta ta daina kuka in haka ba babu ruwana da kai I will hate u to d coo in mummy bata daina kuka akanka ba, sanah tace iyyye lallai sadeeq tsayawa kayi, bakaji abinda nace maka ba ko, kuma ka tsaya kanajin rashin kunyar da wannan yar cikin taka take maka ka kasa tabuka komai, sadeeq da kirjinshi ke bugawa har lokacin yana kallon mummy na zubda hawaye, mummy ta kasa jurewa ta tashi ta shige daki tana kuka, jalila ma ta ruga daki tana kuka sosai kamar ranta zai fita, sanah taga sadeeq bai motsa ba ta karasa kusa dashi cikin fushi tasa hannu zata janyoshi, zulfah dake tsaye jikin kofah itama shigowarta kenan da uniform ajikinta kuma ta gama gani da jin duk abinda ya faru ta karaso da sauri ta shiga tsakani ta rike hannun, wani abu sadeeq yaji tun daga yatsun kafarshi har kanshi ya waigo da sauri yana kallonta, kallon cikin idonshi takeyi itama tana murmushi mai kyau ta juya rike gam da hannunshi ta fara tafiya, a hankali kafarshi ta fara dagawa yana binta kuma yana karewa duk ilahirin jinkinta kallo, duk masifar da sanah keyi baisa zulfah ta sakeshi ba duk da a tsorace take amma ta dake saida ta kai kofar dakin mummy sannan ta tsaya a hankali tana kallon cikin kwayar idonshi tace ka shiga ciki yaya abba, ka shiga gurin mahaifiyarka dan aljannarka tana karkashin kafarta, karka tuna da komai da kowa a lokacin da kake gabanta, ka bata duk wata kulawar da zai sata farin ci--- janyota yayi tafada kirjinshi ya juya baya da sauri glass din da sanah tazo bugawa zulfah ya sameshi a gefen hannunshi, kofar dakin ya bude ya turata da karfi sannan ya dauke sanah da mahaukatan mari, ihu ta saki ya dinga dukanta yana fadin maganganun da baisan daga inda suke fitowa ba, da gudu anty amarya ta fito saboda jin ihun tayi a cikin baccinta, cikin firgici tace kasheta zakayi abba na shiga uku, ta rikeshi itama ya turata ta fadi ya cigaba da dukan sanah dake kuka kamar mahaukaciya da kyar suka gudu daki suka datso ya tsaya yana buga kofar kamar zai ballata, ga jini na bin hannunshi shi kanshi ya rasa abinda ya harzukashi haka, can dakin mummy kuma mikewa tayi da taga zulfah ta rungumota tana kuka sosai, anty laila ta shigo tace mummy alhamdulillah Allah ya karbi adduarmu, in shaa Allahu komai yazo karshe da ikon Allah ta fada ma mummy duk yadda akayi ta cigaba da cewa kuma gashi can sai dukanta yakeyi, ta dafa zulfah tace Allah ya taimakemu bata sameki ba da mun shiga uku, mummy sujjada tayi tana godewa Allah tana tawassali da manzo Allah s.a.w.... Mrs tijjani shattima... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 4⃣0⃣ By Aysha Ya'u Kurah Zama sadeeq yayi a parlon yanaa kuka sosai, ya rasa me ke damunshi,, zuciyarshi sai zafi takeyi, kuka sosai yakeyi harda sheshsheka yaji an dafashi ya waiga ya kalleta itama kukan takeyi ya rungumeta yana kuka yace jalila me yake faruwa dani dnt kn waz wrng wv me, dan Allah ku taimakeni,, plss ki bawa mummy hakuri, cikin kuka tace mummy bata kullaceka ba yaya kazo muje ka bata hakuri, ya girgiza kanshi yace bazan iya haďa ido da ita ba jalila, tace karka ce haka yaya ka tashi muje mummy zata yafe maka, ya mike sukayi dakin mummy da kyar ya iya shiga kanshi na kasa ya karasa kusa da kafarta ya fashe da kuka, ta dagoshi tana hawayen farin ciki ta rungumeshi, cikin kuka yace ki yafemin mummy nayi kuskure dan Allah ki yafemin, tace na yafemaka abba, dama ban rikeka a raina ba kullum addua nake maka kuma gashi Allah ya amsa min adduata, ya dago yace nagode mummy dan Allah kicigaba da yi min addua, mummy tace ay wannan dolene abba addua babu fashi in shaa Allah, cikin dabara tayi mishi nasiha akan sakaci da addua da kuma son zuciya, dan duk su suka jawo mishi wannan matsalar, ta dade sosai tana mishi nasiha cikin hikima inda ya fahimci kurakurenshi sosai kuma yayi nadama akansu ba tun yau ba,, jalila taji dadi sosai yadda mummy tayi mishi taje ta hado mishi abinci ta zauna gabanshi yanaci suna hira amma sam hankalinshi baya gurin, zuciyarshi ta tafi can wani tunanin na daban, daga an taba kofa ko yaji takun tafiya zai dago da sauri ko zai kara ganin zulfah, saida ya gama cin abinci sannan suka fita chemist tare da jalila dake jin dadin dawowar yayanta cikin hayyacinshi ..... Sanah ce durkushe gaban anty amarya da ta zuba tagumi sai kuka takeyi, anty amarya taga bata da niyyar dakatawa ta daka mata tsawa cikin fushi tace wannan kukan ya isheni ki rufemin baki, duk laifinki ne sanah, nasan bai wuce shegen halinki na yawo da rashin tsaftace muhalli bane ya hada ku, ko kuma akwai wani babban laifin da kikayi mishi dan haka kawai sadeeq bazai miki irin wannan dukan ba,, sanah cikin kuka tace walhy babu abinda na mishi lafiya lau muka shigo gidan nan dashi wai dan kawai nace ke zai fara zuwa gaisarwa shine wannan shegiyar yarinyar taja hannunshi suka wuce dakin mummy ni kuma zuciya ta dibeni na zo buga mata glass ya kareta na sameshi shine yayi min irin wannan dukan wallhy anty sai sadeeq ya raina kanshi yanzun nan zan tafi gurin alpha, amarya cikin firgici tace wani alphan? Sanah tace alpha demola wata kawata ce ta hadani dashi ay badan taimakon da alpha yake min ba da tuni sadeeq ya sakeni ko kuma in zama kashi a gidanshi, duk abubuwan da kika ga yanayi duk aikin demola ne, (subhanallah, astagfirullh). Anty amarya ta zube a kasa tace ashe ke kika kashe kanki, yanzu ke baki iya kissa ba sanah, ashe wayewarki ta banza ce baki san yadda zaki magance alamuranki ba sai kin je gurin boka, wa ya fada miki aikin boka naci ya dade yanzu da kowa ya waye addua ta yawaita, lallai kin tafka babban kuskure, sanah ta riko hannunta tace anty to yanzu ya kike ganin zamuyi dan ni wallhy bazan iya rabuwa da sadeeq ba, anty amarya ta yi jugumm tana tunanin yadda zasuyi, can ta dago tace na gano mafita, zaki zauna a nan gidan kisan duk yadda zakiyi da kissa da dabara har mummy ta saki jiki dake sai ki roki gafararta, ni kuma zan dinga bi ta gurin daddy har sadeeq ya kara dawowa hannunki daga nan sai ki maidashi naki na dindindin, sanah tayi dariyar jindadi tace haka ne anty gaskiya naji dadi Allah barmin ke, nan suka gama kullenkullensu har dare yayi suna abu daya... Hmmmm. ... Mrs tijjani shattima.. [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 4⃣1⃣ By Aysha Ya'u Kurah Kwanaki kadan da wucewar wannan alamarin, su mummy suna cikin farin ciki sosai dan yanzu ya'yanta sun hada kansu, Nurain da sadeeq in suna gari suna tare ko da yaushe a dakin mummy suna hirah cikin jindadi, babu abinda yanzu yake damun sadeeq da ya wuce tunanin zulfah da ko kadan ta daina hada hanya dashi, kullum zai zauna saitin dakinsu ko kitchen ko zai ga fitowarta amma inaa dan sam taki yarda su kara haduwa tun ranar da abin ya faru, wani lokacin yakanji kamar ya tambayi jalila amma sai ya fasa dan karta dauka wani abun ne a ranshi game da zulfah, shi kuwa bawai sonta yakeyi ba a ganinshi kawai dai zuciyarshi na muradin ganinta ne, duk irin kokawar da gangar jikinshi keyi da zuciyarshi akan fitar da kara son ganinta abin yaci tura dan kamar daďa ingizata yakeyi, haka shi kadai zaita kewaye gidan ko zaiga inuwarta amma babu hali, wani lokaci ma in abin ya taso mishi sai yayita magana da zuciyarshi akan ni fa ba son yarinyar nan nakeyi ba to meyasa nakeson ganinta, in ya kasa samo ma kanshi amsa sai yayi tsaki ya runtse idonshi cikin jin zafin abinda zuciyarshi ke mishi. ... Suna zaune a kitchen suna aiki sai hira sukeyi suna dariya, sanah ta shigo da hijab a jikinta tana murmushi ta karasa ta gaida anty laila, ta kalleta ta amsa ba yabo ba fallasa, tace kawo in tayaki anty, laila tace no barshi kawai, ta cigaba da aikinta, jalila ta kama yan wake2 tana girgiza jiki sanah bataga fuska a gurinsu ba bare tace zata tayasu aiki, fita daga kitchen din tayi da sauri tazauna a parlor tana kuka, Nurain suka shigo tare da sadeeq, ganinsu yasa ta kara sauti a kukanta, sadeeq yayi tsaki ya wuce, nurain ya girgiza kanshi ya karasa kusa da ita yace lafiya me yafaru ta sauko ta durkusa a kasa tana kuka tace yaya nurain ku yafemin nasan zaiyi wuya ku yafe min, amma dan Allah ku sami koda karamin guri ne a zuciyarku ku yafe min, ka tayani ba su mummy da sadeeq hakuri wallhy nayi nadama bazan kara yin abinda nayi ba dan Allah, Nurain ya tausaya mata dan harga Allah ya dauka da gaske ta saduda tunda wata daya kenan tana zarya gurin mummy da sadeeq dasu jalila akan su yafe mata amma babu wanda yake kulata, ya kalleta a hankali yace ya isa haka biyoni , ta mike tana murmushin jindadi tamishi gwalo a baya suka wuce sama, gefe ta samu ta zauna tana kuka a hankali sadeeq ya mike zai fita nurain ya dakatar dashi yace dawo ka zauna abba, sadeeq ya koma ya zauna yana hararar gurin da sanah take, nurain ya kalli mummy yace mummy dan son annabi kiyi hakuri ki yafe ma sanah, ko Allah muna mishi laifi ya yafemana ya kamata muma mu xama masu yafiya, dukkan alamu sun nuna cewar sanah har cikin zuciyarta tayi nadama, irinsu lada mutum yake samu in har suka shiryu a sanadiyyarshi kayi hakuri abba ka yafe ma matarka ku koma ku gina rayuwa akan addinin islama, mummy tayi ajiyar zuciya zatayi magana wayarta tayi kara, dauka tayi da sallama daddy yace ku sameni a parlor Aisha, mummy tace to ta mike tace ku tashi muje anjima ma karasa maganar, suka fita dukansu,,, Daddy yace dafatan kin fahimceni ko Aisha, mummy ta gyada kanta tace hakane Allah ya yafe mana muma, anty amarya dake kukan munafurci tace nagode yaya da kika yafemana nasan kinada kyakykyawar zuciya nagode sosai yaya, mummy tace babu komai Allah ya zaunar damu lafiya, daddy ya kalli sadeeq dake cika yana batsewa yace abbana kayi hakuri ka dauki matarka ka bata dama ta karshe kaji, nasan abbana yana da hakuri kacigaba da hakuri Allah ya maka albarka, acan ciki yace ameen daddy, ya mike ba tare da ya kara cewa komai ba, daddy yayi dariya a zuciyarshi yace kamar ba shi ake fada dashi akanta ba, dama duk son da ba na Allah ba to tabbas sai an samu matsala, nan ya cigaba da yi musu nasiha har gurin goma na dare, ya kalli anty amarya yace kije kicema sanah ta fito su tafi, ta mike taje daki saida ta gama kitsa mata duk yadda zatayi ta kwantar da kanta har ta dawo da martabarta a gurin sadeeq sannan suka fito tana mata fada da karfi kamar da gaske, a waje suka ga sadeeq shida nurain shima fadan yake mishi sannan suka rankaya mota suka wuce... Mrs tijjani shattima.... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 4⃣2⃣ By Aysha Ya'u Kurah Kwance yake guraren 12am a dakinshi, rungume da pillow idonshi a lumshe yana sauraron wakar ''"manwa laage'' ta film din HNY, juyi kawai yakeyi yana hango surar zulfa a cikin kwayar idonshi, in ya bude idonshi kuma tunaninta ya addabeshi, yayi wurgi da pillon yayi tsaki a xuciyarshi yana masifar wannan balain dake neman zame mishi cuta, ji yakeyi kamar ya rufe ido ya ganshi a cikin gidansu ko zaiga ko da inuwarta ne, ya mike zaune ya dafe kanshi dan Allah ne kadai yasan yadda yakeji a zuciyarshi, can ya fara kokawa da zuciyarshi akan meyasa zai dinga tunaninta yarinyar da ko sec skull ma bata gama ba, yar kauye kwaila wacce bata waye ba, sai yaji kamar ya samu saukin abun sai kuma wani sashi na zuciyarshi ya sake bijiro mishi da tunani fiye da na baya, bude kofar dakin da akayi shi yasa shi dagowa ya kalleta, ďan karamin tsaki yayi ya kauda kanshi, ta karaso cikin dakin fuskarta dauke da mayaudarin murmushi ta zaune kusa dashi kamshin turarenta ya daki hancinshi, hannu tasa a kafadunshi tana daddanawa a hankali tace am sorry once again dear in shaa Allahu yanzu ne zamu fara rayuwar aure mai inganci Wanda musulunci ya tanadar mana, ka yafe min sweety in shaa Allahu bazaka kara samuna da laifi ko wane iri ba, jikin sadeeq ya mutu saboda yadda take mishi waiwaiyi a gaba da bayan wuyanshi, ya kalleta yace komai ya wuce sanah Allah ya yafe mana, ta shige jikinshi tana mishi godiya cikin salonta da tasan yana rikitashi, a wannan daren sanah ta nuna mishi tayi missing dinshi matuka, gareshi kuwa duk wani abu da take mishi sai ya dinga ganin kamar zulface, mikewa yayi babu kwari a jikinshi ya shiga wanka,, bayan yayi wanka yayi alwala ya fito yayi salloli da adduoin da mummy tace ya dinga yinsu, rokon Allah ya dingayi akan ya cire mishi tunanin da ya manne a zuciyarshi kamar mayen karfe, ji yakeyi da da yadda zaiyi ya cire xuciyarshi da ya cireta ya huta ko kuma yayi deleting duk wani tunanin da yakeyi akan zulfah, bai samu bacci ba a wannan daren har saida yayi sallar asuba sannan bacci mai cike da mafarkai ya daukeshi... Yaya abban daddy kazo ka fitar da mu yawo, anty jalila ta fita yawo tace bazata je damu ba kuma muma bazamu zauna a gida ba, ya kalli afrah dake ta mishi surutu yace to maza kuje ku shirya mu tafi bambinos, ihu suka sa dukkansu su ukun suka wuce ya kwalawa amrah kirah dan yasan itace bata da surutu, ya kalleta cikin dabara yace zaki iya kawo min abinci in ci kafin mu wuce, tace kaii bazan iyaba mummy zata min duka in na bata mata abinci, yace kuma gashi jalila bata nan ko, tace eh fatsin ma bata nan saidai ince ma mummy tazo ta zuba maka, yace a'a mummy na hutawa ina ma wannan antyn taku ummm yama sunanta, da sauri tace anty zulfa, yace yauwa ehh ita, je kice ta kawo min, tace ay ta koma skull yaya baka sani ba, yayi dariya yace na manta ne amma ay ni na kaita, tace laaa yaya mu muka kaita da abban ayda banda kai a cikin motar, yace baki dai ganni ba amma motata na bayan taku maza ki shirya mu tafi, ta ruga ciki da gudu, ya mike ya fita da sauri dan karsu sashi yawon da bai shirya ba,, Zama yayi a mota yana tunanin yadda zaiyi ya ganta dan baijin zai iya bacci in har bai ganta ba, ya jingina jikinshi a jikin kujera a fili yace wai meyasa zuciyarshi ta gaza hakuri akan yarinyar nan ne, meyasa takeson janyo mishi raini gurin kucakar yarinyar nan, why?? Tada motarshi yayi zuciyarshi na ingixashi bai tsinci kanshi a ko ina ba sai a kofar "danbo" tsaki yayi sosai yace to me zance mata, wai meke faruwa dani ne?, abunda ya dinga tambayar kanshi kenan, in ya tada mota zaiyi gaba sai ya taka burki, wata zuciyar tace to ka siyan mata wani abu mana kace mummy ce ta aiko ka, murmushi yayi ya tsaya akan wannan shawarar, siyayya sosai yayi mata a wani store ya tsaya ya siyan mata kaza da fresh milk mai sanyin gaske, sannan ya siya fruits kamar hauka a railway, yana zuwa kofar makarantar suka tambayeshi inda zashi, yace yazo ganin kanwarshi ne, mai gadi yace gaskiya ba'a ganin yan extnsion a wannan lkcn, sadeeq yace sako na kawo mata plss ka taimaka in ganta, yayi jumm sannan yace ya sunanta, sadeeq yace zulfa'u, mai gadi yace zulfa'u wa?, sadeeq ya fara kame2 dan ko za'a yankashi bai san sunan babanta ba, mai gadin cikin bacin rai yace I tot as mch nasan kai saurayinta ne kawai,, in da kai yayanta ne na gaske ay zaka san sunan mahaifinta, gaskiya bazaka samu ganinta ba, sadeeq ranshi ya baci sosai yayi tsaki sosai yana ma zuciyarshi nuni da abunda yake gudu kenan gashi tun a gate an fara yasan ita ko kallonshi ma bazatayi ba, zaiyi magana uncle majeed ya fito daga cikin motarshi yace hii sannu, sadeeq ya mika mishi hannu yace yauwa ya kk, uncle majeed yace am fyn kamar naso inganeka , sadeeq yace wrlly, majeed yace yeah brodan smiling beauty ko, sadeeq yace noo zulfa'u dai, uncle majeed yayi murmushi yace ay ita nake nufi, sadeeq yace oo ay bansan nicknm dinta ba kenan, majeed yayi dariya yace muje daga ciki sai in sa a kiramaka ita, motarshi ya shiga maigadin ya bude musu gate sadeeq ya bishi da harara suka wuce, kofar office dinshi sukayi parking ya bude ma sadeeq yace ya shiga ciki bari ya kirata, sadeeq ya shiga kayataccen office dinshi wanda ke cikin cafe, office din da ko student da teachers basa shigarshi, yanzu ma ya shigar da sadeeq ciki ne saboda wata manufa tashi, ya fita yana murna dan yana ganin yau zai mika kokon bararshi gurin yayan smiley, sadeeq zaune a office din yanata kalle2, idonshi ya tsaya chakk kan makeken hoton zulfa wanda akayi mata ranar inter house, sai kuma wani a gefenshi rike da speaker a hannunta duk tayi kyau a hotunan sosai,, kallonsu sadeeq ya tsaya yi haka kawai ya samu kanshi cikin nishadi, yasa hannu jikin hoton kirjinshi na bugawa da sauri2, Salamu alaikum ta fadi hade da shigowa dan duk tunaninta farouk ne, muryarta ta daki dodon kunnenshi ya mayar da bakin glass dinshi da sauri ya waigo, damm!! kirjinta ya buga da karfi ta tsaya tana kallonshi, shima ya kasa dauke idonshi dake cikin glass a kanta..... Mrs tijjani shattima.... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 4⃣3⃣ By Aysha Ya'u Kurah Shuru ne ya ratsa gurin na tsawon mintina 3, zuciyoyinsu kamar zasu fado dan tsananin bugawa, zulfah tayi saurin sunkuyar da kanta kasa muryarta na rawa ta katse shurun tace ina yini, bai bata amsa ba ya tako yazo har inda take, ya kalleta sama da kasa ya lumshe idonshi murya can ciki yace lafy lau, shurun ne dai ya kara ziyartar gurin, kallonta yakeyi sosai tana wasa da yatsun hannunta, ya kauda kanshi da sauri saboda yadda zuciyarshi ke ingizashi yace ummm dama mummy ce ta aikoni muje in ki amshi sakon dan sauri nakeyi, ta gyada kanta ta juya ta fara tafiya kamar wacce kwai ya fashe ma a ciki, ya bude motar ya shiga sakko da kayan motar tanata kallonshi cikin mamaki dan dai babu abinda bata dashi, duka2 ma yaushe ta dawo makarantar da mummy xata kara aiko mata da wasu, muryar uncle majeed taji a bayanta yace badai har zai wuce ba, tayi murmushi kawai ba tare da tace komai ba, ya kalli sadeeq yace tun yanzu zaka tafi har kun gama hirar, sadeeq yace unmmm inada gurin da zanje ne, majeed yace okk to je ki kira su farida suzo su tayaki ko, ko kuma ni in tayaki ya fadi yana mata wani irin kallo mai cike da fassarori, ta zaro ido tayi dariya tace a'a wace ni, bari dai na kirasu ta dauki leda daya tayi gaba ba tare da ta kalli sadeeq dake tsaye jikin motarshi yana kallon irin kallon da majeed ke mata, sai da ta kule sannan ya dauke kanshi hade da ajiyar zuciya ya dawo kusa da sadeeq yana murmushi, sadeeq yace bari na wuce nagode sosai, uncle majeed yace naga kamar kana sauri da akwai maganar da nake so muyi da kai, sadeeq yace okk ba matsala ina jinka, uncle majeed yace maganar mai muhimmaci ce, ko zaka bani numbrka sai inzo gida in sameka, sadeeq yace babu matsala xan iya baka ko 30mnts ne, uncle majeed yaji dadi sosai yace to nagode mu shiga ciki, sadeeq ya rufe motarshi suka wuce ciki, Abdulmajeed ya kalli sadeeq yace magana zanyi maka akan kanwarka, ko kuma ince inason mika kokon bara na gurinku, tun ranar farko da na daura idona akan kanwarka Allah ya jarabceni da sonta, na kasa fada mata ne saboda ina son ta maida hankalinta tayi karatu, kuma inason in fara neman izini a gurin iyayenta shiyasa ban sanar mata ba, yau da na ganka nayi decidn in fada maka so dat kayi min iso gidanku a bani izini, in shaa Allahu zan riketa da amana in har zaka shige min gaba, zufa ce ke ketowa sadeeq tunda majeed ya fara magana, sai da ya kai aya sannan sadeeq ya cire glass din idonshi ya goge zufa a fuskarshi, ya kalli majeed, yace naji abinda ka fada, sai dai kuma am sorry to tll u tanada aure, majeed ya zaro ido yace aure, sadeeq bldly yace yess aure, innalillahi kawai majeed ke fadi a ranshi dan ya gaza yarda da abinda sadeeq ya fada mishi, ya kalli sadeeq idonshi ya soma kadawa saboda tashin hankali yace amma bata taba fada min ba, kuma a skull ma babu wanda ya sani, sadeeq da ranshi ya fara baci ya mike yace to yau na fada maka, abinda yasa take karatu mijinta ba anan yake ba, ya duba agogon hannunshi yace zan wuce Allah ya bamu alkhairi, bai tsaya jin abinda majeed zaice ba ya fita zuciyarshi na suya,,,, A waje yayi parking motarshi saboda bacin rai, ya shiga cikin gidan bai ko kalli masu gadin dake gaishe shi ba, a daki ya samu mummy zaune ita da anty laila suna hira, ya gaishesu ya nemi guri ya zauna, mummy ta kalleshi tace abba lafiya kuwa, anty laila ta mike tace mummy ay kema kinsan bazai wuce yunwa ba, bari in je in kawo maka gas ta fadi tana mishi dariyar tsokana, yayi tsaki a zuciyarshi yace dama yunwa ce ke damunshi da yaji dadi, Dan damuwar dake dankare a zuciyarshi bazata barshi ya iya kai koda rabin loma bakinshi ba, mummy ta juyo sosai ta maida hankalinta a kanshi, tace fada min damuwarka abba, ya sunkuyar da kanshi kasa yana tunanin ta inda zai bullo mata da maganar, saida ta tambayeshi kusan sau hudu, sannan ya daure da kyar yace mummy dan Allah maganar da zan miki karki yi mata wata fassara ta daban, tace uhumm inajinka, yace ammm-- umm dama wa'azi naji akan haramcin abinda kukayi, a firgice tace me mukayi, ya kalleta yace mummy wallhy haramun ne matar aure taje makarantar da maza sukayi mata kawanya, makarantar kwana kuma mummy, ba lallai bane kowa yasan tanada aure, ni kawai fa bawai dan wani abu nake miki maganar ba sai saboda gudun kwasar zunubin da mukeyi dukkan mu, mummy ta harbo jirgin sadeeq, ta hade rai sosai tace a wane hadisin aka haramta makarantar mace, a kirkirarren hadisin kwakwalwarka ko kuwa, yau ne kasan cewa zulfah matarka ce, wato dan kana gudun zunubi ne ma yasa kayi magana a lokacin da karatunta yazo karshe, to ka kwantar da hankalinka dan ni tuni na yanke shawarar rabuwarku saboda bazan cutar da kai da abun da baka so ba, itama gara a saukake mata ta samu wani ta aura kowa ya huta, saboda haka kaje ka kawo min takardarta ni da kai da zulfah duk mu huta da kwasan zunubi, jikin sadeeq babu inda bai bari saboda tashin hankali, ko kadan ya kasa saita kanshi, mummy dake kallonshi ta wutsiyar ido ta rike dariyar da ke son kufce mata ta kara hade rai tace abba magana nake maka, cikin rawar murya yace mummy ay kince baki yafemin ba ko bayan ranki in na saketa, tace ay yanzu ni nace da bakina, wallhy na yafe maka abba duniya da lahira, bazan matsa maka ba tunda kanada wacce kakeso, sadeeq ya mike da kyar kamar xai fadi yace to mummy zan je gida in kawo miki, tace a'a zo akwai takarda anan bari in kira jali--- ya fita da sauri bai jira ta karasa maganar ba,,, dariya mummy tayi sosai tace lokacin ramuwar mu yayi abba, sannan ta mike ta rage a.c dake dakin tana mai jin dadin ganin sadeeq yanzu ya fara son zulfa'u, godiya ta dinga yi ma Allah da ya nuna mata wannan ranar da sauran numfashinta.... Mrs tijjani shattima.. [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: [16:33, 31/01/2016] Aysha Ya'u Kurah: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 4⃣4⃣ By Aysha Ya'u Kurah Allah ne kadai ya tsare sadeeq a hanyar shi ta komawa gida dan sam bai iya kallon gabanshi saboda yadda idonshi ya mishi nauyi sosai, jijiyoyin kanshi sun rike tam kanshi na sarawa kamar zai rabe biyu, motarshi ma a bude ya barta saboda tsabar rudu, bai ko bi takan sanah ba ya wuce daki ya zube a kan gado, kalaman mummy da na uncle majeed suka dinga kai kawo a cikin kwakwalwarshi, ya zaiyi ya fahimtar da mummy halin da yake ciki, ta ina zai bi ya fara fada mata bazai iya sakin zulfa'u ba, duk da yasan ba sonta yakeyi ba amma bazai taba gigin rabuwa da ita ba, ya runtse idonshi kanshi kamar zai fado kasa, mafita ya shiga nema ya kamo can ya kamo nan har dare ya raba bai samo ma kanshi mafita ba, yana idar da sallar asuba ya shirya kayanshi cikin yar jaka karama hade da abubuwa masu amfani, dakin sanah ya shiga ya tarda ta tana wawan baccinta da ta saba, tsaki yaja ya ajiye kudi masu yawa kan mirrow dinta yasa kai ya fita ba tare da ya san inda zashi ba, airport ya nufa zai hau jirgi ya tafi lagos daga nan ya bar kasar ma baki daya, babu mamaki in har baya kasar da take dole zuciyarshi ta hakura da azabtar dashi da takeyi akan yarinyar dashi ba sonta yakeyi, text ya tura ma mummy akan tafiya ta sameshi ta gaggawa dan kar taji shi shuru, tana gama karantawa tayi dariya kawai ta ajiye wayar ta cigaba da adduointa.. A lagos ya kama hotel dan ya dan runtsa kadan kafin yamma ya shirya tafiya inda ya yanke shawarar zuwa wato dubai, karar wayarshi ce ta katse mishi baccin da yakeyi, ya juya yana mika ya dauki wayar, mummy tace an tashi lafiya abba, gabanshi ya fadi sosai ya mike zaune yace laafiya lau mummy, tace naga text dinka kai kuma maimakon ka sauke nauyin dake kanka kafin ka tafi, to yanzu dai ina jiran--- katse wayar yayi da sauri hade da wurgi da ita ta fadi ta tarwatse, idonshi yayi jawur dan ba karamin chaza mishi kwakwalwa mummy takeyi ba, in dai har zata cigaba da mishi wannan maganar to gaskiya bazai kara kiranta ba, wata zuciya tace to kai ka rubuta sakin mana tunda dama ba sonta kakeyi ba, nan da nan wata ta kwabe shi ta mishi nuni da bashi ba kwanciyar hankali in har ya aikata wannan aikin, kwanciya yayi ya kifa kanshi a pillow ko zai samu sauki abinda yake ji, abubuwan sun mishi yawa, shi ya zaiyi da rayuwarshi, haka ya kwanta yanata juyi har la'asar bai kai komai bakinshi ba, rabon da yaci wani abincin kirki har ya manta,, Hello anty dee ina kwana, daga daya bangaren anty amarya tace lfy lau sanah ya gidan da fatan dai kuna nan lafiya, lafiya ba lau ba anty, yanzu na tashi na tarar da kudi akan mirrow na duba ko ina a gidan nan ban ganshi ba kuma na duba jakar da yake tafiya da ita duk basa nan, anty amarya tace yanzu kika tashi kika ce, wace matar aurece mai neman martaba a gurin mijinta zata kai har sha biyu tana bacci, ashe sanah baki ji fadan da nayi miki ba, bazaki taba canzawa ba dan haka makomarki wallhy, karki kara nemana tunda kin maida ni mutuniyar banza ta kashe wayar ranta a bace, ta mike ta wuce kitchen tana mita a zuciyarta dan sanah tana neman ta wargaza mata plans dinta gashi har yanzu babu labarin daukar ciki bare har ta samu dan da zai zame musu garkuwa, taja tsaki ta bude fridge ta kwankaďi ruwan sanyi ko hankalinta zai kwanta... Mrs tijjani shattima... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: [20:09, 31/01/2016] Aysha Ya'u Kurah: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 4⃣5⃣ BY Aysha Ya'u Kurah Zulfa'u zaune a daki ita da jalila suna duba prizes din da ta samu ranar speech dinsu, suka dinga budesu cikin nishadi suna hirah, gift din da uncle majeed ya aiko a bata ta bude cards ne da turaruka sai wata guntuwar letter, da sauri jalila ta dauki letter tana dariya ta bude, ta karanta, kai ta girgiza cikin tausayinshi da ta gama karantawa, ta kalli zulfa dake karanta cards tace uncle majeed yasan kinada aure ne, zulfa ta ajiye cards din tace a'a, jalila tace ya akayi ya sani, gashi karanta, wai yana miki fatan alkhairi a rayuwar aurenki, zulfah ta karba ta karanta a zuciyarta tace to waye ya fada mishi, kenan wannan shine dalilin canjin da yayi mata har suka gama exams baya ko bari su hadu, jalila ta katse mata tunanin da takeyi tace Allah sarki majeed ba tun yau nasan ya kamu da sonki ba, tun ranar inter house na dinga lura da yadda yake miki, walhy badan ke matar aure bace da na shige mishi gaba saboda sai macen dake very lucky ita zata iya sace zuciyar irin su, zulfah jikinta yayi sanyi a zuciyarta tace aure ko so called aure, ita yanzu bata daukar kanta macen aure walhy badan tana ganin darajar mummy ba da ta nemi mummy tasa ya sauwake mata itama tayi rayuwarta ta zabi wanda zai sota itama ta soshi, wayar jalila ita ta katse mata zancen zucin da takeyi, jalila tayi murmushi ta dauki wayar ta shiga hira da saurayinta wanda aka sa musu rana tare, sai da ta kusa minti goma tana waya sannan ta kashe ta kalli zulfah da ke kara kallon letter, ta fisge tace haramun yarinya, kina tunanin wani namiji kuma kinada miji, gara ma muje mu kwanta saboda gobe da wuri ishaq zaizo mu tafi rabon I.v da ashoebi, zulfah ta tattare kayanta jikinta a sanyaye ta zuba cikin wardrbe, sannan ta kwanta tana tunane tunane aranta, Watan sadeeq biyu bai waiwaiyi 9ja ba, daga ka ganshi kasan yana cikin matsananciyar damuwa, ya rame sosai saidai yayi fresh fatarshi ta kara haske, baya waya da kowa a gida sai daddy da yayi ma karyar wasu takardu yaje amsowa, mummy ma ta dan damu da rashin sadeeq, hankalinta kan kwanta ne in daddy yace mata suna waya, Sanah kuwa ko a jikinta dan harka ce ta bude mata na tara kawaye da maza abokan harkarta, ko tunanin sadeeq ma batayi bare tayi kewarshi tunda ta samu wadanda take ganin sun fishi iya harka, (wa iyazubillah) A cikin satin ne yaji gaba daya bazai iya cigaba da zaman dubai ba, abinda yakeji game da Zulfa'u ya karu matuka a zuciyarshi fiye da kwanakin baya, tunanin da ke hanashi komawa bai wuce abinda zai ce ma mummy ba, yasan tana kan bakarta na sai ya saki zulfa, dafe kanshi yayi idonshi ya ciko da kwalla yace zai hakura kawai ya rubuta mata sakin ya bata ko da kuwa hakan zai zama ajalinshi, dan bazai kara tafiya ko ina ba kuma bazai kara nunawa mummy bazai rubuta ba saboda kar su ga kamar sonta yakeyi, shi kuwa a ganinshi ba sonta yakeyi ba kawai dai zuciyarshi ce ke matukar bashi wahala akan tunaninta, Karfe 8 na dare ya isa gida dan yaso ya kwana a abuja saboda dare amma sam zuciyarshi taki bashi hadin kai, a bude ya tarar da kofar parlon dan haka ya shiga ya rufo kofar ya wuce dakinshi ba tare da ya kalli dakin sanah ba, sai da yayi wanka sannan ya fito ya shiga dakin sanah, kwance ya sameta cikin bargo kanta a ya mutse, tana ganinshi ta mike zaune daure da zanin gado a kirjinta, zaro ido tayi cikin firgici tace yaushe ka dawo, ya harareta ba tare da yace mata komai ba ya juya saboda wani irin wari da yakeji a dakin, ta mike da sauri ta fada bayin ta samu Nasir dake wankan tsarki tace shikenan mun shiga tara ma ba uku ba nasir, yace lafiya me ya faru, tace shi ne ya dawo, yace shi wa,? tace sadeeq mana, ya wurgar da sosan hannunshi yace wayyo Allah na, saida nace miki muje hotel kika ki, gashi yanzu kin sani cikin matsalar da zata iya shafar career ta, tace kai career ka kakeji ni da aure na zai mutu fa, kasan yadda nakeson wannan auren kuwa, nasir ya harareta zaiyi magana muryar sadeeq ta hana shi, kwala kiran sanah yakeyi kamar zai tsaga gidan, da gudu ta fito tace ma nasir ya sa key a kofar, towel ta daura ta fito parlon tayi hanyar kitchen ta ganshi tsaye fuskar nan a hade kamar hadari, ta tsaya a gabanshi jikinta na rawa tace gani, ya harareta yace kalli kitchen dinnan, yanzu ke tsakaninki da Allah zaki iya cin abinda ya fito a kitchen dinnan, wannan wace irin kazanta ce kitchen sai wari yakeyi abinci sun fara rubewa, kalli,, ya fara bude kulolin yana nuna mata, wani irin kara yayi da ya bude wata kular amala da ta fara tsutsotsi, fita yayi a kitchen din yana masifa kamar zai ari baki, ya dauki key din motarshi yace wallhy taallhi in na dawo baki gama gyaran kitchen din nan da parlo ba wallhy sai dai ki nemi wani gurin ki kwana amma ba nan ba, kazama kawai, ya fita yana tsaki hade da tsirtar da miyau, Ajiyar zuciya sanah tayi ta koma daki tace ma nasir ya shirya ya tafi da sauri tunda sadeeq ya fita, da sauri ya gama sa kaya ya fita har yana karo da kofa, saida ya fita sannan ta koma kitchen ta tattara duk kulolin da abinci ya rube tana yatsina fuska ta fita ta zubar dasu a cewarta zata siyo wasu gobe dan bazata iya sa hannu a cikin kulolin ba, ta wahala sosai gurin gyaran kitchen da parlon duk da haka bai bada wani qamshi mai dadi ba haka ta wuce bayi tayi wanka,, Sadeeq gidansu ya nufa ranshi na baci da irin kazantar sanah, har ciki ya shigo da motarshi yayi parking, daga cikin mota ya hango farouk da zulfah tsaye a hanyar shiga parlor sai hira sukeyi tana dariya harda kyakyatawa, a hankali ya fito daga motar ya kasa dauke idonshi a kansu zuciyarshi na bugawa sosai saboda ta hango abinda take tunani dare da rana, farouk ne ya fara ganinshi yace yaya abba ya matso kusa dashi yana murmushi yace yaushe ka dawo, sadeeq idonshi na kan zulfah da ta dukar da kanta gashinta da yasha ribbons ya kwanta a gefen wuyanta yace yanzu na dawo farouk, welcm farouk yace sannan ya kalli zulfah yace bari in shiga in fito, ta dago kanta tace to, ta kalli sadeeq tace ina wuni, ya amsa yana tafiya ciki kamar baya son amsawa, tabe bakinta tayi saboda kiyayyarshi yanzu ta daina damunta tunda itama ta daina jin masifaffen sonshi da take kiranshi da kaddara, Mrs tijjani shattima... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: Mrs tijjani shattima... [20:20, 31/01/2016] Aysha Ya'u Kurah: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 4⃣6⃣ By Aysha Ya'u Kurah Cikin faduwar gaba sadeeq ya karasa cikin parlon ya tsuguna ya gaisar da su mummy, mummy da anty amarya suka amsa a tare daddy yace yaushe ka shigo, sadeeq yace yanzu daddy ina wuni, lafiya lau daddy yace, sannan yace Allah yasa ka samu takardun, sadeeq ya sosa keya yace a'a zan dai koma in an gama kammalawa, yace to madallah, suna dan hira sadeeq na satan kallon mummy ko zatayi mishi maganar zulfah, har ya gama zamanshi yaci abinci bata ce mishi komai game da zulfah ba, shi kam hankalinshi ya kwanta dan ya dauka ta hakura ne, sai aftr 10 ya bar gidan cike da farin ciki... an fara bikin "jalila da captain ishaq tambuwal" kwana biyu da dawowar sadeeq, tsaftataccen biki akeyi sosai na masu nairah, anyi kamu ranar thursdy, ranar friday da xa ayi "sword crossing" tun safe suke preparation ankon su material army green da maroon head, wani irin dinki akayi musu iri daya ita da zabba'u kanwar hilal saboda sune manyan kawaye, suna zaune suna cin abinci farouk na gefensu shima abincin yakeci gidan cike yake da baki, zabba'u ce ta shigo da silk dinsu a hannunta ta zauna tana maida numfashi tace dakyar ya dawo ya bani head dinnan wallahy, jalila tace ay yaya hilal sai a slow shi a sanshi ma wai kar ayi wasu kide2, zabba'u tasa hannu a abincin tace rabu dashi dalla auren zamani ay dole sai mun chashe ko yaya farouk, ya mike yace ba ruwana karku sani a ciki mudai yan zuwa kallo ne, zulfah ta harareshi tace kallon ma kar ku je tunda duk daya ne ay, yayi murmushi yace in dai kawar nan taki xata zo to babu abinda zai hanani zuwa, jalila ta kwashe da dariya tace wai yaya farouk da gaske kake san rolex kakeyi, yace ban sani ba, ya fita suka kwashe da dariya zabba'u tace su umaran mummy an girma, zulfah tace lallai ma, to ke da haka kike, ku kyale min angona ya sakata ya wala, sukayi dariya jalila zatayi magana sukaji karar wayarshi a gurin da ya tashi, zulfah ta kalli wayar tace manta ta yayi bari in kai mishi, ta mike da sauri dan kar wayar ta tsinke, kofar dakin ta tura hade da sallama tace gashi da sauri kiranka akeyi, tasa mishi a kunne tace na riga nayi picking, shurun da taji ne yasata kallonshi da kyau ta firgita dan kusan kaya iri dayane a jikinsu na farouk milk wannan white, ta mudubi ta kalleshi ta saki wayar lokacin da suka hada ido, ahankali ta fara zare hannunta , da sauri zuciyarshi ta ingiza shi ya riko hannunta ya juyo yana kallonta jikinta na rawa, tace walhy gurin yaya farouk nazo bansan kai bane dan Allah kayi hakuri, ya lumshe idonshi ya bude yana kallonta sama da kasa idonshi ya tsaya kan hadadden lallen kafarta, gefen hagu da dama na zuciyarshi suka dinga kokawa akan ka saketa ta tafi kar ta raina ka, dayar tace ka rungumeta zaka samu saukin radadin dakake ji game da ita, zulfah ta fara kokarin kwace hannunta tana ja baya kar wani yazo ya gansu ga kofa a bude, da kafarshi ya tura kofar ya rufeta tasa daya hannunta jikinta ya tsananta rawa zata bude kofar ya matseta sosai, yana iya jiyo bugun zuciyarta, takalmin kafarshi ya cire yasa kafarshi yana shafar kafarta a hankali, ta runtse idonta ta daga kanta sama numfashinta na neman daukewa, kallonta yakeyi zuciyarshi na tunzurashi tana fada mishi tunda mallakinka ce komai kayi mata lada zaka samu ba zunubi ba, kara matse hannunta yayi cikin nashi yana murzawa nan da nan idonshi ya kada ya kai bakinshi wuyanta yayi mata kiss a hankali, kuka ta fashe dashi a hankali jikinta na rawa sosai tana kokarin kaucewa daga jikin kofar saboda abinda yake mata yafi karfin daukar kwakwalwarta, rungumeta yayi sosai a jikinshi yana shafar bayanta, ko kadan hankalinshi baya jikinshi, turashi takeyi iya karfinta tana fadin ka rufa min asiri, wallhy mummy na kirana dan Allah ka bar-- ya daura bakinshi kan nata ta kara runtse idonta ta datse bakinta sosai, bin fuskarta yayi da kallo zuciyarshi cike da nishadi, bude idonta tayi a hankali ya sauka cikin nashi ta kara runtse su tana kokarin yin wani kukan, tsintar kanshi yayi yana murmushi ya kara maida kanta cikin kirjinshi zuciyarshi tayi tass kamar babu wata damuwa da tayi katutu acikinta, jin an murda kofar yasa shi sakinta ya maida idonshi kan kofar, farouk ne ya shigo ciki yana waka, a bakin kofar ya tsaya yana kallonsu, zulfah ta kasa hada ido dashi tace wayarka ake kira gata can ta nuna mishi ta bi ta gefenshi zuciyarta a dagule babu wani farin ciki a cikinta,, farouk yayi murmushi ya karasa ya dauki wayarshi yace yaushe ka shigo yaya abba, sadeeq yace tun dazu, na kira wayarka ay hilal yace ya baka sako ka bani, farouk yace eh na dauka ma ba yanzu zaka zo ba yana gurin mummy, sadeeq yace okk sannan ya fita farouk ya bishi da kallo yace Allah ka dai2ta wadannan bayin naka dan sunyi matukar dacewa da juna,, Mrs tijjani shattima... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ZULFAH ◆◆ 4⃣7⃣ By Aysha Ya'u Kurah Dakin mummy ya wuce yana gaisawa da bakin da suka cika gidan, zaune ya sameta da wasu bakin ya tsuguna ya gaishesu suka amsa mishi da fara'arsu sannan ya kalli mummy yace mummy farouk ya baki sako ko? ta mike tace eh dama ina son ganinka, gaban sadeeq ya fadi sosai ya mike ya bi bayanta yana adduoi cikin zuciyarshi, dayan dakin suka shiga ta mika mishi sakon da hilal ya bayar a bashi sannan ta mika hannu tace bani,, gabanshi ya tsananta faduwa ya dake yace me zan baki mummy? Ta harareshi tace baka ma san abinda zaka bani ba ko?, to takaddar zulfah nake nufi, saboda inason tunda babu idda akanta a hada bikinta gobe dana jalila Allah cikin ikonsa yasa ta samu mai kaunarta har na ma bashi saboda haka rubuta kawai ka bani kafin ya kawo sadakin, gumi ya shiga tsatstsafo wa sadeeq tsayuwa ta gagari kafarshi, ya zauna a kasa ya dukar da kanshi cikin sarkakakkiyar murya yace mummy Allah baya son saki, da sauri tace amma ya halasta shi ko?, yayi shuru ya kasa bata amsa, tace tunda dama babu wanda yasan matarka ce sai mu, kaga sai ka saukake mata saboda abincin wani gubar wani kuma hilal tun tana yar aikinta da ka fada mishi yake sonta dan haka maza rubuta karka bata min lokaci ina da abubuwan yi, shuru sadeeq yayi yana share zufar da ta jika ko ina a jikinshi zuciyarshi kamar zata buga saboda tsananin tashin hankali, mummy taji shurun yayi yawa tace abba a tsaye nake fa, ya rike kafarta ya dago jajayen idonshi ya kalleta yace ki yi min rai mummy, , dan Allah dan son annabin Allah ki bar wannan maganar, tace kamar yaya in bar wannan maganar, kana nufin zan cigaba da zama da ita a gabana ne kamar hoto, itama tana feelns ay ba dutse bace, bazan taba cigaba da cutar da ita ba, gara ka saketa ta samu mahaďinta itama kamar yadda kaima kake da mahaďi, ga dukkan alamu mummy so takeyi ya mutu a wannan lokacin, kara rike kafarta yayi yace Alla--- ka daina hadani da Allah abba, ya zaka dinga hadani da Allah muna cutar yarinya, ta kusa shekara uku a gidan nan baka taba maganarta ba, baka taba cewa yau wannan matata ce bari in sauke nauyiyyikanta da ya rataya a wuyana ba, yanzu dinma bansan me kake nufi ba tunda har yanzu ba sonta kakeyi ba, dan Allah abba ka rubuta sakin nan ka bata gobe in maye gurbinka da hilal dan Allah, wani irin kuka ya fashe ma mummy dashi zuciyarshi kamar zata tarwatse saboda kalamanta na karshe gashi shi ya kasa gasgata sonta yakeyi ko kuwa, shidai yasan yana jinta a dukkan ilahirin gabobinshi da jinin jikinshi,, Mummy taja baya da sauri tace kuka kuma abba, me nayi maka, cikin kuka ya mike yace wallahy mutuwa zanyi mummy, wallhy bazan iya sakinta ba in kuma kika matsa wallhy zan mutu, cikin halin ko in kula tace duk wanda ya mutu lokacinshi ne yayi Allah ya jikanka in ka mutu amma sai ka rubuta, na shiga uku ya shiga fadi kamar karamin yaro yana ta yarfe hannu hawaye na bin idonshi, mummy tace baka shiga ba tukunna dai abba, ya kasa magana sai kuka yakeyi sosai mummy ta matso kusa dashi a hankali tace abba sonta kakeyi? Ya dago kanshi ya shiga girgizawa yace bana sonta amma bazan iya rabuwa da ita ba, mtswwwwww mummy ta fadi saboda takaici tace kaji na rantse idan baka rubuta min takardarta ka bani ba yanzu sai tsine maka, ya mike tsaye kamar zararre yace ki rufa min asiri mummy, wallhy bazan rayu ba in na rabu da ita, dan Allah mummy ki taimakeni, ta daka mishi tsawa tace wallhy bazan bari aurenka ya kai gobe a kanta ba abba, dole ka saketa gobe a daura mata wani auren itama, yace mummy ki bari in tambayeta ko ita tana sona mana, ki bari mu zauna tare dasu daddy in bata sona na yarda zan saketa, mummy tayi kwafa tace Allah ya kaimu yau komin dare sai ka rubuta, kuma ko tana sonka bazan bari ba sai ka saketa saboda ka cika son kanka dawa, tayi tsaki ta fita tana masifa tabar sadeeq tsaye sai kuka yakeyi yana nemowa kanshi mafita, saida ya kusan minti talatin sannan ya fito bayan ya gama yanke shawarar daura mata iddar da mummy ke tutiyar bata dashi, motarshi ya shiga zuciyarshi a dagule yana tunanin rabuwa da zulfa'u, sam bazai iya rabuwa da ita ba, gurin hilal ya yanke shawarar fara zuwa yaci mutuncin shi kafin ya wuce gurin da suke sword crossing din, har ya kama hanya wata zuciya ta kwabeshi akan in kaje me zaka cewa hilal, kana ma sonta kenan, kuma kai shikenan akan mace sai kayi ta fada amininka, tunanin irin fadan da sukayi akan sanah da yadda suka dau lokaci kafin su shirya shi ya hanashi zuwa gurin hilal, to amma meyasa hilal zaiso matarshi why,?? yayi tsaki ya juya ya nufi sde rsrt,, a harabar gurin yayi parking ya zauna cikin motar zuciyarshi na zafi saboda mummy na neman daura mishi ciwon da baisan wani bangare bane zai fara kamuwa da ciwon saboda yadda yakeji,, yana cikin tunanin ya hangosu ita da zabba'u sun fito daga ciki da jakar kayan waleed din anty laila a hannunta sunyi kyau har sun gaji, zabba'u ta juya ciki sakamakon kiranta da akayi , zulfah ta fara takawa a hankali ta karaso kusa da motar anty lailah tasa key ta bude, tunda take tahowa yake kallonta baya ko kiftawa fitowa yayi da sauri lokacin da ta tura kanta cikin motar, tana dagowa taga inuwar mutum a bayanta ta juyo da sauri cikin firgici, suna hada ido ta maza ta kauda kanta ta kama murfin motar zata rufe ya rike hannunta hade da murfin yana bin ko ina na jikinta da kallo, , janyota yayi ya rike kugunta sosai ya tura motar, ta dinga waige2 tana kokarin kwace jikinta kara riketa yayi ya bude motarshi a hankali kamar mai raďa yace shiga muje, ta juyo cikin rashin fahimta tace ina zani, ni dan All---- ya turata cikin motar yayi lockn dinta yana jinta tana bubbuga glass din motar ya koma ya rufe ma anty laila tata motar sannan ya dawo ya shiga ya ja suka wuce, duk irin ihun da takeyi bai saurareta ba har suka kai kofar gidanshi tana kuka..... Mrs tijjani shattima... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 4⃣8⃣ By Aysha Ya'u Kurah Horn yayi mai gadi ya bude mishi da sauri yana sara mishi, yayi parking motar ya kalleta ta hada kanta da murfin motar tana kuka harda shashsheka, ya bude motar yana shawara da zuciyarshi akan ya maida ita kawai karta rainashi, ya tsaya jimm kusa da kofar motar yace to ay in ya maida ita ba tare da ya daura mata idda ba tabbas gobe mummy xata bawa hilal, gara ya daura mata idda ya saketa, yasan zai iya maida ita tunda har sai tayi wata uku, "(hmmmm) " bude motar yayi ya tsuguno da kanshi cikin rarrashi yace kukan me kikeyi, bata dago kanta ba tace ni ka maida ni gida, yace to sakko zan dauki wani abu ne sai mu tafi, ta kara matse kanta tace um um kaje ina jiranka, ya shafo gashin kanta yace kina biye ma jalila kina matar aure kina barin jikinki a bude kina kwasar zunubi ko, ranta ya fara baci tace ni ba matar aure bace, dan Allah kazo ka maida ni gida, yayi murmushi yace lallai ma yarinyar nan wato baki daukar kanki matar aure ko, tayi banza dashi, da yaga yana lallabata tana bata mishi lokaci ya dauketa cak tanata ihu tana zillo, riketa yayi sosai bai damu da ihun da ta cika mishi kunne dashi ba har saida ya shiga parlor ya wuce dakinshi da ita, kwantar da ita yayi kan makeken gadonshi, ta mike da sauri ta diro tana ihu jikinta ko ina rawa yakeyi, kafin ta kai kofar ya rigata ya murdeta da key, , ta matsa jikin kofar tana ihu tana girgizawa ko zata iya budewa ta jingina jikinta jikin kofar tana kuka kamar ranta zai fita, dariya yayi ya karaso kusa da ita yace ki daina kukan nan dan ba wanda zai ji ki, gara ki zo ki zauna muyi magana, tace ni a'a wallhy bazan zauna ba, kuma duk abinda kamin saina fadawa mummy, yayi murmushi yace ita tace inje in dauko ki ay, ya kamo hannunta yace kuma kinsan meye, ta kwace hannunta tace dan Allah ka bude min kofa in tafi gida banason sanin komai,, shuru yayi yana kallonta, ta karkatar da kanta idonta na zubar da ruwa tace Allah fa nace, yayi dariya ya janyota ya rungumeta yace nima Allah nace, Tace to me kakeso inyi maka, yace yauwa maganar da zakiyi kenan kin tsaya munata bata lokaci, ya dago fuskarta ya share mata hawayen fuskarta yace karki kara kuka kinji, ta gyada kanta tana kokarin shanye hawayen dake kokarin zubo mata, yace au wani kukan ma zakiyi, ta girgiza kanta tana boye fuskarta saboda hawaye ya riga ya zubo a kan kumatunta, Yayi murmushi ya kara share mata hawayen, ya jata suka zauna gefen gado, a hankali ya fara magana, yace kinga yanzu shida ta wuce ko, ta gyada kanta, yace gud, to idan kika bani hadin kai cikin mintina kadan zan maida ki gida kinji, da sauri tace to,, yayi murmushin jin dadi dan yasan bazai sha wahalar yi mata wayau ba, ya matso sosai kusa da ita ya dago kanta yana kallon cikin idonta, a kunne ya rada mata abinda yakeso ta matsa da sauri tana girgiza kai tace wallhy bazan iya ba, na shiga uku na, dan Allah ka taimakeni ka mayar dani gida, ya mike yana mika yace kina son kwana a gidan nan kenan, tace a'a, yace to zabi ya rage naki, ta kara sa kuka tace wayyo Allahna nasan yanzu ana can ana nemana, ya ciro wayarshi a aljihu yace haka ne kin tuna min bari in kira mummy in fada mata gaki nan kin kawo kanki gidana kince ke a gidan mijinki zaki kwana, ihu tayi sosai ta sa hannu zata kwace wayar ya rike wayar hade da hannunta, cikin kuka tace karya haramun ne kuma walhy wutar jahannama Allah zai saka in har kamin sharri, ya janyota ya rungumeta yana dariya sosai harda rike ciki, ya fara shafar gashinta har wuyanta yace dagaske kikeyi wuta za'a sani, ta ture hannunshi tace ban sani ba, ya dago kanta yace ni kika ture ma hannu, muryarta na rawa tace to ka mayar dani gi--- shigar bakinshi taji cikin nata cikin wani irin rikitaccen salo, kuka takeyi tana kokarin kwacewa ta kasa, sadeeq ya riga ya shagala, kukan da takeyi ma kamar tana kara ingizashi ne, bai ankara ba yaji cizon da ya gigita shi a harshenshi, cire bakinshi yayi da sauri yana fadin "aushhhh", ya kalleta idonta a runtse ta datse bakinta yace yau zan nuna miki na fiki iya mugunta, tunda na biki ta lalama kinki, cak ya dauketa ya daurata akan gado duk ihun da takeyi baisashi ya daina abinda yakeyi ba, zulfa taga duk ihu da dukan da take mishi baisahi ya kyaleta ba, ta shiga hadashi da Allah akan ya kyaleta, inaaa sadeeq bai ma san tanayi ba shima hakurin yake bata cikin rudewa dan sam hankalinshi baya jikinshi, saida ya cire mata kaya sannan ya shiga aika mata da sakonni masu rikitarwa, ihun da naji cikin dashashshiyar yasa na gane sadeeq ya maida zulfa'u cikakkiyar mace, sambatu kawai yakeyi cikin ficewar hayyaci, shi kanshi baisan abinda yake fadi ba saboda bai taba tsintar kanshi cikin wannan ni'imtaccen yanayin ba... Mrs tijjani shattima.. [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: [11:08, 02/02/2016] Aysha Ya'u Kurah: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 4⃣9⃣ By Aysha Ya'u Kurah Kuka zulfah takeyi muryarta bata fita saboda azaba a zuciyarta tana jin haushin sadeeq saboda ya gama bata mata rayuwa kuma ba sonta yakeyi ba, shi kuwa sadeeq gefe ya mirgina ya rungumeta tsamm a jikinshi hawaye na fita a idonshi, gaba daya ya rasa ta inda zai fara fada mata irin tsananin kaunar da yake mata ta yarda dashi, sai yanzu yasan meye ainihin kalmar da ake kira so, ashe shirme yayi lokacin da yayi haukar son sanah, yanzu ne ya gane dimbin kaunar da yake ma zulfah, da wani baki zai fara fada mata yana sonta, in ya tuno abubuwan da yayi mata a baya sai yayi tsaki a hankali yaji ya tsani zuciyarshi da bata mishi nuni da irin wannan ranar ba lokacin da idonshi ya rufe, kenan wannan ranar ita ce ranar da anty laila ke nusar dashi a kullum, runtse idonshi yayi hawaye masu zafi suka zuba a goshin zulfah, a hankali ya fara magana kamar mara gaskiya, kiyi hakuri I don't mn to hurt u, ki yafe min plss karki hukuntani akan kurakuraina, zan iya jure komai amma banda hukuncin da zaki min, nasan ni mai laifi ne, dan Allah kiyi hakuri, Dan Allah ka kaini gida ta fadi tana ajiyar zuciya, yace nan ma gida ne, babu wanda zai zarge ki in kika kwana gidan mijinki, ta runtse idonta tana kukan takaici dan tasan jikinta kawai sadeeq ke so ba ita ba, ya matseta sosai yana rarrashinta yace zan maida ke gida amma sai kin daina kukan nan, ita dai babu abinda tace mishi, ya juyo fuskarta ya goga hancinshi kan nata yace kinga yadda fuskarki tayi, ya fara lashe hawayen dake kwance a kan kyakykyawar fuskarta, "I LOVE U" taji ya fada mata a kunnenta, ta bude idonta da sauri tana kallonshi, ya lumshe idonshi yana shafa mararta yace I love u so much, ta kauda kanta tana kukan jin karyar da ta fito daga bakin sadeeq, bakin da yace bazai taba sonta ba har abada wai shine yake fada mata wannan kalmar, ya marairace murya can kasa yace ki daina tunanin komai wallhy ina sonki son da bazan iya ma misalta miki shi ba, dan Allah ka rabu dani da kalaman nan naka nagaji da jinsu nidai ka maida ni gida, yayi murmushi ya dauketa ya kaita bayi ya taimaka mata tayi wanka sannan suka fita har lokacin idonta bai bar zubar da hawaye ba, taimaka mata yayi ta shirya yana kallonta yana tausayin kanshi in har mummy tayi yunkurin rabashi da ita, jallabiya yasa yayi sallar magriba yayi adduoi sosai akan Allah ya sanya ma mummy hakuri yasa tabarshi da matarshi da yake jinta har cikin bargon shi, mikewa yayi ya kalleta yace har yanzu kuka, to bari in jiraki ki gama sai mu tafi, da kyar ta iya mikewa saboda azaba tace ni ba kuka nakeyi ba, yayi murmushi ya kamata suka fito parlon, yaso ta zauna tasha tea amma fir taķi, har sun kusa fita yaji wani ihu a bayanshi ya waiga yaga sanah tsaye idonta ya rine saboda kishi, da sauri ta matso kusa dasu tace zina har cikin gida sadeeq, ta fara ihu tana daura dankwali a kugunta, ya kara rungumo zulfah yace ke dakata2 kalleta da kyau wannan matata ce, Allah ya tsare ni da yin zina da matan banza kema shaida ce tunda ban taba kusantar ki ba har saida na aureki so ki dinga sanin abinda zaki fada, da karfi tace kan bala'i mata fa kace, yaushe ka dauketa a matsayin matarka, ta kalli zulfah dake kuka tace munafuka wallhy kinji kunya ba"a sanki amma saboda kulafuci da shegen son maza sai da kika biyoshi har gida, kinyi asara wall--- sadeeq ya dauketa da mari yana huci, ta rike kuncinta tana kururuwa, tace wallhy yau sai na kashe yarinyar nan, wallhy saidai ko ni ko ita, ta ruga kitchen kamar tababbiya, sadeeq ya dauki zulfah saboda tafiyar da takeyi ya kaita mota da sauri ya shiga ya ja baya yana hangota ta fito da wuka tana ihu tana tsalle kamar mahaukaciyya.. Zabba'u ta fito daga cikin hall din tana neman ta inda zulfah tayi bata ganta ba, taja ta tsaya tana jiranta ta dawo suje su fara rabon souvenirs, shuru Zabba'u taji har kusan minti talatin, tayi gurin parking motoci ta dinga dubawa babu zulfah ba alamarta, cikin kidima ta koma hall din tana dubawa ko tana ciki nan ma bata ganta, har kusan 1hour tana dubata, share zufar fuskarta tayi taje kusa da anty laila tace anty zulfah ta maido maki da key ne, anty laila tace yanzu na gama maganarta wallhy tana ina, Zabba'u tace wallhy ban ganta ba anty kuma na duba ko ina, anty laila ta mike tace saidai ko wani gurin ta shiga suka cigaba da dubata bata ba alamarta, Zabba'u ta kira farouk ko ya tafi da ita gida, yace a'a kuma gashi a gida bata nan, har aka tashi a gurin hankalinsu a tashe yake saboda ko alamunta basu gani ba, kuka jalila ta fashe dashi suka dinga bin layin kaff babu zulfah, to ina ta shiga haka wasu suka dinga fadi, laila ta kira nurain ta fada mishi yayi salati yace garin yaya, tace aikenta mota nayi ban kara ganinta ba, innalillahi kadai yake fadi sannan ya kashe wayar ya shiga ya fadawa mummy, mummy ta rude sosai dan ko mayafi babu akanta ta fito tana salati, nurain yace mummy ki kwantar da hankalinki, tace ta yaya hankalina zai kwanta ba'a ga yar mutane ba, ta zauna a parlor tana kuka tana jiran dawowar su jalila, suna shigowa ta mike tace an ganta, jalila cikin kuka tace wallhy babu inda bamu duba ba;, mummy ta koma ta zauna hawaye na bin idonta tana fadin ta shiga uku waye ya sace yar mutane, aka dinga ba mummy hakuri amma bata ko kallonsu dan tana tunanin abinda zata fadawa mahaifin zulfah, sam basu kawo su kira sadeeq ba saboda sun san zaiyi wuya ya dauketa tunda ko magana basu yi to me zai mata ma in ya dauketa haka zuciyoyinsu suka dinga sakawa, har kusan 8 babu labarinta, daddy ma ya shiga tashin hankali yasa nurain ya fita yaje ya sanar ma yan sanda, anty amarya na zaune itama tana kukan munafurci tana rarrashin mummy.. Gasashshiyar kaza ya biya ya siyo da madara, yana kallonta tana kuka bai ce mata komai ba suka wuce, a zuciyarta tana tunanin me zata ce ma su mummy, shima yana tunanin karyar da zaima mummy dan yasan hankalinsu a tashe yake, yana isa kofar gidan ya shiga ciki ya bude mata mota ta fito tana share hawayen da yake zubo mata ya rikota suka kama hanyar shiga cikin gidan,, da nurain suka fara karo lokacin ya fito zai kai report, tsayawa yayi yana kallonsu baki sake, sadeeq ya kalleshi yace ina wuni, nurain bai amsa ba ya juya ya kalli zulfah da fuskarta ke kumbure yace me ya sameki, ta girgiza kanta hawaye na ambaliya a idonta, tace bakomai, cikin rashin gamsuwa yace okk ya wuce ciki suna binshi a baya.... Mrs tijjani shattima... [13:39, 02/02/2016] Aysha Ya'u Kurah: ◆◆ ZULFAH ◆◆ [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: ♢♢50♢♢ By Aysha Ya'u Kurah Mikewa mummy tayi da ta hango zulfah ta karasa kusa da ita ta rungumeta tana shafa fuskarta, tace meya sameki, ina kika shiga, zulfah ta fashe da kuka ta kasa magana, mummy ta kalli sadeeq da kanshi ke sunkuye tace me ya sameta abba, fadamin abinda kayi mata, daddy yace Aisha ki nutsu mana su zauna sai muji abinda ya sameta tunda Allah yasa an ganta, tayi kwafa tana hararar sadeeq ta ja zulfah suka zauna, daddy ya kalli zulfah a hankali yace ina kikaje, ta dago kanta cikin muryar kuka tace nnn.. a... sadeeq ya amshe da sauri yace daddy naje gurin bikin ne sai na ganta a waje a haka tana hira da wani shine ni kuma naga zunubi take ďiba saboda ba muharraminta bane shine na dauketa muka tafi gida kafin a tashi sai in dawo da ita gida dan nasan in na maidota gida a wannan lokacin zata iya komawa gurin,, zulfah ta kwalolo ido tana kallon sadeeq yadda yake sharo karya, mummy cikin fushi tace kai za a rubutawa zunubi ko ita, ina ma ruwanka da ita dan ka ganta da wani, wllhy ka fita idona in rufe in dai baso kakeyi ranka ya baci ba, kuma ka miko min takardarta yanzun nan,, kowa a gurin saida ya girgiza da jin kalaman mummy, daddy ya kalleta yace wace takadda kike nufi Aisha, tace takardar saki nake nufi, gobe in shaa Allahu za'a daura mata aure da hilal har na karbi sadakinshi, "innalillahi wa inna ilaihi rajiun" abinda daddy ya fadi kenan yace kina da hankali kuwa Aisha, kin taba ganin inda aka karbi sadakin wani da auren wani akan yarinya, tace an fara daga kan zulfah saboda ina da tabbacin nata auren zai kare yau, daddy yayi ajiyar zuciya ya kalli sadeeq yace abba kunyi da mahaifiyarka zaka rabu da matarka ne, ka fa daina cewa matarshi dan ta kusa zama ba tashi ba mummy ta fada tana gyara zama, sadeeq yace daddy dan Allah ka bawa mummy hakuri wallhy bazan iya sakinta ba, mummy tace wallhy sai ka saketa tunda ni na aura maka ita dama, yau babu abinda zaisa ta kara kwana da aurenka a kanta, Nurain ya kalli mummy yace mummy kiyi hakuri muji meye nufinshi na kin sakinta tunda baya sonta, da sauri sadeeq yace ni bance bana sonta ba dan Allah daddy ka fadama mummy haramcin tursasa saki, anty amarya ta mike tayi daki rai a bace saboda yadda taga alamun sadeeq yana mutuwar son yarinyar nan, masifa mummy ta shiga yi ma sadeeq kamar zata dakeshi sannan tace wallhy ya biyota da takaddar har daki in baso yakeyi ta sa wando daya dashi ba, ta mike ta daga zulfah dake kuka sosai suka kama hanyar daki, tsayawa mummy tayi da taga yadda zulfah ke tafiya, ta janyota da sauri suka shiga daki, gefen gado ta zaunar ita tace fada min abinda abba yayi miki, zulfah ta kara fashewa da kuka ta kasa yi ma mummy magana, zama mummy tayi kusa da ita tayi tagumi tana kallon bango, hankalin zulfah ya tashi sosai ta tsuguna a kasa tace wallhy tallahy mummy shi ya daukeni da kanshi ya kaini gidanshi ya..... ya.... ta kasa karasawa tana kuka sosai, mummy tayi murmushi ta dagota ta rungumota tace kwantar da hankalinki ki daina kuka, zulfah ta hadiye kukanta tana share hawayenta, mummy ta kalleta tace kina son abba? Zulfa ta sunkuyar da kanta idonta taff da kwalla a zuciyarta tace so na hakika wanda na boyeshi acan cikin zuciyata na danneshi da tunanin kiyayyar da yayi min, mummy ta kara dago kanta tace kar ki cuci kanki zulfah ki fada min wallhy in baki sonshi dole in kwato miki yancinki ki auri wanda kikeso, zulfah ta kara sunkuyar da kanta ya za'ayi tace bata son dan mummy matar da ko rayuwarta ta bukata zata iya bata inda hali, ta yaya bakinta zai iya furta ki ga jinin baiwar Allahr da ta maida ita cikakkiyar mace mai yanci, ay ko bata son sadeeq bazata iya kin zama dashi ba, bare tana matukar kaunarshi tun bata san kamanninshi ba ma, mummy tayi murmushin jin dadi tace nagode zulfah kin gama min komai shurunki amsa ce mai girma a gareni wallhy bani da kamarku ke da laila dan daya kuke da yayan da na haifa, nagode sosa-- zulfah ta katseta tace mummy ni ya kamata inyi miki godiya, bani da wata uwa a duk duniya da ta wuce ke, kin daukoni gidanki kin bani komai na rayuwa kin sa nasan abubuwa da yawa kin yi min abinda babu wanda zai iya min shi a rayuwata, babu abinda zan iya biyanki dashi,, mummy tace kin gama biyana tunda kika jure komai saboda ni, Allah yayi miki albarka tashi ki shiga bayi kiyi wanka, ta mike tana tafiya da kyar mummy ta fito mata da magunguna tana mai jin dadi cikin zuciyarta ta dinga adduar dorewar farin cikin nan na har abada,, Parlon ta koma ta zauna ta kalli sadeeq da idonshi yayi ja daddy da nurain suna mishi fada tace duk fadan da kuke mishi na banza ne dan kunnen abba na kashi ne, so yakeyi mu bashi ita yanzu ya wulakanta ta in ya samu wata saboda har yanzu baisan me yake so ba, baima san me kalmar so take nufi ba, ya dago kai kamar maraya yace wallhy mummy ina sonta na rantse da Allah mummy gaskiya na fada miki, tace to ita bata sonka kaje can ka karasa tsufanka da matarka, nurain yayi dariya yana kallon mummy yace mummy dan Allah ki bashi dama kadan in bai canza ba sai ki dau mataki, mummy tace to shi hilal din fa da yake sonta tuntuni, sadeeq cikin daga murya yace karya yakeyi mummy wallhy na fishi sonta, farouk ya kwashe da dariya harda tsugunawa kasa, ran sadeeq ya baci ya dauki remote ya wurgo mishi mummy ta danne dariyarta tace karka illata min ďa, haka kawai zaka hanashi dariya, sadeeq kamar zaiyi kuka yace to ni sa'anshi ne, daddy yayi dariya yace kai ba sa'anshi bane babana, ya kalli farouk yace fita ka bamu guri ana maganar manya ka wani zo kana mishi dariya, farouk ya mike ya fita yana dariya sosai, daddy ya kalli mummy yace ya isheki haka Aisha, ki daina susuta min uba dan ma kinga yanzu yana sonta shine kike neman ki haukatar min dashi, to ko ki janye wannan maganar taki ko kuma muyi fushi mu nemi wata ko babana, sadeeq ya girgiza kanshi kamar karamin yaro yace ni ita nake so daddy, mummy tace to ita kuma bata sonka kayi hakuri kawai ka nemi wata, yace wallhy tana sona, ni nasan tana sona, mummy tace to tunda tana sonka sai muga yadda zaku zauna tare, nurain tashi ka wuce gurin iyalinka kaji, ya mike ya wuce yana dariyar dramar mummy da sadeeq, ta kalli sadeeq tace tashi kaje gida kaima ka huta ko, yayi narai2 da ido yace haba mummy wai yanzu kin daina sona ne, tace soyayyar ce tasa na ke son rabaka da abinda baka so, KWAILAH ce fa kai kuma ay sai HIGH CLASS BEB ko, ya kalleta yace ki yi hakuri Allah ma muna mishi laifi fa mummy, tace ni ay ba laifi kayi min ba, daddy yace dan Allah ki kyaleshi haka yaje ya huta ay kin bashi wahala ya isa haka tunda kin rama, tace ay ban yi mishi komai ba ma,, sadeeq yace wannan ay yafi komai mummy wallhy kadan ya rage in samu "strk" tayi dariya sosai tace to naji tashi kaje, yace to mummy.... ammm... menene kuma ta fadi tana harararshi ya sosa kanshi yace ta.... taz.. babu inda zata ko zan baka ita sa nan da wata daya in naga yanayinka kuma na gasgata gaskiyarka, ya mike dan kar ya harzuka ta duk da ba haka yaso ba yace to Allah ya kaimu tace ameen.... Mrs tijjani shattima... : ◆◆ ZULFAH ◆◆ 5⃣1⃣ By Aysha Ya'u Kurah Sai kai kawo anty amarya takeyi a tsakar parlonta, hankalinta in yayi dubu to ya tashi, tana kallon wayarta dake faman ruri taki dagawa, ya akayi abba ya fara son yarinyar nan, lallai sanah ta cika yar iska da har tayi sake hakan ta faru, zama tayi tana huci kamar zaki ta dau wayarta taga kusan 10msd calls kuma duk na sanah ne, tsaki tayi tayi dialing numbr maman sanah, sau uku tana kira ba"a daga ba a na hudun ne ta daga murya can kasa tace ina meeting ne "deee" in na fito zan kiraki, anty amarya tayi tsaki tace at dis tym ake meeting, me zaisa ďan da ka haifa ma ka bashi tarbiyya kai kanka baka da lokacin kanka, tayi tsaki bayan ta yar da wayar ta dinga sambatun maganganunta ita kadai ta kasa samo mafita, meyasa sanah zata yi mata haka, meyasa? Wayarta ta shiga ringing ta duba tym taga afta 11 ta girgiza kanta ta dauka maman sanah tace dee ya akayi ne, yanxu na dawo gida wallhy duk na gaji, anty amarya tace baki gaji ba yanzu ne zaki gaji in kikaji abinda zan fada miki, maman sanah cikin firgici tace meya faru? Anty amarya tace komai ma ya faru, ta bata labarin duk abinda yake faruwa a gidan sanah, sannan ta cigaba da fada mata irin son da ta gani na zulfah a idanun sadeeq, maman sanah ta zame dankwalin kanta ta ya mutsa kitson attch din dake kanta cikin tashin hankali tace kina nufin sanah bata canza halinta ba, anty amarya cikin fushi tace ay kinji abinda nace yanzu mafita kawai zaki kawo meye mafita, maman sanah ta furzar da iska mai zafi a bakinta tace ay ni hadiza bansan me zance miki ba, gaba daya ji nake kamar zuciyata zata buga, anty amarya tace xata ay lokacin da yarki ta zama bora, lokacin da zata dinga ganin yaran sadeeq amma ba ita ta haifesu ba, ni ban taba ganin kaxamar karya irin sanah ba a rayuwata, maman sanah ranta ya kara baci sosai tace dakata hadiza yar tawa ce karya, anty amarya tace wallhy tama fi karya, in ba isk-- ya isheki maman sanah ta katseta da karfi, da wanne zanji da halin da sanah take ciki ko da cin mutuncin da kike min yanzu, ko mutuwa tana jin kunyar mahaifi a kunne na kike zagin yata da karya saboda baki san dadinsu ba ke kin gama watsar da naki a titi ko, in sanah karya ce ke kuma kare ko kuma me zan kiraki, sannu gwano wacce bata jin warin jikinta sai na wani, in kin manta bari in tuna miki, halinki sanah ta dakko na bin mazan da ba nasu ba, ko kin dauka bansan har yanzu kina pipn idan hasheem yayi tafiya ba, to wallhy ki fita idona in rufe kuma wallhy kinji na rantse da Allah kika kuskura wata matsala ta gifta tsakanin auren sanah da sadeeq ki tabbatar naki kema zai samu matsala, gara ku hada hannu ke da ita ku sama ma kanku mafita, tunda ta fara masifa anty amarya ke kuka kamar ranta zai fita saboda takaicin kalaman yar uwarta, saida maman sanah tayi masifa mai isarta sannan ta kashe wayar ta bar anty amarya na shashshekar kuka, Washe gari karfe 11 aka daura auren Jalila da Ishaq, hidima ake tayi babu kakkautawa a cikin gidan, ko ina ka xaga mata ne zaka gani masu ji da kansu saboda naira ta zauna a gurinsu, daga can ciki kuma zulfa'u ce kwance a dakin farouk saboda nan ne babu mutane, jalila na gefenta ana mata makup, zabba'u ta kara taba kan zulfah tace ohh wannan zazzabin xai kwafsa mana sai yau zai wani tashi ya hana mana sukuni kuma yaki sauka kamar yazo gidan ubanshi, jalila tayi dariya tace ay ko ya sauka ko kar ya sauka yau bani barin garin nan sai da "Z-square," zabba'u tayi dariya tace sunan da kika rada mana kenan, tayi tsaki tace nima da sunana da z ya fara da kinga shikenan sai komai ya tafi dai2, zabba'u tace ay bai baci ba baby rago kadai zaki siyo sai a yanka miki da sunan '"Zankaďaziyya", duk suka kwashe da dariya meenah me makup tace ay kuwa sunan ya dace dake, zulfah dai na kwance tana murmushi tana kallonsu, ciwon da jikinta da kanta ke mata shi yafi komai damunta, wayar jalila aka kira ta dauka tace yaya abba gud a.m, yace morning amarya ya kuke, tace fyn, yace good, ya rage muryarshi yace kina kusa da zulfa'u ne, tace eh, yace plss sa mata wayar a kunnenta inji muryarta, tayi murmushi tace to, ta sa ma zulfah wayar a kunne ta rike tana kallonta, runtse idonta tayi da taji muryarshi a cikin kunnenta, magana yake mata a hankali kamar baison yi har ya gama bata ce mishi komai ba, jalila ta cire hannunta ta mayar da wayar kunnenta tace yaya abba hannuna, yace jalila bata min magana ba, jalila tace wallhy bata da lafiya ne yaya a dukunkune ma take tun jiya, yace subhanallah me ya sameta, cikin wasa tace zazzabin rabuwa dani mana, yace bansan shirme dan Allah ki tasheta tasha magani yanzuu, tace okk baka da matsala, yace gidan duk a cike yake ko hayaniya ma ay zai sa mata ciwon kai dan Allah kuyi sauri a daukeki a kaiki gidanki mu huta, tayi dariya tace ay tare zamu tafi da ita sai tayi min shekara daya sannan zata dawo, yace shekara 1 ay yayi kadan why not tayi spndn rayuwarta a gidanki har ki tsufa, jalila ta yar da wayar tana dariya sosai kamar tababbiya.... Mrs tijjani shattima.... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 5⃣2⃣ By Aysha Ya'u Kurah Wasa wasa saida zulfa'u tayi sati daya tana ciwo tasha allurai da magunguna, kullum sadeeq yana tafe zuwa duba ta mummy sam bata barinshi ya ganta ko ya ganta saidai daga nesa, a bangaren sanah kuwa tunda tayi haukanta a wannan daren sadeeq bai kulata ba shikenan itama ta daina kulashi ko hanyar dakinshi bata bi saidai in yana parlor tayi shigar da a tunaninta zai ďaga mishi hankali tayi ta karkaďa jikinta dan in yazo ta samu damar wulakanta shi, tsaki yakeyi ya kauda kanshi saboda ko kadan sanah bata bashi sha'awa, sam baijin dadin tarayya da ita, a kullum in ya tuna tarayyarshi da zulfa'u sai yayi ta murmushi shi kadai wani lokacin ma daurewa yakeyi da tsananin da mummy tayi mishi akanta saboda shi kadai yasan dadďar zumar da ya lasa a jikinta... Yana zaune a dakinshi da daddare yana duba wasu aiyuka, yayi kusan 1hr yana dubawa ga yunwa ta addabeshi, tsaki yayi a hankali ya mike ya kashe lptp din ya fito zai shiga kitchen ya hada tea, zaune ya samu sanah ita da kawarta beeba suna hira suna shewa, beeba na ganinshi ta tsuguna har kasa ta gaishe shi ya amsa mata ciki2 ya wuce, sanah taja tsaki tace dan wulaknci, ke kika ma gaida shi wallhy ni bai isheni kallo ba, beeba ta dan bugeta kadan tace ke wawiya ce, da dabara ake cin ribar zama da mutane, ta matso kusa da kunnenta ta raďa mata wasu maganganu sanah ta watse da dariya suka tafa, beeba ta mike ta dauki jakarta tace maza ki tashi kije inji feedbc a waya komin dare kinji, Sanah tace karki damu kawas ta mike tana karairaya ta karasa kitchen din, yana tsaye ya gama hada tea zai dauka sanah tayi wuff ta dauke, ta marairaice fuska tace haba dear wai laifin me nayi maka ne duk kabi ka canza min, ta shige jikinshi tace nice fa sanarka wacce take tsananin kaunarka, ya matsar da ita a jikinshi ya murtuke fuska yace miko min tea dinnan ki bace a gabana, ta kara shigewa jikinshi tana kuka kasa2 tana magana kamar marainiya, wa'azin karya ta shiga yi mishi akan yaji tsoron Allah ya dinga sauke hakkinta akanshi wa'azi sosai take mishi wanda itama zuwar mata yayi a baki saboda ta samu biyan bukatunta, jikinshi yayi sanyi kadan dan yasan gaskiya ta fada shi rabon da su hada shimfida da sanah har ya manta, kuma yasan baya kula da duk wasu needs dinta, share mata hawaye ya shiga yi yana bata hakuri ya jata suka wuce daki shima ya shiga yi mata nasiha akan abubuwan da takeyi marasa kyau, narkewa tayi a jikinshi tana bashi hakuri kamar da gaske, nan ta shiga aika mishi da salonta dake rikita maza, sun lula can wata duniya idon sadeeq babu abinda yake hange da wuce zulfah gani yakeyi kamar tare suke tarayya da ita a wannan daren, ina ma ita ke mishi irin wadannan abubuwan da sanah ke mishi abin da ya dinga aiyyanawa a cikin ranshi kenan, saida ta gamsu dan kanta sannan suka mike suka shiga wanka tare,, ta riga shi fitowa ta zauna a bakin gado tayi tagumi, yana fitowa ya zauna kusa da ita yace meya faru kuma, ta kwanto da kanshi jikinta tace waalhy dazu na samu waya wai momy na bata da lafiya shine nake jin tsoron tambayarka ko zaka barni inje, ya salam ya fadi cikin damuwa yace ciwo ay ya wuce komai gobe ki shirya da wuri muje mu dubata, gabanta ya fadi amma sai ta dake tace a'a bari dai In fara zuwa saboda naji ance india za'a fitar da ita goben, kuma kaga dole ni zanyi jinyarta a can din, yace hakane to Allah ya bata lafiya ya kuma kaimu goben, ameen ta fadi hade da rungumeshi tace tnk u so much swthrt, yayi murmushi ya mike yana karasa goge jikinshi, dakinta ta wuce ta kira beeba tace ya faďa beeba, wallhy komai ya daidaita kawata, gaskiya samun kawaye irinki sai an tona, beeba tace yauwa ko kefa yanzu kinga zakije ki sheke ayarki babu wanda ya sani, sanah tace hakene kawata, bari in kirah Mukhtar in fada mishi ina tafe gobe yayi min shiri na musamman, beeba tace ay kema kinsan a shirye yake tunda har ya matsu kuje yawon bude ido kinsan kasashe hudu yace zaku, tace yeyyy ai zamu hole kawata ke dai Allah ya saka miki, tace ameen suka cigaba da hirarsu ta karuwan mata masu neman mazan mutane, Allah ka tsare mana mazajenmu "ameem thumma Ameen" .... Mrs tijjani shattima... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 5⃣3⃣ By Aysha Ya'u Kurah Kwance take safiyar asabar a daki ta dukunkuna cikin bargo saboda sanyin da akeyi, waya ta gama yi da jalila ta ajiye wayar tana lumlumshe ido ko zata koma bacci, tun daga parlor yake sallama shuru babu wanda ya amsa ya hau sama ya murda dakin mummy ya ganta kwance tana bacci, a hankali ya janyo kofar ya wuce dakin zulfa'u cikin farin cikin samun damar ganinta, a hankali ya murda kofar ya mayar ya rufe, karasawa yayi ya zauna gefen gadon ya bude fuskarta dake cikin bargon, bude idonta tayi da sauri suka hada ido, ta runtsesu sosai tana jan bargon dan ta kara rufe fuskarta, rike bargon yayi sosai yana dariya yace ki saki bargon nan ko in cireshi gaba daya, ta maza ta saki bargon ta rufe fuskarta da hannunta, kwanto da kanshi yayi dai2 fuskarta yasa hannunshi yana shafar yatsun hannunta, ciresu tayi da sauri zata juya kanta cikin pillow, da sauri ya tallabo habarta da hannunshi, ta kara runtse idonta jikinta na rawa ta ko ina, a hankali yayi mata peck a kuncinta yace bude idonki ki kalleni, um um ta fadi kamar me shirin yin kuka, ya daura bakinshi kan nata ta kauda kanta da sauri ta bude idonta, yayi mumushi yana kallon cikin kwayar idonta daga ganinta a tsorace take a hankali yace baki iya gaisuwa ba ko? Ta girgiza kanta tace ina kwana, ya kama kunnenta yace bazan amsa ba tunda saida na roka, ta noke gefen fuskarta kan hannunshi saboda yadda yake mata waiwayi a kunnenta cikin rawar murya tace dan Allah ka daina, yace to daga min hannuna sai in daina, ta juya da fuskarta cikin muryar shagwaba tace to ka tashi, ya kara matsowa sosai yana shafar fuskarta, hawayen tsoro suka shiga tsere a fuskarta, a kasalance yace wannan hawayen dama nakeson gani, ya fara lashesu a hankali, ta bude baki zatayi magana ya hanata yin maganar da bakinshi saida ya dan rage ma kanshi wahalar da yakesha akan tunaninta sannan ya kyaleta, ta juyar da kanta tana kuka tana tsoron ya sake bata wahalar da bata rannan, kamar ya karanto abinda ke zuciyarta yace ki daina jin tsoro babyna babu abinda zan miki rannan ma tsautsayi ne, ta ji dadi sosai ta dan share hawayen fuskarta, a hankali yace ya kamata ki saki jikinki dani ki cire kunya ki nuna min tsantsar son da kike mini, ta juyo fuskarta da sauri suka hada ido, ya kashe mata ido yace ko bakya sona, ta turo baki ta juyar da kanta gefe, yayi dariya yana jan bargon jikinta yace nasan kina sona in ma bakya sona zan gane yanzu in har baki fada min da bakinki ba, tayi shuru kirjinta na bugawa da sauri2, yace baxaki fada ba kenan, to bari in tambayi zuciyarki, ya fara yaye bargon ta rike da sauri saboda nyt gown din dake jikinta, tace na hadaka da Allah ka tashi ka tafi, yayi murmushi yana kallon hannunta yace in kinga na fita a dakin nan to naji labarin da ke cikin zuciyarki, tace wayyo Allah na, dan Allah to ka bari in fada maka da bakina, ya girgiza kanshi yace bana so nafison inji a gurin da baza'a min karya ba, ta kara cukuikuiye bargon tace nima bazan yi maka karya ba wallahy, ya karkatar da kanshi gefe yace ni kuma bana son jin ta bakinki, ya fara jan bargon? tana ja itama tana rokonshi tana kuka, sakin bargon yayi yana murmushi yace oyaa ina jinki zo ki fada min a kunne, ta marairaice tace me zan fada maka, yace ohhh tambayata ma kikeyi ko, ya rike bargo tayi yar kara tace na tuna zan fada, yace matso da sauri ki fada min yadda kike sona, ta kai bakinta kunnenshi ta runtse idonta, a hankali tace I love u saboda ka matsa min in fada, ya kauda kanshi yace auuu ni ma na matsa miki ko? Ta riko hannunshi tace um umm kayi hakuri, yace to kara fada min kina kallon cikin idona, ta girgiza kanta ta runtse idonta tace I love u, ya rungumeta sosai yace luv u more more more baby , dan Allah ki saki jikinki dani ki manta da komai da ya faru a baya mu gina rayuwarmu cikin farin ciki kinji, ta daga mishi kanta a zuciyarta tana jin dadi da godewa Allah da ya bata wanda take matukar so kuma shima yake sonta, saida ya dade rungume da ita shima zuciyarshi tayi fari kal saboda kasancewar shi da abin kaunarshi,! (To Allah yasa farin cikin na wadannan masoyan ya daure ameen) cikin yan kwanaki kadan ta saba da mijinta har ya zamana in bata ganshi ba ko bata ji muryarshi ba bata jindadi ko kadan, mummy na hankalce dasu haka anty lailah dan kullum in yana gari suna tare a dakinta, wannan abu yayi ma su mummy dadi saboda dama abinda take jira kenan taga sun daidaita kansu,, Daddy zaune a hotel din da ya sauka a England wani doctor na kanshi yana mishi aune2 saboda baya jin dadi tun zuwanshi, magunguna ya bashi suka yi sallama daddy ya rakashi har waje ya juyo dan komawa daki idonshi na mishi nauyi sosai, hayaniya yaji a dakin kusa dashi harda ihu da kuka kuma muryar hausawa ce, ya bude kofar ya shiga, wani saurayi ne tsaye rike da wani saurayin ya shake mishi wuya daddy yayi saurin rabasu dayan saurayin ya rarumi kayanshi ya fita da gudu yana haki, shi kuma dayan ya koma kan yarinyar dake duke tana kuka daga ita sai towel, zai fara dukanta daddy ya rikeshi yace kayi hakuri samari mata rauni garesu karka duketa ka lallabata har ku koma gida babu mamaki ma akwai ya'ya a tsakaninku, kaga bazai yi kyau ba ace ka duki uwar ya'yanka, yaron tofar da miyau yace Allah ya kyauta wannan karyar ta xama matata, macen da duk namijin da ta gani burinta ta kwanta dashi , inaga alhakin mijinta ne ma ya kamani saboda da mijinta tayi mishi karya ta biyoni wata kasa, shine yau daya dan naje wasu ayyuka ta kasa hakuri ta nemo wani dan ya biya mata bukatunta, tirrr da halinki, daddy ya girgiza kai cikin kyama da tausayin mijin yarinyar, yace yarinya kiji tsoron Allah, ta dago kanta cikin masifa tace dakata mal-- muryarta ta makale saboda ganin daddy da tayi, daddy yaja da baya da sauri jiri na dibanshi yace s..a..n..ah, ta juya bayanta da sauri jikinta na rawa tace yau na shiga uku, taro daddy saurayin yayi dan ya kusa kaiwa kasa saboda tashin hankali, yace baba kasanta ne, sanah ta tattara yan komatsan kayanta da jakarta dake cike da kudi ta fita da sauri tana kuka, daddy yace ma saurayin matar ďana ce, innalillahi wa inna ilaihir rajiun, abinda saurayin ke fadi kenan ya rike daddy yace dan Allah kayi hakuri, daddy yace ba laifinka bane yaro sai dai zan baka shawara kaji tsoron Allah, ka tuna da ranar karshe, ranar da babu wata sauran nadama, ranar da kana gani ranka zai fita daga jikinka ba tare da ka tuba ba, jikin saurayin da ya kira kanshi da mukhtar ya mutu sosai, yana hawaye yana bawa daddy hakuri, daddy yayi mishi nasiha sosai sannan ya kaishi dakinshi ya kwantar dashi, kuka daddy yakeyi jikinshi na rawa ta ko ina, ya daga waya ya kira tawagar da suka taho tare yace su shirya tafiya yau in shaa Allah, sannan ya kira sadeeq, sadeeq ya dauka ya gaida daddy yace ya jikinka, daddy yace da sauki abbana, ina matarka, ya shafo kan zulfa'u dake kwance a jikinshi yace gata nan daddy tana gaisheka, daddy yace dayar fa, sadeeq yayi jimm yana tsoron kar daddy yayi mishi fadan rashin zuwa duba mahaifiyarta, yace daddy tana india tana jinya mamanta bata da lafiya, jikin daddy ya mutu sosai yaga bazai iya fadama danshi abinda ke faruwa a waya ba, yace to Allah ya kara sauki, sadeeq yace ameen daddy sukayi sallama suka kashe wayoyin, daddy wani irin yanayi ya dinga ji a jikinshi gaba daya tun daga kan jininshi har gabobinshi duk sun saki, a zuciyarshi yace ya Allah ko bayan raina ka fitar da gurbatattu daga cikin zuriata kuma karka bawa wani gurbatatacce daman shiga cikinsu... ""Ameen daddy amma da ka fada ma sadeeq dan rashin fadar da wuri bamusan me zai haifar ba, tabbas akwai wanda zai shiga gaggarumar matsala a gidanka saboda rashin fadin da bakayi ba da wuri""' Mrs tijjani shattima.... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 5⃣4⃣ By Aysha Ya'u Kurah Sanah airport ta nufa da sauri tana kuka ta kira beeba ta fada mata duk abinda ke faruwa, beeba tayi salati tace yau mun shiga uku yanzu ya zakiyi sanah, sanah cikin kuka tace ko ma meye zanyi dan inga daddy bai fadawa sadeeq ba, koda kuwa kasheshi zanyi wallhy, dan da in rabu da sadeeq gara in mutu, beeba ta harari bango a zuciyarta tace kinsan kina sonshi kike bin mazan banza, amma a wayar ce mata tayi kiyi sauri ki taho mu san abin yi kafin ya dawo, sanah tace yanzu kuwa dan ina airport, kuma karki bari kowa yasan ina gari ma, beeba tace trust me dear, suka gama hada plans dinsu suka kashe wayar sai a sannan sanah ta samu nutsuwa, karfe biyu na rana jirginsu ya sauka a abuja da hanzari ta dauki drop ta fada ma beeba ta iso, beeba tace to sai kin karaso sanah, a motar ta dinga sake sake , can ta dauki waya ta kira anty amarya, ta dauka suka gaisa anty amarya tace kwana biyu kina garin nan kuwa, sanah tace wallhy naje dubai sarin kaya anty, anty amarya tace manya to yaushe zaki dawo, tace inaga jibi, da England ma naso zuwa, anty amarya tace aiko da kinje can dan daddy ma na can da ya cika miki jakarki da kudi, sanah tace gaskiya nayi missn ko dai zan wuce can ne, anty amarya tace kin makaro yarinya ya riga ya taso inaga magriba ma a gida zaiyi ta, sanah tayi murmushi cikin faduwar gaba tace kice yanzu ana can an hada mishi delicious, Anty amarya tayi tsaki tace inaa ay bani bace da girki nasan yanzu wannan bazan yarinyar tana can tana iyayin girki a kitchen dan yaya da laila ma suna biki sai dare zasu dawo, nima fita zanyi ita kadai zamu bari a gida tayita iyayinta shegiyar, sanah cikin farin cikin ta samo satar amsah ta taya anty amarya tsine ma zulfa'u dake can tana kici kicin faranta ran uban mijinta da daddan girkinta, saida suka dade sannan suka kashe wayar, karfe uku da rabi ta shigo kaduna ta wuce ta dakko beeba da tayi mata guzurin muguwar gubar dake gurbata ya'yan hanji, sunata plans dinsu a mota kasa2 suna dariya babu imani a zuciyarsu, dan a ganin sanah zata jefi tsunsu biyu da dutse daya, suna karasawa suka biya dan texi din sanah tasa nikab din da beeba ta dakko mata suka shiga ciki, masu gadi suka tambayesu inda zasu beeba tace nazo gurin aminyata ne sunanta zulfah, suka ce to ku shiga, suka wuce ciki suna murmushi, zulfah na daki tana shiryawa dan a yau ne mummy tayi ma sadeeq alkawarin zata bashi matarshi saboda farin cikin gano boyayyen karamin cikin dake jikin zulfah wanda babu wanda ya sani sai ita, buruntu taji a gurin dining ta fito da sauri taga bata ga kowa, ta deko ta windo ta hango fuskar beeba, ta daga kafadarta ta juya tace may be gurin anty amarya tazo dan ta taba ganinsu tare da sanah, ta dauki wayarta dake gurin dining ta koma daki ta cigaba da shirinta... Karfe takwas da yan mintina daddy ya shigo gidan, mummy ta fito ta taryeshi cikin farin ciki ta karbi jakar hannunshi tace muje a ci abinci sai ayi wanka ko, ya zauna bai ce mata komai ba, cikin damuwa ta zauna kusa dashi tace yallabai me yake damunka ko jikin ne, ya girgiza kanshi yace damuwata Aisha tafi karfin ciwo, ina cikin matsananciyar damuwar da idan kuka ji ta ku kanku sai kun shiga cikin damuwar da tafi tawa, tace subhanallahi wace irin damuwa ce wannan? Yace damuwar matar abba, wacce daga ciki mummy ta fadi cikin kagauta, yace kedai kawo min abinci inci sai muyi magana, ta je dining ta kwaso mishi abincin, babu abinda ya iya ci a abincin sai kunun gyada, gaba daya kunun ya shanye sannan ya mike yace zaiyi wanka tukunna sai ta kira kowa yazo a zauna ayi magana,, mummy dai cikin zulumi daddy ya barta saboda taso ya fada mata wacce a ciki matan abba, ta zauna tayi jimm tana jiran fitowarshi, mummy taga awa daya ta gota daddy bai fito ba, ta mike tace yau inaga canza fata kakeson yi ko, wannan irin dade---- maganar ta makale a makoshinta saboda ganin daddy da tayi kwance bakinshi duk kumfa, karasawa kusa dashi tayi da sauri tana salati, ta shiga girgizashi babu alamar motsi, da sauri ta fito tana kuka tayi dakin nurain, Nurain yana ganinta cikin wannan yanayin ya mike dan yasan ba lafiya, tace nurain fito muje ka gani tana magana kamar tababbiya nurain yabi bayanta laila ma ta fito da gudu tabi bayansu, ihu nurain yayi shima hade da salati ya shiga girgiza daddy, ya dago kai yana kuka yace shikenan mummy daddy babu, ya kwanta jikinshi yanata gunjin kuka kamar karamin yaro, laila kuwa zama tayi dabas a bayin tana kuka sosai ta kalli mummy wacce take kamar a sankare ta kasa yin komai saboda shock, sun kusa minti talatin a haka kafin nurain yayi ta maza ya tallabo daddy da kyar ya fito dashi daga bayin... Sadeeq kwance a side dinshi na gidan da aka gyareshi tun satin da wuce, rungume yake da zulfa'u bayan sun idar da sallar godiya ga Allah, yanata mata hira cikin so da kulawa suna aikawa juna sakonni, gaba daya ta cire kunya a wannan lokacin tana mishi duk abinda yakeso amma zuciyarta na tsoron abin da yayi mata a ranarsu ta farko, cikin kasala ya matseta jikinshi ya dinga rada mata kalamai a kunne cikin so da kauna, yanata nusar da ita akan bazata ji zafi ba dan Allah ta bashi hadin kai su raya sunnar manzon Allah s.a.w, cikin hikima ya lallabata har ta yarda suka shiga faranta ran junansu, iya ficcewar hayyaci sadeeq yayi dan gaba daya bai san duniya da yake ciki ba, yana gab da shiga "koramar zuma" yaji bugun kofar parlonsu babu kakkautawa, tsaki yaja ya mike jikinshi a mace yasa kaya ya fita da sauri dan har lokacin ba'a bar bugun kofar ba, yana budewa yaga nurain idonshi jawur, a firgice yace yaya nurain lafiya me ya faru, nurain cikin muryar kuka yace ka biyo ni muje, sadeeq gabanshi na faduwa yabi bayanshi a tsakar parlor ya hango daddy kwance babu rai, mummy da anty amarya na gefenshi suna kuka, sadeeq ya karasa da sauri yace me ya sameshi, ya fara girgizashi yana kuka yace ka tashi daddy, dan Allah ka tashi karka tafi ka barmu, me yasameshi ku fada min dan Allah, anty amarya cikin kuka tace wannan kumfar ta bakinshi ta guba ce wallhy guba aka bashi yaci dan ya mutu, gaban mummy ya fadi ta sauko dan bata kawo guba a ranta ba, taba kumfar tayi taji tana yauki ta fashe da kuka tace waye ya gaji da rayuwarka ya baka guba, wanene ya cuci rayuka da yawa ssboda bukatar kanshi, ta dinga magana kamar zautacciya, anty amarya ta dago kanta ta hango zulfah dake tahowa cikin hijab da sauri, itama ta fito jin abinda ke faruwa ne saboda dadewar da mijinta yayi, harararta tayi ta kauda kai tace koma wanene ya zuba maka guba wallhy bazamu kyaleshi ba sai mun dauki fansa a kan mutuwarka tana magana tana kuka, zulfah ta shigo ciki da sauri ta zauna gefen mummy tace mummy lafiya, mummy ta rungumeta tace an kashe shi zulfah an kasheshi, bansan me yayi ba aka kashe shi, bansan wace irin tsana bace tsakaninshi da wanda ya kashe shi, zulfa ta fashe da kuka ta toshe bakinta da hijab dinta tana kallon daddy a tsorace, a daren akayi mishi wanka aka suturce shi yayi kwanan keso.. duk iyalan gidan suna kewaye dashi suna mishi addua da kuka sosai..... Mrs tijjani shattima... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 5⃣5⃣ By Aysha Ya'u Kurah Washe gari tun safe police da manyan sojoji suka kewaye gawar chief of air staff, bincike sosai akeyi akan gawarshi inda aka tabbatar da guba ce yaci ta mai saurin illata yayan hanji,, cikin kwarewa manyan yansanda suka fara aiwatar da bincikensu tun daga kan wadanda sukayi tafiya tare da irin abincin da yaci a hanya, har kawo cikin gidanshi inda kowa ke zaune cikin tsananin tashin hankali, ta kan mummy aka fara, tambayoyi wani police yake mata cikin muryar kuka take bashi amsa, tace tunda ya shigo dama ranshi a bace yake yace zai fada min damuwarshi, kuma damuwar tashi akan matar dana ne gashi can abba, amma bai fada min wacce aciki ba, kunu kadai yasha ya shiga wanka shine na iske shi a kwance babu rai, police din yace hajiya an duba ingancin kunun kuma an tabbatar da tsaftarshi kafin a bashi, tace kwarai kuwa dan matar dana keyi mishi kunu yama fi son kununta fiye da na kowa a cikin gidan nan, police din yace ko zamu iya samun flask din da aka zuba kunun in ba"a wanke ba, tace kwarai kuwa zulfa je ki dakko, zulfah ta mike taje ta dakko ta kawo musu, ya bude flask din babu kunu a ciki sai dan kadan daya kwanta a can kasan flask din, dan sandan yayi mata godiya ya koma kan sauran duk yayi musu tambayoyi, duk suka amsa mishi, fita waje sukayi da flask din suna tunanin yin bincike akan ragowar kunun ciki tunda ance shi yasha karshe, daya ya basu shawarar su hada kunun da madara asamu mage a bata tasha in dai har wani abu ya samu magen to tabbas a kunun gubar take, haka kuwa sukayi suka wanko flask din da ruwa kadan suka dama madarar dashi, mage suka bawa tashanye tasss ko minti biyar ba'ayi ba magen ta fara shure2, cikin kankanin lokaci ta cika, police din sun tsorata matuka da ganin wannan alamarin, cikin minti kadan suka isa gidan, lokacin mutane sun cika makil ciki harda sanah da tayi ikirarin dawowarta kasar kenan, police din na shigowa parlon suka bukaci ganin mummy, mummy ta tashi ta bisu karamin parlon yara, nan suka fada mata komai game da kunun sannan suka bukaci ganin wacce ta dama shi, mummy ta fara kuka tana girgixa kai tace wallhy zulfau bazata kasheshi ba, kudai sake bincikowa, saboda me zaki ce bazata kasheshi ba, haihuwarta yayi ko rainonta muryar anty amarya sukaji tana karasowa cikin parlon ay ni biri yayi kama da mutum dama tun ganin gubar nan nasan wallhy itace zata kasheshi ta fashe da kuka tace dama saida ya fada yace kin shigo mishi da matsala cikin gida gashi ta kasheshi kowa ya huta, mummy jikinta ya fara rawa tace wallhy inspector zulfa bazata iya kisan kai ba, inspectorn yace hajiya bincike ne zai fadi koma zata iya ko baxata iya ba, kedai ki bamu hadin kai muyi mata tambayoyi, a statement dinki na dazu kince yace damuwarshi akan matar danshi ne abba ko, ta iya yiwuwa yanada wata boyayyar damuwa akanta, mummy tace ay ba ita kadai bace matar tashi, anty amarya tayi wuff tace ay sanah ba'a gidan nan take ba kuma bata ma kasar sanda abun ya faru, police din yace duk a tsayar da wannan cece kucen a kira mishi zulfa'un, mummy ta mike hawaye na bin idanunta ta kira zulfa'u da laila sannan tasa aka kira mata sadeeq da nurain a waje.. Zulfa'u zaune gaban police din dukka mutanen dake gurin sun tsura mata ido, police din yace malama zulfa'u ki fada mana gaskiya duk abinda kika fada shi zamuyi amfani dashi a gaban shari'a, cikin rawar murya tace to, yace kunun da kika dama jiya kin sha? Tace eh nasha, yace ke da waye a cikin gidan nan lokacin da kika gama aikin, tace ni kadai ce, kin duba ingancin ruwan da kika dama kunun dashi, kuma kin duba kullun babu wani abu da zai cutar a ciki, tace eh na duba,,, yace kinsan kunun da kika dama na dauke da guba a ciki, ta mike tsaye da sauri ta dafe kirji jikinta ko ina sai rawa yakeyi, tace wallhy tallahy bani bace na zuba, police din ya mike yace relaxx nasan bake bace kika zuba, babu mamaki wani ne yayi miki barazana akan zai kasheki in baki zuba ba ko? Ta rike cikinta dake murda mata tana girgixa kanta kamar zata fadi, sadeeq ya mike ya rungumeta da sauri yana bubbuga bayanta yace wace irin banzar tambaya kakeyi mata haka, ta kankame sadeeq tace wallhy ban zuba komai a ciki ba, wayyo Allahna na shiga uku, rarrashinta ya shiga yi yace nasan bazaki zuba komai a ciki ba u r innocent ki daina kuka, police din yace mr man ka barni inyi aikina, sadeeq cikin fushi yace ka gama yi mata tambayoyin da zasu dinga firgita ta, ka tashi ka tafi kawai bamu bukatar ka, anty amarya cikin tsawa tace wallhy bazai tafi ba sai ya gama bincike an gano azzalumin da ya kashe min miji, sadeeq ya harareta yace to sai ki zauna a bincike ki amma ni babu wanda ya isa ya cigaba da firgita min mata, nan hayaniya ta kaure tsakanin sadeeq da anty amarya, zulfah dai kara kankameshi tayi saboda tsabar tsoron da take ji dakyar nurain ya lafar da kurar da ta taso yace ma sadeeq ya barsu suyi duk abinda zasuyi gaskiya zata bayyana, sai da ya dade yana bata baki sannan suka zauna,, police din ya cigaba da magana, yace babu wanda ya shigo gidan lokacin da kika gama aikin,, gaban sanah dake zaune rai a bace saboda yadda sadeeq ya kankame zulfa ya fadi saboda beeba tace mata zulfah ta ganta, tayi saurin yi mata flashing, kafin zulfa'u ta bada amsa wayar dake hannunta tayi ringing, AMINIYATA ta gani kururu, ta shiga zare ido to wacece aminiyata abin da ta dinga tunani kenan, har wayar ta kusa tsinkewa sadeeq yayi answern yasa speaker saboda taji da kyau, dariya sosai akayi a wayar sannan akace aminiyata komai yayi dai2 ashe shine baki kirani kin fadamin aiki yayi ba, na miki text jiya da na koma gida kin gani, zulfah murya a sarke tace waye?, aka sake yin dariya sosai akace ohh na gane kina cikin mutane zan kiraki anjima nidai kar amanta dani in GADO ya shigo hannu, kafin zulfah ta sake magana har an kashe wayar, sadeeq cikin rudu ya kalli zulfah yana matsawa daga jikinta, innalillahi wa inna ilaihir rajiun shi suka dinga maimaitawa shida su mummy zulfah ta mike jikinta na rawa tace wallhy bansan ta ba, karar shigiwar text wayar yasata yin shuru, sadeeq ya bude text din da ya kara gigita shi, yayi scrolln na jiya ma, wurgi yayi da wayar ya mike tsaye da sauri yana ma zulfah kallon tsana sosai, police din ya dauki wayar ya bude text din farko kamar haka, (aminiya gani nan zuwa na samu gubar sharp sharp wanda ko minti biyar bazaiyi ba zai sheka barzahu, kinga daga nan sai musan yadda zamuyi da sadeeq in kin haifa mishi ya'ya shima a shekeshi gida ya zama naki dan naji kince baya bi takan tsinanniyar kishiyar nan taki itama nan gaba waje zamuyi da ita) sai text na biyu (Aminiya na gane kina cikin mutane,, ko'ina ka zaga yau mutuwar sirikinki kadai akeji gaskiya u are very smart da kikayi tunanin kasheshi kafin ya tona miki asiri, zuwa anjima ina nan zuwa) Faduwa kasa zulfah tayi sumammiya da ta gama jin maganganun dake cikin text din, yayin da duk mutanen gurin suka dauki salati...... Mrs tijjani shattima... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 5⃣6⃣ By Aysha Ya'u Kurah Babu wanda yaje kanta sai anty laila, kuka takeyi sosai tana girgixa ta tace mummy wallhy sharri akayi mata, wallhy zulfah bazata aikata wannan aikin ba, frmn dinta akayi, mummy dai banda kuka babu abinda takeyi haka nurain, sadeeq kuwa hanyar waje yayi kamar zararre hawaye sun kafe a idonshi, wani iri ya dinga ji a cikin zuciyarshi, meyasa zulfah zata kashe daddy, why why?? Ya fadi yana buga kanshi a bango, hilal ya taso da sauri ya rikeshi yace haba marafa ya zaka kashe kanka saboda mutuwar daddy, kayi tawakkali mana kasan duk mai rai fa mamaci ne, sadeeq ya tsuguna ya rike kanshi sosai yace hilal zulfah ce ta zuba ma daddy guba yaci ya mutu, hilal ya mike tsaye yana girgiza kanshi yace karyane, karyane wallhy, ya shiga cikin parlorn da sauri inda ake kokarin yayyafa ma zulfah ruwa dan ta tashi, gurin mummy ya tsuguna idonshi duk ya canja yace mummy kin zauna da yarinyar nan na tsawon lokaci, kinsan abinda zatayi da wanda bazatayi ba, wannan maganar daga jinta ansan shiryayya ce wallhy zulfah bazata iya kisan kai ba, anty amarya ta mike cike da masifa tace sannu sarkin shishshigi ga abu nan a zahiri mun gani kuma mun ji zaka zo kana neman kareta to kodai da kai ta hada baki ne in taci dukiyar ta gudu kuje kuyi aure, hilal ya daka mata tsawa cikin bacin rai zaiyi magana jalila ta shigo da gudu tana kuka ta rungume mummy, kukan jalila da hayaniyar da anty amarya sukeyi da hilal shi ya farfado da zulfah cikin firgici tace wallahy bani bace dan Allah mummy ku yarda dani, anty laila ta dagota ta karasa goga mata ruwan adduar dake kofi, zulfa tayi crolln ta karasa kusa da mummy ta dafata tace mummy ki yarda dani, wallhy tallahi bansan wacce ta kirani ba, wallhy babu wanda yazo nemana gidan nan ku tambayi masu gadi ma zasu fada muku, mummy dai kallonta kawai takeyi tana kuka jalila ta rungumeta tace nasan bazaki iya kisa ba zulfa, akwai dai wani abu boyayye a kasa, dan sandan ya mike da wayar zulfa a hannunshi ya kalli anty amarya dan itace ke bashi full attention dinta, yace hajiya bari muyi binciken mu na karshe sai musan abin yi, tace go on kuyi duk abinda kuka san ya dace, yace good yasa aka kira masu gadin, yayi musu tambayar shin akwai wani wanda yazo gidan nan jiya da misalin hudu da wani abu lokacin mutanen gidan basa nan, mai gadin yace ehh wasu mata su biyu sunzo daya ta rufe fuskarta da wani bakin abu, sunce mana sun zo gurin small madam, zulfah ta mike da sauri ta karasa gabansu tace ku fadi gaskiya, karkuyi min sharri da kudin zai kare ya barku da zunubi, dayan mai gadin yace I swear gaskiya muke fada dan basu dade a gidan ba ma suka tafi, zaman dirshan zulfah tayi a gurin gaba daya ta nemi kuka a idonta ta rasa, sai bin su mummy dake kuka takeyi da ido, ta runtse idonta tace ya Allah kai kadai ne shaidata akan wannan daurin zato da akayi min, Allah dan isarka da ikonka kafitar dani daga cikin halin da nake ciki da gaggawarka ba ta shaidan,. ameen anty laila tace tana sheshsheka, hilal ya tsuguna a gabanta yace tabbas wanda yayi miki wannan sharrin yayi nisa sosai cikin tsanarki, ki sa a ranki Allah zai fitar dake daga wannan musibar da kika shiga ko ba anan duniya ba zai wanke ki a lahira, yana kaiwa nan yafita yana share hawaye masu zafi.. Bayan yan sanda sun gama rubuce2 suka bukaci tafiya da zulfah station, sai a lokacin mummy ta mike tana kuka ta matso kusa da zulfah, tace har yanzun zuciyata ta kasa yadda zaki iya aikata wannan danyen aikin, amma kuma wani sashi na zuciyata yana gasgata kwararan hujojin da suka fito cikin kankanin lokaci, kuje zan cigaba da yi miki addua Allah ya bayyana gaskiya, ta juya tayi hanyar daki tana kuka nurain da jalila suka bita suna rarrashinta, sadeeq kuwa daki ya wuce yana kuka, wanda ke waje ma zai iya jiyoshi, sanah na tsaye tana bashi hakuri amma kamar kara zugashi takeyi, ta zauna itama tana matsar kwalla tace ashe mafarkin da ka tabayi zai zama gaskiya, kayi mafarkin faruwar wannan alamarin duk tunanina aikin mafarki ne ashe zai zama gaske, gaskiya yarinyar nan ta cutar damu matuka, sadeeq ya juya yayi ruf da ciki yace tashi ki fita plsss inason kadaici yanzu, bana bukatar yawan magana, ta mike sum2 ta fita tana gimtse dariyarta, yanzu kokari kawai zatayi taga ta dauki ciki ta haihu da sadeeq tunda yanzu ita kadai ce dashi... Labarin wannan mutuwar ko ina ka zaga a fadin nigeria zaka jita, news papers, gidan radio da tv kowa yasamu aikin yi , daga ka kunna kafafen yada labarai zakaji ana fadin mutuwar, sunan zulfah da hotonta babu inda bai zaga ba mutane sai Allah wadai sukeyi da halinta, labari ya iske goggo marka tana zaune tayi tagumi tana kallon ya'yan salaha dake raba mata kashi a tsakar gida, cikin tsawa tace ma salaha tazo maza ta tsaftace mata guri, bazai yiwu kazanta ta koroki daga gidan mijinki ba ki zo nan kuma ki dira min wata, haba!! ko waina an daina siya tun dawkwarku gida saboda bakar kazantarku, gashi abinci ma da kyar muke samun ci sau daya, maza gyareshi wallhy, shigowar wani yaro wanda yake siyan waina a gurinta ne ya katse masifar da takeyi, yaron yace markus kinsan abinda ke faruwa kuwa a kasar nan, marka sarkin son jin gulma tace a'a me yafaru, yace hmm an kashe surikin zulfa kuma kinsan waye ya kasheshi, tace a'a Allahn misiru gareni, yace zulfa ce ta samishi guba a abinci, goggo marka gabanta ya fadi tasan zulfah ko kyankyaso tana jin tausayin kashewa bare dan adam, amma a fili saboda tsabar hassada da kiyayya tace ay kadan ma suka gani, yarinyar da ni kaina tasha kawo min hari zata kasheni, Allah ya kyauta gaba ta fadi ta mike da kuzari da murna saboda taji zulfah ta shiga tsaka mai wuya. Goggo amina ma sunci kuka ita da fa'e dake da da daya da wani cikin, kuka sosai sukeyi suna rokon Allah ya fitar da zulfah daga cikin wannan bala'in.... . Mrs tijjani shattima... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆5⃣7⃣ By Aysha Ya'u Kurah Ranar da daddy ya cika kwana uku bayan gabatar da adduoi da sadaka mutane sun watse cikin jimamin mutuwar bawan Allah mai taimakon talakawa,, Zaune suke a parlo dukkansu kowa yayi tagumi daga ka gansu kasan suna cikin matsananciyar damuwa, afrah ta kalli mummy da hawaye ke fita a gefen idonta tace mummy dan Allah kisa su yaya nurain suje su fito da anty zulfa'u wallhy kinsan bazata iya kashe mana daddy ba, Nurain ya kalli mummy ko zata ce wani abu dan shima zuciyarshi ta kasa yadda da wannan sarkakaken alamarin, ya maida kallonshi gurin sadeeq da ya takure kanshi guri daya yace abba tashi muje station muga inda suka tsaya a binciken, sadeeq bai kalleshi ba ya girgiza mishi kai kawai, anty laila ta mike tsaye tace muje abban ayda dan Allah muje inga halin da zulfah take ciki, anty amarya ta fito daga daki tana kuka sosai wata matashiyar yarinya na biye da ita, cikin kuka tace duk wani bincike ya gama tabbata yaya, kalli wannan hoton, mummy ta share kwalla a idonta ta karbi hoton, fuskar zulfah ta gani muraran kwance tsirara da wani saurayi, runtse idonta tayi ta wurgar da wayar tana salati, anty amarya tace yanzun nan yarinyar nan tazo ta kawo hoton ashe abun da daddy ya kamata tanayi kenan shiyasa tayi saurin kasheshi dan kar ya tona mata asiri, mummy ta mike tsaye jiri ya debe ta tafi luuu ta fadi kasa sumammiya, da sauri dukka yan gidan suka yi kanta suna kuka aka shafa mata ruwa, saida tayi kusan minti 5 sannan ta farfado tana kuka sosai, anty laila dake rike da wayar tace wallhy wannan ba zulfa'u bace mummy, wai meyasa kowa baya fahimtar abinda nake fahimta a kwakwalwata ne, ta matso kusa nurain kamar zararriya tace abban ayda nasan zaka fahimce ni, wallhy wannan sharrin computer ne, yarinyar dake tsaye tayi saurin cewa zakiyi kaffara kuwa, ni ko alqurani za'a bani zan rantse da cewar wannan zulfa'u ce, ranar da abun nan ya faru kunga text din da tayi min, suka duba text din da numbr duk na zulfa ne, lokacin da muka hadu da ita na rakata hotel din na jirata a reception ta gama ta fito suna fada da shi wannan da kuka gani mai suna Bamba akan kudin da ya bata kadan ne, sunata zage2 lokacin shi kuma marigayi ya fito da abokanshi ya ganta, tun daga lokacin da ya ganta take fada min ya fara ciwo har an fita dashi waje, tace min bai fada ma sadeeq ba amma tasan yana dawowa zai fada mishi saboda haka zata san abun yi kafin ya dawowa ashe kasheshi zatayi yarinyar ta karasa fadi tana kuka sosai, anty laila ta harareta cikin kuka tace munji tatsuniyarki yanxu imani ne ya shigeki kika zo kika tona ma kawar shashancin taki asiri, yarinyar ta dake saboda kwarewa a iya sharri tace ni bana biye mata kullum fada nake mata kuma wallhy in baku yarda ba yanzu sai in shigo muku da Bamba dan shima yace sai ya tona mata asirin abun da takeyi a boye, anty amarya tace je ki shigo dashi, sadeeq dai tunda ya kalli hoton ya runtse idonshi bai sake budewa ba, har suka gama karyarsu da karairayi, zuciyarshi ta zama kamar dutse saboda duk yadda yaso ya tankwarata taki tankwaruwa, fashewa yayi da wani irin kuka mai tsuma zuciya yana tambayar zuciyarshi whyy ta damu da his father murdrr, meyasa bazata daina tunanin zulfa'u ba a wannan lokacin da ya kamata ta tayashi tsanarta, meyasa har yanzu zuciyarshi take kallon zulfa'u innocent, kukan da yakeyi ya ba dukka yan parlon tausayi jalila ta rungumeshi tana rarrashinshi tana kukan itama, Bamba da maimzy basu bar gurin ba saida sukayi ma zulfah qullin da babu mai warwareshi sai Allah, duk gurin sun yarda saboda hujjojin da suka kawo musu ciki harda warwaron zulfah da mummy ta siyo musu tare da jalila wanda nata ya bace kwana biyar kafin faruwar wannan lamarin anty laila ce kadai bata yarda ba, tirkashi.... Nurain yaa dafe kanshi da ya dau zafi yace laila ki daina kukan nan haka mana, hujjoji nawa aka kawo kuma duk masu karfi, shi kanshi daddy kafin a kasheshi saida yayi ma mummy tsokaci akan hakan, tsokacin me yayi mata ta fadi rai bace, tace matan abba nawa ne, abban ayda bakasan sharrin mutum ba ko, babu abinda zance maka yanzu saboda ko nace bani da shaida amma ol wat I knw shine zan koma aiki saboda zulfah, in shaa Allahu sai na gano azzalumin da ya daura mata wannan sharrin, nooo nurain ya fadi yana kallon cikin idonta, bazaki koma aiki ba laila, babu abinda zakiyi da case din wacce ta kashe min mahaifi, ka daina cewa ta kasheshi ta fadi da karfii, wallhy zaka tsaya shaida ranar gobe kiyama,, kuma aiki sai na koma ko da kuwa hakan zai kawo karshen auren mu, tana kaiwa nan tasa kai ta fita daga dakin, dafe kanshi yayi idonshi yayi jawur saboda kalaman laila, ya za'ayi laila tayi mishi haka, yanzu da wani baki zai fara fada ma mummy laila zata tsaya ma zulfa'u, dole ya dakatar da laila kar ta karama mummy wani ciwon... mrs tijjani shattima... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 5⃣8⃣ By Aysha Ya'u Kurah Tun safe laila ta gama shirin tafiya gurin zulfah, duk irin tataburzar da sukayi cikin dare da Nurain bai sa ta karaya ba, ita dai abin da tasani shine xata fara bincike daga yau kuma ita kadai tasan inda ta karkata akalar bincikenta,, dakin mummy taje ta gaisheta da jiki sannan tayi mata sallama tace zata je asibiti ta dawo, mummy tayi murmushi dan jalila ta gaya mata duk yadda sukayi da nurain cikin dare kuma ta goyi bayanta dari bisa dari baza dai ta nuna ma kowa bane dan kar mutane su dauka mutuwar bata dameta ba, ta kalleta tayi mata Allah ya tsare kuma Allah ya taimaka, anty laila tace Ameen mummy, ta fita ta dauki motarta bata yarda wani driver ya kaita ba, Baban zulfah ne tsaye shi da kabiru a waje sai sharar hawaye yakeyi kabiru na rarrashinshi, tun jiya suke tsaye a gurin an hanasu ganin zulfa, saboda tana kebabban dakin masu manyan laifuffuka, laila nayin parking ta fito tayi hanyar shiga ciki, ganin baban zulfah ya dakatar da ita, ta karasa gurinsu ta gaishesu, baban zulfa yayi saurin tsugunawa saboda ya ganeta, cikin kuka yace hajiya walhy zulfah bazata aikata kisan kai ba, an samu sabani dai gurin bincike amma ni nasan bazata aikata ba dan Allah ku taimaka ku fito min da ita, anty laila ta share hawayen da ya zubo mata a idonta tace karka damu baba, ka daina wannan kukan addua ita kadai ce zata fitar da ita daga wannan mugun kullin da akayi mata, adduarka muke bukata Allah zai bayyana gaskiya, malam ado yace to nagode hajiya Allah ya bayyana gaskiyyar nan cikin gaggawa, ameen anty laila tace sannan ta wuce ciki suna binta a baya, Da kyar aka barta ta shiga gurin zulfah saida ta nuna musu itama bata da mutunci sannan suka barta ta shiga dakin da akayi mishi kewaye da mukullan tsaro masu matukar tsauri, can lungu inda ta hango zulfah a dukunkune ta karasa, dafata tayi sannan ta tsuguna tana fuskantarta, a hankali ta fara mata magana, zulfah taki dago kanta sai sheshshekar kuka da takeyi, anty laila tace zulfa kiyi shuru ki dago ki bani hadin kai in fitar dake daga cikin wannan zargin da ake miki, nan ma zulfah bata dago ba, anty laila tayi maganar duniya zulfah taki dago kanta ta kalleta bare ta bata amsa, gaba daya ta cire rayuwar duniya a ranta gara ta mutu da ta cigaba da rayuwa a wannan rudun dake cikin wannan kazamar duniyar mai cike da sarkakiya, ran anty laila yayi matukar baci ta mike tace kinsan shurun nan naki zai iya haifar da munanan abubuwa kuwa, kinsan mutanen dake bukatar ki a rayuwarsu kuwa, shin kin manta da mahaifinki wanda kike fada min a kullum burinki ki yanta shi daga wahalar da ya dade yanayi in har kika tsaya da kafafuwanki, ta matso kusa da ita ta girgizata tace meyasa bazaki bamu hadin kai ki fada mana abinda kika sani ba, ta fita waje da sauri ta kira mahaifin zulfa suka shigo tare suka hadu suka dinga yi mata magana harda kukansu amma zulfah bata dago kanta ta kallesu ba saboda bata da wata kalmar da zata fada wacce zata iya fitar da ita daga sharrin kisan kai da zinah, har lokacinsu ya cika basuyi nasarar jin komai daga bakinta ba, tashi sukayi suka fita cikin bakin ciki,, kwana uku anty laila tayi tana zuwa gurin zulfah amma kullum da bacin rai take komawa gida, gashi su anty amarya sun matsa sosai akan a shigar da kara kotu a yanke mata hukuncin da ya dace, ramewa sosai laila tayi saboda bata da kuxarin cin abinci, Ranar akayi bakwai ranar farouk ya dawo, tun a makaranta ya shiga matsanancin tasshin hankali jarabawar da yakeyi ita ta hanashi dawowa, yayi mamakin ganin duk su mummy sun yarda da cewar zulfah zata iya kashe daddy, har daki yaje ya samu sadeeq da ya kauracewa fita ko nan da bakin kofa, ya zauna yana mishi magana akan su san yadda zasuyi su fitar da zulfah tun kafin a shiga kotu, hararar shi sadeeq yayi murya a dashe yace farouk ka daina min wannan maganar wace hujja kake da ita da zaka ce bazata iya kashe daddy ba, hujjoji sun nuna itace farouk, idonshi ya fara fitar da ruwa yace farouk zuciyata taki bani hadin kan cireta a raina, ka fada min yadda zanyi inji na tsaneta farouk, ka fada min dan Allah, farouk ya tsuguna kasa shima yana kuka yace yaya abba zuciyarka tasan gaskiya kaine kaki bata hadin kai, shawarar da zan baka shine mu dage da addua ba dare ba rana har Allah ya fito da gaskiyar wannan alamarin... Hada hannu farouk da laila sukayi gurin bincike, babu yadda farouk ma baiyi ba akan zulfa ta fada mishi abinda ta sani, da kyar ya shawo kanta tace yaya farouk bani da wata kalmar da zata fitar dani, duk yadda zanyi in kare kaina bazai yiwu ba, kawai ku barni in mutu in huta da wahalhalun dake cikin duniya, daga haka bata kara ce mishi komai ba har ya tafi shima cikin kunan rai.. Ana gobe za'a shiga kotu anty laila a susuce take saboda rashin shaida ko daya, tun asuba ta tashi tayi tagumi tana tunanin ta inda zata bullo, wayar zulfah dake gurin police ta fado mata a rai, ta mike da sauri tayi wanka nurain dai na kallonta baice mata komai ba saboda mummy tace ya barta tayi kuma ya bita da addua, tana fitowa wanka ta wuce station din, bata bukaci ganin zulfah ba saboda tana matukar bata mata rai, saida ta jira police din da case din ke hannunshi ya iso sannan ta karbi wayar, tun a gurin ta fara duba wayar, dialled calls ta duba tun na kwana uku kafin rasuwar, daga na jalila sai na sadeeq sai kawayenta Rolex da Frisky, haka ma recieved cals sai wannan number "aminiya" din da akasa kuma sau daya takk aka taba kira da ita, ta shiga mesges ta duba recvd shima na sadeeq ne kadai sai na numbr aminiya, a send kuma wata numbr ce akayi ma sending text din da su maimzy suka kawo, ta duba tym din da date din, taayi mamaki matuka saboda lokaci daya akayi su da wanda akayi sending na aminiya, ta dunga binsu tana dubawa saboda ta gasgata idonta, saida ta gama tabbatar wa sannan ta mika ma police din wayar bayan ta copy numbrs din ta mike tayi mishi godiya ta fita, a mota ta dinga kiran layikan duk a kashe mtn office ta nufa dan ayi mata binciken layikan, abunda ya kara girgixa anty laila da aka gama bin diddigin layin bai wuce cewar duk sababbin layi ne da ake siyar dasu da register su, sannan dayan ko kira ba'a taba yi dashi ba, dayan kuma sau daya tak aka taba amfani dashi, da sauri jikinta har yana rawa tace ayi mata printing informatns din, nan sukayi mata ta fita tana musu godiya dan tana ganin kamar komai zai zo da sauki, To Allah yasa..... Mrs tijjani shattima... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 5⃣9⃣ By Aysha Ya'u Kurah Ranar monday 12 ga watan sept, ranar ce aka shirya shiga kotu, a daren ranar daukacin masoyan zulfah basu runtsa ba, addua ce suke ta yinta gurin ubangijin talikai akan Allah ya bayyana gaskiyar wannan alamarin, dakin sadeeq na shiga yana zaune kan dadduma yana kuka mai sauti, haka kawai ya tsinci kanshi da yin addu'a akan Allah ya bayyana gaskiyar wannan alamarin a yanke hukunci kowa ya huta, sanah da ta tare a gidan saboda mutuwar tana tsaye jikin kofar dakin tana hararashi a zuciyarta tana ba ameen ba, gaskiya bazata taba bayyana ba tunda babu wani mai shaida a hannu, tayi murmushin mugunta da ta tuna irin kullin da sukayi ma alamarin ta juya ta shiga daki ta kwanta tayi baccinta cikin kwanciyar hankali... Tun tara mutane suka fara dafifi dan jin hukuncin da za'a yanke ma matar da ta kashe surikinta, duk inda ka kewaya a gurin zaka ga mutane gungu2 suna tattaunawa game da rashin imanin mutanen wannan zamanin, Goma dai2 kotun ta cika makill wasu ma a tsaye suka tsaya saboda cikowar gurin, shigowar alkali ne ya sa kotun tayi tsitt kamar babu rayuka a ciki, nan suka gabatar da abinda suka saba yi kafin daga bisani a fara gabatar da shari'u, mai gabatarwa ya mike ya gabatar da case din dake gabanshi na farko, na zulfa'u Adam wacce ake zarginta da kashe mahaifin mijinta, alkali ya gyara glass dinshi da alkalminshi, ya fara da sunan Allah mai rahama mai jin kai, sannan ya bukaci a shigo da wacce ake tuhuma, Mutane suka maida kallonsu gurin kofa dan ganin wacce suke ma kallon mara imani mai son duniya, shigowar zulfah cikin hijab da ankwa a hannunta yasa kotun ta dauki hayaniya sosai,jalila dake rakube gefe daya ta kalleta idonta ya ciko da kwalla saboda yadda duk ta zube cikin yan kwanaki, rolex da frisky na hango suna kuka mai sauti suna kallon zulfah, bayan ta tsaya a inda aka bukaci ta tsaya yan sanda na tsaye gefenta, alkali ya bukaci ayi shuru a kotun, nan ya kalli barristers din ya dan sauke glass dinshi, nan da nan wani bakin handsome ya mike cikin girmamawa yace sunana barrister "Tahir Kurah" nine lauyan wanda suke kara, ya koma ya zauna, anty laila ta mike itama cikin girmamawa tace sunan Sunana barrister "Lailah Isah Ameh" nice lauyar wacce ake kara, bayan dan gejeren lokaci alkali yace barrister Tahir bismillah, tahir ya mike ya isa kusa da zulfah yace baiwar Allah ko zaki iya fadawa kotu sunanki, kan zulfah a sunkuye taki dagowa ta bashi amsa, ya kara wurga mata tambayar, nan ma shuru tayi, anty laila ta dafe kanta cikin bacin rai, alkali ya tausasa murya yace baiwar Allah ya kamata kisan nan ba gurin wasa ko taurin kai bane, ki bamu duk wata amsar da aka tambayeki ba tare da kin bata mana lokaci ba, tayi shuru bata dago kai ta kalleshi ba, tahir yace ko zaki iya fadawa kotu sunanki, a hankali ba tare da ta dago kanta ba tace sunan zulfa'u adam, zan takaice muku shariar nan ba tare da kowa yasha wahala ba, ni na kashe shi, nice na kashe shi da hannuna, ta dago kanta tana kuka sosai tace dan Allah mai shari'a ka yanke min hukunci ba tare da bincike ba, duk hujjojn da aka kafa na daukesu, ta rage kukanta a hankali tace meye a cikin duniyar nan da mutum zaiyi sha'awar ta, menene burin wadanda suka daura min wannan KAZAFIN (littafin kawalliya ta), burinsu shine su zauna a duniya suji dadinsu ni kuma in mutu da yarfen kisan kai ko, ta daga hannunta tace dan Allah mai sharia ka cika musu burinsu ka yanke min hukuncin kisa, nasan ko yau ko gobe ko jibi ko nan da shekara dari ne zasu zo inda zanje anan ne za'ayi shariar karshe lokacin da nake da mafita su basu dashi, dan son annabin Allah karka barni in kara kwana a wannan duniyar, ka yanke min hukuncin kisa kamar yadda ubangiji ya fadi a alqurani, ta kara fashewa da kuka mai tsuma zuciya, kalaman zulfah sun sanyaya gwiwar dukkan mutanen dake gurin, sadeeq da sauri ya tashi ya fita yana kuka shima kamar kwakwalrshi zata buga, alkali ya dan dukar da kanshi kasa yasa hannu cikin glass dinshi ya share kwallar da ta taru a idonshi, ya dago kanshi ya kalli tahir da ya tsaya kamar gunki yace barr tahir baka da tambayar da zakayi mata, barr tahir yace duk wata tambaya da zan mata ta riga ta bada amsa da bakinta saboda she's guilty, zan gabatar da hujjojin da nake dasu duk da ta fadi da bakinta but saboda kotu ta kara gamsuwa zan gabatar mata da kwararan hujjoji, wayar da ke hannun police din aka amsa aka mika ma alkali bayan an budo mishi txes din sannan ya bukaci a shigo mishi da wasu shedun da zasu tabbatarwa da kotu itace ta kasheshi, bamba aka fara shigowa da shi ya fadi duk karyar da ya fadi rannan, sannan aka shigo da maimzy itama ta fadi duk karyar da ta fadi a gidan, alkali ya tambayi laila ko tanada tambayar da zatayi ma maimzy, laila ta share hawayen idonta ta mike tace eh, ta matsa kusa da maimzy bayan ta gama gyara hular kanta, tace malama maimzy tun yaushe kika san zulfa'u, zufa ta fara tsatstsafo ma maimzy tace wata rana a hamdala hotel, laila tace gudd tun daga lokacin kuka zama kawaye kenan, maimzy tace eh, laila ta kafeta da ido tace kuma a statement dinki kince fada kike ma zulfah akan shashancin da takeyi kenan daukar karatu kikaje yi hamdala har kuka hadu da zulfah, maimzy iya tsurewa tayi tace ammm.... eh naje... naje,,, Objection mai girma mai shari'a tahir ya fadi hade da mikewa tsaye ya kamata barr, laila tasan irin tambayar da zata dingayi, bai kamata ta dinga ruda wanda take tambaya ba, alkali yace barr laila a kiyaye, tace okk my lord, tace maimzy ko zan iya ganin wayar da zulfah tayi miki text a ciki, da sauri jikinta na rawa saboda laila ta gama rudata tace eh gata nan, laila ta karbi wayar sannan ta amshi wayar zulfah tace ya mai girma mai shari'a, a ranar 3 ga september karfe 4:45pm text ya shigo wayar zulfah sannan at dat very tym wani text din ya fita daga wayarta, kuma a statement din maimzy tace tun kafin mutuwar marigayi zulfah ta turo mata da text din, ya akayi text ya shiga kuma ya fita lokaci daya a ranar mutuwar marigayi, ko daga nan ma zamu gane cewa wannan shiryayen abune, ta mika wayoyin aka mika ma mishi, sannan ta dakko takarda tace ya mai girma mai shari'a wannan takardar bin diddigin layi ne wanda aka tabbatar min da a rana daya aka fara amfani da wadnnan layikan, kuma wannan layin da maimzy ke ikirarin tana amfani dashi layi ne da ko sau daya ba'a taba kira dashi ba kuma tace mana suna waya da zulfah har ma suna shirya gurin da zasu hadu duk ta wayar,, sannan dayan ma sau daya takk akayi kira dashi, dayan shine ke cike da rudu saboda an rubuta AMINIYA kururu a jiki, kuma in aka duba wayar zulfah bata taba kiran layin ba ko sau daya, haka text, in har zulfah ta shirya plan din kisa dole mu samu numbers din nan a kan dialled calls dinta, wannan shine shaida ta ta biyu da zan tabbatar muku da wannan plan ne shiryayye, jikin maimzy ya fara rawa cikinta ya duri ruwa ta maida kallonta gurin da sanah dake zaune itama a tsuree..... Mrs tijjani shattima... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 6⃣0⃣ By Aysha Ya'u Kurah Anty laila ta cigaba da cewa ya mai shari'a ya kamata a duba wannan lamarin da kyau, a daura shi a kan mizani a aunashi sannan ayi wa wacce ake tuhuma adalci, "nagode ya mai shari'a", alkali ya gama rubuce rubucen shi, ya dago kai ya kalli barr tahir yace barr tahir ko kana da abin cewa, tahir ya mike yace eh ranka ya dade, ya fito ya tsaya yace ya mai shari'a wadannan hujjojin da barr laila ta fada yayi kama da labarin kanzon kurege, hujjojinta basuyi karfin da har zai iya sawa a kori wannan shariar ba, barr laila tace a wayar makashiyar babu kiran numbr da suka hada plan din akan dialld calls, shin ko barr ta manta cewa ko wace wayar duniya akwai gurin da ake share abubuwan da ba'a bukatar wani ya gansu musamman ma abin nan in na sirri ne, ko ma wanene in har yasan bashi da gaskiya zai iya yin duk abunda xaiyi dan ya ga asirin shi ya rufu, saboda haka ina rokon wannan kotun mai alfarma da tayi watsi da wannan shaidar in akayi la'akari da rashin karfi da ingancinta, sannan shaida ta biyu barr tace a mtn office an bi mata diddigin layin kuma an gano sababbi ne, yayi murmushi yace ya mai shari'a mutumin da har yake da fasahar kisan kai har zai rasa dabarun da zai batar da mutane akan layikan waya, barr laila da bakinta tace lokaci daya aka siya layin nan, ta yiwu makashiyar ita ta siya layukan ta rabasu ga aminanta saboda su gama komai ba tare da an gano su ba, text kuma da take cewa lokaci daya aka turo kuma aka fitar, wannan kowa yaji yasan ita ta kitsa abinta saboda ko da an kamata ta samu mafaka akan bata san komai ba, mutum mai wayau zai iya yin text shekara biyar ma da suka wuce, dan ya sabunta text din zai iya copying dinshi ya goge wancan ya tura wani a lokacin kaga anan ya mai shari'a an sabunta date din da tym din, da wannan nake rokon wannan kotu mai alfarma akan tayi watsi da wadannan hujjoji ta biwa marayun da suka rasa ubansu da kuma matan da suka rasa mijinsu hakkinsu da gaggawa saboda rashin kwakwarar shaida da za'a gabatar da ita a gaban kotu,, ya numfasa sannan yayi godiya ya koma ya zauna, sai a sannan sanah ta gyara zama ta share zufar dake kwance a kan fuskarta, alkali ya gama nazarin bangarorin duka biyu sannan yace shaidu sun gabata a gaban mu, amma saboda rashin karfin shaidar dayan bangaren zamu ďaga wannan shari'ar har 10 ga watan October dan a taro gamsassun hujjoji saboda yin adalci ga kowane bangare, nan hayaniya ta kaure a cikin gurin anty laila taji dadin adalcin da akayi musu dan yanzu ne take da lokacin fara bincike saboda samun karin lokaci, bayan an tashi daga kotun anty laila da farouk suka bukaci a basu belinta amma samm aka ki saboda karfin laifin da ake zarginta dashi, haka suka hakura suka wuce gida suna tattauna yadda zasu sake bullowa alamarin, sanah kuwa da ta koma gida ita da amarya dake takaba suka kule can daki cikin rashin jin dadin rashin yanke hukunci tun yau, amma sai suka shagala saboda a ganinsu sun ma abun daurin da dakyar za'a iya warwareshi, da wannan tunanin hankulansu yayi daya suka cigaba da harkokinsu.... Kwance yake akan resting chair a gidan yake, wani littafin addini yake dubawa yana kara zurfafa iliminshi akan karfafa gaskiya a cikin aikinshi, gaba daya ya maida hankalinshi akan littafin, burinshi kawai duk shariar dake gabanshi ya aiwatar da ita bisa gaskiya da amana,, wannan dalilin ne yasa wata kotu mai zaman kanta a kasar singapore suka rikeshi aikin dindindin saboda kwazonshi da nutsuwarshi, sam wasu kyalekyalen duniya basu dameshi ba, aikinshi kadai yasa a gaba kuma cikin ikon Allah duk wani aiki da akazo mishi dashi sai ya samu nasara akanshi saboda tsayuwar da yayi akan ibadarshi da kuma rikon amana, muryar abokinshi naji yana fitowa daga kitchen rike da glass cup din juice a hannunshi yana cewa ya ustaz yau dai we are free rabon da mu zauna mu samu hutu yafi sati uku saboda wannan shari'ar,,. yau daya dai sai ka ajiye littafin hannunka muyi hira mu kira gida muji lafiyarsu anjima kuma mu fita yawo muyi murna saboda samun nasara akan wannan shariar da ta kara daga sunanka a cika da batsewar singapore, SALEEM ya rufe littafin ya mike ya zauna ya karbi cup din ya kora juice yace amma ay ansha bakar wahala kafin samun nasarar, ni dai kam babu inda zani gara in zauna abuna a gida in huta in samu lokacin da nayi sati biyu ban samu ba mu gana da ubangiji na, Isma'il yayi murmushi yace Allah taimaki ustaz ina son halin nan naka nima Allah ya koyar dani kyawawan dabiunka, saleem yace ya koyar da kai kyawawan dabiun da manzon mu,, ya rage namu mu bi ko mu bi san ranmu, amma ko wani muslmi Allah ya koyar dashi dabi'u na gari in har xaiyi koyi da sunnar manzo s.a.w, isma'il yace hakane saleem Allah ya ganar damu, ya dauki wayarshi da ya bude data tun dazu yana jiran ya gama komai ya hau ya sada zumunci da yan uwa da abokan arziki, saleem kuwa komawa yayi ya kwanta ya lumshe idonshi zuciyarshi na tasbihi ga Allah, Isma'il ya gama gaishe gaishen da xaiyi a whatsapp ya dan bata lokaci yana hira da budurwarshi da sukayi missing juna, facbk ya hau,, news feed barkatai ya gani ya shiga binsu yana girgiza kai da Allah wadai da shuwagabannin mu na Nigeria, Rariya, Sahara, naija report da sauransu a gurin yaga abubuwan da suka girgizashi, duba date din yayi yaga tun on 3rd sept abin ya faru, sannan yaga har an shiga kotu 12 sept, a zuciyarshi yace wannan kisan ya kusa 3wks kenan ma, innalillahi wa inna ilair rajiun shi ya fadi da karfi, saleem ya bude idonshi yace lafiya ismo me ya faru, isma'il yace wani alamari nagani mai ban tausayi gashi nan a rubuce wai an kashe "Air- marshal Hasheem abubakar marafa", saleem ya zabura ya mike zaune yace watt,?? isma'il ya mika mishi wayar yace kalli kagani kuma surikarshi ake zargin ta kashe shi, saleem ya karbi wayar da sauri, hoton zulfa da sunanta da yagani shi ya sashi mikewa tsaye ko ina na jikinshi na rawa, isma'il ya mike shima yace kaga rashin imanin mutane ko, yanzu yar wannan yarinyar har tana da dabarar kisan babban mutum haka, yaran yanzu duniya kadai suka sanya a gaba,. saleem cikin rawar murya yace "allahumma ajirni fi musibtn wa akhlifni khairan minha, la haulu wala kuwwat illah billah"", ya koma dabas ya zauna, isma'il yace saleem lafiya, saleem idonshi yayi jajur yace isma'il zulfah bazata iya kisan kai ba, isma'il ya dafashi yace u mean zulfar da ka taba bani labarinta ce wannan, saleem ya daga mishi kai, ismo yace ya Salam kaga tsiyar rashin xama current ko, kai kullum sai kace mu daina shagala akan waya ko wasu abubuwan more rayuwa kuma wallhy saleem nwadys sai ta waya aka fi jin duk wani abun da ke yawo a fadin duniya, yanzu gashi abu har ya kai three wks har an shiga kotu za"a kuma shiga on d 10th, saleem dai bai ma san me ismo yake cewa ba, mikewa yayi ya shiga ciki ya kunna wayarshi, texes ne suka fara kara kainin shigowa cikinta, dan har ya manta rabon da yayi amfani da ita, text din yayanshi malam labaran shi ya bude ya karanta magana ce yayi mishi akan mutuwar da yarfen da akayi ma zulfah, bai bude sauran ba ya shiga kai kawo cikin dakin, ismo ya shigo ciki yace saleem yanzu ya za"ayi kenan, saleem murya can ciki yace abin da nake tunani kenan isma'il, yarinyar nan tana cikin matsala babba, dole in nemi tafiya cikin kwana uku ismo, wannan hakkin ya rataya a wuyana dole in san yadda xanyi in fitar da ita daga cikin kangin da take ciki, kuma dole a gano koma waye yayi wannan kisan in shaa Allahu zan tsaya kai da fata sai an gano ko waye an hukuntashi, ismo ya dafa shi yace tare zamu tafi saleem, duk wani aiki tare muke yinshi wannan ma tare zamuyi in Allah ya yarda sai munga karshen shari'ar nan cikin kankanin lokaci duk da tana da zafi amma a gurin Allah mai sanyi ce, saleem yace nagode sosai ismo ya kamata tun yanxu mu fara shirya shiryren tafiya, ismo yace hakane bari inyi wanka mu tafi..... Mrs tijjani shattima ... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 6⃣1⃣ By Aysha Ya'u Kurah Ranar laraba karfe 6 na yamma jirginsu ya sauka a abuja, ismo nata raba ido a airport din ko zaiga yayanshi har suka kusa minti goma bai hango kowa da ya sani ba, can yaji anyi ihu a bayanshi an dane kanshi ya juyo da sauri yaga kanwarshi Nafeesah, yayi dariya yace feenah bakya girma ke ko, so kike ki ballani, ta shagwabe fuska ta turo baki tace kai yaya iloli dan ma kaga ina murna shine zaka cemin haka ko, yace to am sorry sis baki gaisar da bako na ba, ta matsa kusa da saleem ta tsuguna tace ina wuni, saleem yace lafiya lau, ismo ya kalleta yace yaya bai zo ba ko, tace ay baya nan shine ya kira anty tasa driver yazo ya daukoka, ta dauki wata jaka a kasa tace muje yaya dare nayi, ya kamo hannun saleem suka wuce, suna karasawa gidan su dake sun city anan cikin garin abuja ismo yasa aka kwaso musu kaya suka shiga ciki bayan sun gaisa da Anty husaina suka wuce dakin ismo nan suka huta suka ci abinci suna hirarsu cikin nutsuwa akan ta inda xasu fara binciken tunda yau kwana 8 ya rage a shiga kotu.. Karfe 11 na ranar alhamis a kofar gidan su sadeeq tayi ma su saleem, bayan gajerun tambayoyi da masu gadi sukayi musu, sannan suka bude musu kofa suka shiga ciki, sallama saleem ya tsaya yayi kafin ya danna bell, farouk dake gyara agogo suna shirin fita shi da anty laila shi ya bude musu kofar, saleem yayi mishi sallama ya mika mishi hannu suka gaisah sannan yace dan Allah hajiya na nan, farouk yace eh ku shigo mana, suka shigo suka zauna farouk ya hau sama ya kira mummy, tare suka sakko tana ganin malam saleem ta fadada fara'arta, ta nemi guri ta zauna suka gaisa sukayi mata gaisuwar rasuwar mijinta, hira suka taba kadan akan nasorarin da ya samu tayi mishi murna sosai shima yayi mata godiya saboda itace silar cigaban shi, , anty laila ta fito daga daki suka gaisa dasu saleem, ta kawo musu dan abin tabawa, saleem ya fara tambayar mummy maganar zulfah, ta gyara zamanta fuska cike da damuwa ta kwashe komai ta fada mishi, shi da ismo dai sukayi tsamm cikin tunani, barr saleem yace hajiya kiyi hakuri, karki ce na karyata hujjojin da aka gabatar, kuma karki ga kamar ko zan goyi bayan zulfah ne amma zan tsaya inyi bincike har agano gaskiyar wannan lamarin, in zulfah nada hannu a ciki zan tsaya kai da fata inga anyi mata hukuncin da ya dace, mummy tayi ajiyar zuciya ta rage muryarta tace, saleem zuciyata ta kasa gasgata wannan alamarin, amma bani da yadda zanyi saboda kwararan hujjojin da sukayi ma alamarin nan kawanya,,, yanzu dai kasan abin da nake so da kai, ka tashi ka fita waje zan turo maka laila dan itace lawyern dake bincike akan alamarin, banason ko kadan mu sake tattauna wasu maganganu a cikin gidan nan, saboda zuciyata bata aminta da mutanen dake cikin gidan ba, Allah ya gaggauta bayyana gaskiya, suka ce amin,, suka mike cikin farin cikin mummy bata yarda ba ita ma saleem yace to nagode hajiya sannan suka fita shi da ismo suna tattauna karamci irin na mummy, A dakin sadeeq mummy ta samu laila suna zaune ya dafe kanshi da ruwan lipton a gabanshi, tana lallabashi ya dan sha sannan ya danyi mata bayani akan abinda yace daddy ma ya kirashi ya fada mishi, ya dan kurbi lipton din yace ehh daddy ya kirani ana gobe zai dawo ya fada mata duk tambayoyin da daddy yayi mishi, mummy dake tsaye a kansu tace laila kira farouk kuje ga baki can a waje suna jiranku, anty laila tace to mummy, ta mike ta fita tabar mummy gurin sadeeq itama tana rarrashinshi akan yaci wani abu... Mota daya suka shiga dukkansu su hudun suna tafe suna tattaunawa suka wuce gurin zulfah, anty laila tace wallhy malam yarinyar nan bazata taba yi maka magana ba, ita kullum burinta a barta a yanke mata hukuncin kisa shiyasa bana bi ta kanta yanxu a bincike na,, saleem yace to bari mu je in jarraba in gani, suna karasawa anty laila tayi zamanta a mota dan ji takeyi kamar ta shaketa ta huta, Zaune take kamar kullum a takure kanta na cikin cinyoyinta, karasawa sukayi suka tsuguna kusa da ita, saleem ne ya fara mata magana, ta gane muryarshi tsaff amma taki dago kanta ta kalleshi, cikin dabara ya kara mata magana, zulfa'u ki saurareni da kyau kiji abinda zan fada miki, ruwanki ne ki dauka ruwanki ki zubar ni dai na fita hakkinki kuma na sauke alkawarin da na daukarwa kaina cewar duk lokacin da kika shiga cikin wani hali zan taimaka miki, rayuwar dan adam tana da matukar muhimmaci zulfa, dan adam duk tsanani baya ma kanshi fatan mutuwa, me kika tanada yanzu idan kin tafi lahira,? wa kika ajiye a duniya da zai miki addua ko bayan ba ranki, ko kina tunanin wannan taurin kan da kikeyi in har aka kasheki zaki je ki samu rahamar ubangiji, to bari kiji in fada miki, ubangiji na baiwa dan adam dama a rayuwar shi, kinga wadannan damomin da kika samu ubangiji shi ya turo miki su,kinga anan rashin maganarki ya nuna cewar bakya farin ciki da abinda Allah ya turo miki dashi, shin kina tunanin mahaifinki kuwa, ashe bazaki godewa Allah da ya baki gida irin wannan da har suke tunanin taimaka miki duk da irin karfin hujjojin da aka kafa akanki ba, zan barki yanzu babu wanda zai sake dawowa gareki, amma ki sani har a nade duniya sunanki bazai taba goguwa akan wacce bata da imani mai kisan ba, kuma ko a lahira shaidar mutane na iya cetonka ka shiga aljanna, kinga anan kin rasa wannan shaidar, sannan zunde da maganganun da za'ayi tayi akanki zai iya daurawa mahaifinki ciwon mutuwa kinga kenan laifin kisan kai biyu kenan da naki da na mahaifinki, dan haka na barki lafiya in an kasheki zan miki adduar samun rahama, maganganun malam saleem sun sanyaya gwiwar zulfah, jin takun tafiyarshi yasa ta kara fashewa da kuka mai tsuma zuciya, farouk idonshi ya ciko da kwalla yace zulfah dan Allah dan annabi ki yi mana magana wallhy mutane da yawa suna cikin halin kunci akan wannan alamarin kuma rashin maganarki zata cutar da rayuka da dama ciki harda dan mala'ikan Allah dake cikinki, da sauri ta dago kanta idonta kamar nama ta shafa cikinta tace yaya farouk me kukeso ince, me kukeso in fada muku, kome zan fada muku baida karfin da zai fitar dani daga wannan kazafin da akayi min, saleem da ya kusa kaiwa kofa ya dawo rai a bace yace kalma daya ta gaskiya zata iya tarwatsa kalmomi dubu na karya, saboda haka ki bude baki ki bada amsar tambayoyin da zamuyi miki, ta gyada kanta tana kuka sosai, farouk baisan sanda murmushin jin dadi ya kubuce mishi ba,, ismo yace ki nutsu sosai duk abinda aka tambayeki ki yi tunani da kyau kafin ki bada amsa, tace to,, saleem yace a ranar da abin ya faru ance babu kowa a cikin gidan sai ke ko, tace eh, yace to amma ance wai wata tazo gurinki a lokacin, zulfah tace ni babu wacce tazo guri na, ismo yace kuma babu wanda kika gani ko kuma kikaji muryarshi kodai wani abu makancin haka, ya kalli saleem yace kasan meyasa na tambayeta haka, saboda wanda ya shirya wannan plan din a tym din ya shirya shi tunda har masu gadi sun ga mutum biyu sun shiga cikin gidan, kaga dole wanda yake cikin gidan yaji ko yaga wanda ya shigo, zulfah tayi shuru tana tuno sanda ta fito wanka taji buruntu a gurin dining da kuma ganin da tayi ma beeba, da sauri tace ehh wallhy na ganta lokacin da na fito wanka naji kamar ana taba wani abu a gurin dining da na fito banga kowa ba ta window na hangota, kuma wayata ma na kan dining sai a lokacin na dauketa, jikinta ya fara rawa tace wallhy na ganta.... Mrs tijjani shattima... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 6⃣2⃣ By Aysha Ya'u Kurah Saleem cikin farin ciki yace wacece ita, Zulfa tace kawar sanah ce,, wallhy ita na gani kuma itama ta ganni, farouk yace kawar sanah wacce a ciki, tayi shuru tana nazari can tace Beebah ce ita nagani, farouk yace Habiba Garba kike nufi, tace eh ita wacce suke zuwa gida tare da sanah gurin anty amarya, farouk ya tashi ya fita da sauri, gurin anty laila ya nufa dake zaune cikin mota ya bude motar yana sauke numfashi yace anty tunaninki ya zama gaskiya, zulfah tayi magana tace taga beeba a cikin gidan mu on dat vry day, anty laila da sauri ta fara maida takalmanta kafarta ta bude motar suka fito ita da farouk suka koma ciki, suna shiga anty laila ta dafa ta tace haba zulfah kinsan da wannan shaidar kikayi shuru kika bari munata wahala, ta kalli su malam saleem tace alhamdullah yanzu komai zai tafi da sauki ay ko gobe ma a shiga kotu, saleem da isma'il suka kwashe da dariya suka ce da wace hujjar, anty laila tace wannan hujjar mana ay wannan hujjar mai karfi ce tunda me ya kawota gidan a wannan tym din gurin wa tazo, saleem ya mike yayi murmushi yace anty wannan hujjar bata karfi ko kadan mu ne zamu maida hujjar ta zama mai karfi, a yanzu in muka shiga kotu da wannan shaidar to tabbas zamu rikito, beeba nada access da gidan ko ba haka ba, duk suka gyada kansu, saleem yace xata iya denying flat tace aiko ta akayi ko kuma tace tare suke da anty amarya, ka tsoraci sharrin mai sharri inji hausawa, haka in baka iya kama barawo ba to tabbas shi zai kamaka, wanda duk ya iya kulla wannan sharrin to ba karamin devil bane sai da dabara za'a iya kayar da ko ma waye, anty laila tace haka ne to yanzu ya za'ayi mu maida wannan shaidar ta zama mai karfi, good saleem ya fadi yana gyyara tsayuwar hularshi, yace wannan maganar a kebantaccen guri zamuyi yanzu muna fita daga nan dan zuwa gobe in shaa Allahu zamu fara aiwatar da aikin ... Farouk ne tsaye kofar dakin sadeeq sanah na zaune tana jefo mishi hira jefi jefi saboda rashin sabon da basuyi ba, shigowa dakin yayi gaba daya ya zauna suna hirah cikin dabara, can ya shafa cikinshi yace wallhy yunwa nakeji anty sanah, ran sanah yayi fari kal dan a tunaninta yanzu sun fara sonta saboda abinda zulfah ta aikata, mikewa tayi tana murmushi tace bari in dafa maka ko indomie ce, ya gyara zama sosai yace aiko da kin kyauta min, ta wuce kitchen tana murmushi, farouk ya saci kallon sadeeq dake kwance idonshi a lumshe ya mika hannunshi gefen da sanah ta tashi ya dauki wayarta cikin sauri ya shiga contact dinta yayi searching sunan "Beeba Gee" ya gani ya dauka da sauri sannan ya mayar da wayar ya ajiye, kwala mata kira yayi da karfi har saida sadeeq ya dan razana ya bude idonshi yana tsaki yace tashi ka fitar min a daki, farouk ya mike bai mishi magana ba ya deka yace bari inje in dawo ki ajiye min, tooo sanah ta fadi da karfi itama, farouk ya fita yana waka yana murmushi dan ya gama abinda ya kawoshi, tsakii sadeeq yaja ya mike ya wuce ciki dan ya kwanta ya huta, Farouk da sauri ya karasa dakin anty lailah yace angama anty, komai yayi dai2, anty laila ta karbi wayarshi tana dariya tace yauwa dan kanina shiyasa nake sonka wallhy duk kafi manyan banzan can hankali, ta kirah saleem tace ga numbr nan an samu, yace to ta turo mishi da ita "Asap" tace yanzu kuwa ay ba maganar sanya, ta kashe wayar ta tura mishi number suka cigaba da tattaunawa da farouk har saida nurain ya dawo sannan ya bar dakin... Oh my God khady zo kiga wani abun ala'ajabi, khady ta mike daga kwanciyar da tayi daga ita sai daurin kirji tace lafiya beeba, beeba ta mika mata wayarta tace kati ne kin ganshi nan na 20k aka turo min, khady ta karbi wayar da sauri tace waye wannan, beeba tace wallhy ban sani ba, ko ma waye ay zai biyo baya, dama yanzu na gama maular katin 400 sai gashi na samu wannan a bagas, ay ko mistake din numbr akayi wallhy bazan mayar ba yanda nake jin garin nan, yanzu ma zan samu in siyar da na 15k wallhy, khady tace gaskiya ki siyar ko zamu samu nacin abinci, beeba tace kwarai kuwa ay wannan tsuntsune daga sama gasashshe dama tun jiya nake kiran wannan yar iskar taki dagawa, wallhy sanah tana wasa dani, khady ta tabe baki tace ay wannan yar akuya ce, matar da kuna tare tana cikin daula har yanxu ta kasa baki jarin 500k ma, me akeyi da ita, ni wallhy ko kadan bata raina tunda maza kadai ke cin moriyarta, beeba tayi kwafa cikin bacin rai tace kedai bari ashe dai bani kadai ce ke wannan tunanin ba, ki bari kawai tym nake jira wallhy in naso samun milyan ma sai na sameshi a gurinta, khady zatayi magana wayar beeba ta fara ringing, beeba tace ke numbr da aka turo min da katin nan ne aka kira da ita,, tayi jimm kamar bazata dauka ba dan kar yace ta dawo mishi da katin, sai da ya kira sau biyu sannan ta dauka taji ance heeyyy cutie how are u, cikin rawar murya tace fyn, yace sunana Nurah Aliyu majeh, ta mike tsaye tace Nurah aliyu majeh, yace yess, tace u mean kai dan ministern abuja ne Hon Aliyu Majeh, yace yesss dear murya na rawa tace ina wuni, yace lafiya lau ya kike ya 2days, tace lafiya lau, yace gaba daya yanzu kun daina shigowa abuja, ina kawarki sanah, tace tana gidan mijinta, yace ohhh so tayi aure kai am happy 4 her, dazu na karbi numberki a gurin wani guy da yake kawo min mata in na dawo nigeria so da naga hotonki sai naji kinyi min kuma dama ina yawan ganinku a sharaton ke da kawarki, Allah yasa u are ready to spend dis wknd wv me, jiki na rawa tace why not, ko yanxu kakeso inzo ay zaka ganni, isma'il sukayi murmushi shi da saleem sannan yace no ba yau ba kin ga yamma tayi, ki bari gobe zan turo miki da transport sai kizo ko, tace ehh to Allah ya kaimu, yace ameen ina jiran account numbr bye, tace ok bye, tana kashewa ta daka tsalle ta tura mishi accnt no, murna suka dinga yi da khady, beeba ta dinga godewa Allah da yasa tace sanah tayi aure da tasan sanah zaice yana so saboda kyanta, tana cikin wannan tunanin taji alert na 30k, wani ihun sukayi ita da khady harda rawa dan a ganinsu banza ta fadi, wanka tayi ta dau atm zata banki da kasuwa siyo turaruka da kayan mata, su beeba anga masu gidan rana Mrs tijjani shattima... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: Aysha Ya'u Kurah: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 6⃣3⃣ By Aysha Ya'u Kurah Zaune suke a harabar cikin gidan cikin wata yar bukka suna hirah, feenah ta fito musu da juice ta zauna itama suna hirar tare tanata basu labarin ban dariya, horn sukaji anyi da sauri mai gadi ya wangame gate din wata bakar glk350 ta kunno kai cikin gidan, da sauri feenah ta mike ta karasa gurin tana fadin yaya mukhtar oyoyo ya karasa parking ya fito ya rungumeta yana murmushi yace feenah ya kk, tace am fyn broo ta dauki jakarshi dake cikin motar ta wuce ciki tana murna, saleem da isma'il suka gaisheshi ya amsa suna shiga cikin gida yace irin wannan zuwan na bazata iloli, isma'il ya sosa kanshi yace wallhy kuwa aiki ne ya kawo mu, dai2 lokacin suka shiga parlor, yace aikin me kuma, suka zauna isma'il yace wani case muka zo yi a kaduna, muna sa ran komawa daga an gama in shaa Allahu, Mukhtar yace okk Allah ya taimaka case din menene, isma'il yace wallhy case din kisan kai ne yau saura 5dys a koma kotu amma har yanzu bamu da kwakwarr shaida ko guda, mukhtar yace Allah ya fitar daku, kwanan nan kisan kai kawai akeyi ko ina a fadin nigeria last three weeks da suka wuce ma an kashe alhj hasheem marafa, mutuwarshi tayi touching dina sosai saboda ana gobe zai mutu we met a england yaje duba lafiyarshi ranar ma na fara ganinshi, mutumin kirki wallhy, saleem ya kalli isma'il suka hada ido, ismo yace yaya case din da mukeyi kenan abun akwai rikitarwa sosai, yanzu haka wacce ake zargin ta kashe shi ita muke karewa, ya gyara zamanshi yace wallhy yaya abun akwai rudu a cikinshi nan suka warware mishi komai har dawowar da yayi mummy ta tambayeshi yace damuwarshi akan matar danshi ne, da kuma wayar da yayi wa sadeeq duk saida suka fada mishi, mukhtar ya gyara zamanshi cikin rudu yace wait isma'il u mean matan shi dan nashi biyu ne, saleem yace eh biyu ne amma bai fadi wacce yake nufi ba, kuma sai akayi sara a akan gaba dan a ranar aka samu nasarar kashe shi abin da yasa aka karkata abun kanta saboda ita tayi girkin kuma dayar matar tashi bata kasar wannan dalilin ne yasa gaba daya aka daura kisan a kanta, sann-- wayar isma'il ta shiga kara numbr beeba ya gani ya mike dan ya tabbatar ta iso yayi ma saleem alama da ido yace bari inje in dawo yaya dan aramin motarka, mukhtar ya mika mishi keyn da sauri yana son jin karashen labarin, isma'il ya karbi keyn har ya fita ya dawo ya wuce daki ya fito da jaridar da suka sa aka nemo musu ita saboda zata taimaka musu yasa kai ya fita daga gidan, mukhtar ya kalli saleem yace ina jinka, saleem ya cigaba da bashi labarin yadda akayi mata sharrin zinah kuma aka ce dan ya kamata tanayi ne yasa ta kasheshi,, mukhtar ya share gumin da ke fita a fuskarshi yace yanzu ita dayar matar dan nashi fa, sun rabu ne ko kuwa, saleem yace a'a suna tare, mukhtar ya boye tashin hankalinshi yace to Allah ya bayyana gaskiya bari in dan huta inci abinci dan madam tun dazu take ta safa da Marwah saboda ta janyeni daga sauraron hira, anty husaina dake tsaye a dining room tace karka min sharri malam in zaka koma ka koma, yayi dariya ya wuce ciki... Kwanan beeba biyu a abuja banda kisan kudi babu abinda ismo ke mata, bai taba kusantarta ba saboda mugun kyamar ta da yake ji, duk lokacin da ta bijiro mishi da bukata zaisan yadda yayi ya kauce, abinda yasa abun bai damunta saboda makudan kudaden da yake narka mata, a daren ranar da suka cika kwana uku ya shigo hotel room din ya zauna yana maida numfashi, mikewa tayi cikin karairaya ta isa gabanshi ta durkuso tana shashshafashi, yayi dan tsaki ya ture hannunta, cikin tashin hankali tace lafiya kuwa, wallhy raina ne yake a bace saboda wani aikin da ya kamata ace ni nayi shi wata ta rigani ya fadi yana duba jaridar hannunshi, kallon jaridar beeba keyi itama kafin tayi magana wayarshi ta yi kara, yasa hannu ya dauka yace dad yanxu na karasa gida, daga daya bangaren saleem ya kaurara muryarshi kamar ta babban mutum yace Nurah goben ka shirya ka tafi kadunan duk yadda ake ciki ka nemi mahaifin yarinyar nan dan naji ance shi kadai gareta ka tabbatar ka bashi 100milion din da nace maka, isma'il ya ce dad nima zan kara mishi 50m saboda jin dadin abinda daughtern shi tayi, naso ace ni na kashe chief hasheem da hannuna saboda in samu ladan kawar da bata gari irinsu, ay wannan yarinyar ba karamin jihadi tayi ba dad ta rage mugun iri kaga ko an kasheta aljanna direct saboda su kansu masu shariar basu san waye hasheem marafa ba, mutumin da zai yanka jariri ba tausayi yaci namanshi, ay da tun da wuri nasani bazan taba yarda a kama yarinyar ba amma gobe da kudi masu tarin yawa zansa a kori shariar kuma in bata makudan kudi na ban mamaki wanda ba tun yau ba nayi alkawarin duk wanda ya kashe alhj hasheem zan bashi, daga daya bangaren akace goben ka fita da wuri dan mu samu nasarar korar karar kafin a shiga kotu, sannan ka fada ma mahaifinta su bar kasar nan gaba daya, nan suka cigaba da ruda beeba da fadin kudade masu yawan gaske sannan suka kashe wayar, ta wutsiyar ido ya kalli beeba duk yanayinta ya canza saboda jin nairah, ya dan tallabo fuskarta a hankali yace baby gobe zan je kaduna, ta hadiye miyan dake bakinta tace tare zamu tafi kenan, yace anya jirana zakiyi dan so nakeyi jibi in samu full tym a jikinki dama wannan alamarin shi ya tsare ni na kasa samun lokacinki, yayi murmushn jin dadi yace yau daddyna na cikin farin ciki har yayi kyautar kudi masu yawa beeba, ni kaina saboda farin cikin da yake ciki zanyi signing blank check in bawa yarinyar nan da mahaifinta ko da kuwa 1blin zasu cire, tace waiiii gaskiya sun gama arziki wadannan, ismo yace kwarai kuwa ay burinmu ni da dad shine mu ga bayan hasheem in kuma wani ya rigamu mu bashi kudin da yafi karfin ganinshi dan ni sau uku ina atmptn kashe shi ban samu dama ba,, beeba ta shiga rudun ganin zulfah zatayi gaining akan abunda suka aikata, na farko za'a fito da ita, na biyu zunubin kisan nasu ne ita da sanah, na uku kuma shi yafi komai daga hankalinta jin irin makudan kudin da zulfah zata caska, nan da nan idanun beeba suka rufe tace nura da gaske kakeyi akan maganar kudin nan?, yace haba baby ay kinsan dai ni bana karya bari ma ki gani, ya dauki biro da check book yace kinga wannan account din akwai fin 1bln a ciki shine mafi karanci a kudade na na bankuna, signing yayi ya nuna mata sannan yace gobe ana fito da yarinyar zan mika mata muje tare in ciro mata alkawarinta, beeba taga blank check muraran gaba daya basirarta ta toshe, can wata kasa take hangota tana fantamawa cikin naira, a zuciyarta tace to meye ma na jin tsoron fadi tunda waccan ma fito da ita za'ayi a kori karar gaba daya, tayi ajiyar zuciya ta kalle shi sosai tace wata magana nake son muyi dakai, bai kalleta ba yana kallon waya yace ina jinki baby, tace to ai bansan yadda zaka dauki maganar bane ta yiwu ka karyata ni, ya mike tsaye ya isa wata kusurwa a cikin dakin yace ina zuwa baby, yana zuwa ya manna camera ya saita ta sosai inda suke, ya dawo ya zauna ba tare da tasan abun da yayi ba saboda kankatar camerr, dagota yayi sosai ta inda fuskarta zata haska sosai, sannan yace ina jinki baby, tace amm dama sai kuma tayi shuru, yayi mata peck a kumatunta yace go ahead fadi koma meye kinsan zanyi miki, tace maganar wadannan kudin da kake cewa zaka bawa yarinyar da tayi kisan nan, ya yi murmushi yace kwarai zan bata ke in takaice miki goben nan ni da lawyern dad dina zamu tafi kaduna ko nawa ne sai mun kashe yarinyar nan ta fito kuma mu bata kudin da zasu bar kasar nan ita da dad dinta, beeba tayi murmushi tace yanzu fa in nace maka ina da hannu a kisan nan sai kace karya nakeyi dan kudin da zaku bayar ne ko, yace yess karyata ki zanyi mana tunda me zai kaiki gidan har ki samu damar zuba mishi guba, beeba tayi murmushi tace to bari dai in daina kumbiya kumbiya wallahi kaji na rantse maka ko, yace eh, tace ko alqurani aka bani zan dafa ba karya zan fada ba, yace uhum inajinki, tace wallhy akwai hannuna a cikin wannan kisan, yayi dariya yace babyna bansanki da kar ya ba ya akayi har kika shiga gidan duk irin tsaron dake ciki, tayi murmushi tace ni kawar matar danshi ce, yace u mean ke kawar wacce tayi kisan ne, tace a'a ba ita ba kawata sunanta sanah, wallhy waccan bata san komai ba, isma'il dake Zaune a gurin da saleem dake kallo tru laptp suka dinga adduar Allah ya cigaba da ingiza zuciyarta ta fada, Allah ya kara dode mata basira ta fadi komai, isma'il yace yanzu baby kina nufin kune kuka kashe shi, ta kara gyara zama tace yess, yace wow kuma yayi ruining life dinku kenan kamar yadda yake ma mutane, tace eh to kawata yaso yasa a koreta a gidan, kuma sannan she hate wannan kishiyar tata saboda mijinta ya juya mata baya saboda ita, nan ta fara rattafo labarai bata rage komai a ciki ba sai na wayar da aka kawo hoton zulfah tsirara dan bata da idea akan wanda ya aikata, nan da nan saleem ya katse camerar daga lptop dinshi, shi kuma isma'il rungumeta yayi yace wow gaskiya kin biya ni baby, ya dauki blank check ya mika mata jikinta na rawa ta karba,, ya kira saleem yace dad ashe ba yarinyar da ake zargi bace tayi kisan yanzu haka ma muna tare da wacce tayi kisan, saleem cikin fada yace haba nurah ya zaka yarda da maganar mace alhalin ga wacce kowa yasan ita tayi kisan, beeba jikinta ya fara rawa dan taga samu kuma zata ga rashi ta bude murya tace wallhy dad mune wallhy bazan yi maka karya ba, isma'il yace sune dad tunda ta fada baza tayi karya ba, saleem yace to indai tanaso in yarda sai na ga evidence a gurinta tace wallhy zan kawo maka nurah wallhy akwai wayar da nayi text da ita ko ita zata gasgata zance na, isma'il yace dad ka yarda da ita dan baza tayi min karya ba, yanxu dai muyi watsi da maganar yarinyar da ke kulle a yanke mata hukunci kawai kaga sai mu ba su beeba kudin ko, yace ohk to ba matsala yanxu dai zuwa gobe sai kuje da ita ka ciro mata na wajen nawa, isma'il yace ohk dad yanzu haka ma na bata blank check bari in bata 50k kafin goben, beeba ta tafi duniyar tunanin wai itace yau a dare daya ta mallaki makudan kudi, tayi murmushi tace wallhy ko sanah bazan fada mawa ba sai dai taga ina juya dala, ta dinga tunanin kasar da zata ta sakata ta wala, isma'il ya kalleta yace baby gashi bari inje in dawo zuwa gobe sai muje in ciro miki na gurin dad ko, beeba tace to gaskiya nagode da ka yarda dani, yace ay mu ke da godiya saboda u hlpd us alt, tayi murmushi ta raka shi bakin kofa ta juyo tana ihu ita kadai... Mrs tijjani shattima.... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: [20:27, 06/02/2016] Aysha Ya'u Kurah: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 6⃣4⃣ By Aysha Ya'u Kurah Murda kofar taji anyi ta juyo da sauri ta kalleshi, yayi hanyar gurin da ya manna camera yace baby irin wannan ihun ay sai ki tara yan hotel dinnan su dauka wani abun nayi miki, tayi dariyar jin dadi tace duk cikin murna ne, ya kai bakin kofa yace ay ni yau na fiki farin ciki, ya fita yana murmushi itama ta juya tana rawa hade da tsalle, gida ya wuce yana parking motarshi mukhtar ma ya shigo da tashi, tare suka shiga cikin gidan suna hirah, zama sukayi a parlo ya dauki wayarshi ya kira saleem, ko minti biyar ba'ayi ba sai gasu sun shigo tare da feenah, ismo ya kalleshi yace wannan sarkin surutun ta dameka ko, saleem yayi murmushi ya suka gaisa da mukhtar, saida suka gama cin abinci sannan suka koma cikin parlon suna hira cikin nishadi, ismo yace yaya alhamdulillah yau Allah ya kawo mana saukin binciken nan da mukeyi, mukhtar yayi murmushin jin dadi yace kai gaskiya na muku murna, an gano wanda yayi kisan kenan, ismo yace wallhy kuwa yaya da bakinta ta fada, plan muka hada mata, nan ya kwashe labarin yadda suka hada mata plan din da yadda ta auka cikin sauki ya fada mishi,, laptp ismo ya aiki feenah ta dauko ta mike taje ta dauko ta kawo, saleem ya amsa ya kunna maganganun da beebah tayi, cikin gigita mukhtar yace sai da nayi wannan tunanin wallhy, ismo da saleem suka kalleshi cikin rashin fahimta wane irin tunani,suka hada baki suka tambaya, ya kallesu dan baisan ma maganar ta fito ba, ya dafe kanshi ya kalli feenah yace Nafee tashi ki shiga ciki, ta mike ta wuce daki, ya juyo ya kallesu yace tun ranar da kuka bani labarin nan saida nayi tunanin sanah ce wallhy, dan dai bani da wata hujjar da zan nuna muku ne shiyasa nayi shuru da bakina, saleem ya gyara zamanshi yace yaya kasan ta ne, yace farin sani ma kuwa, ya rage muryarshi saboda kar anty husaina taji shi, yace na dade ina sabawa Allah ba tare da kowa ya sani ba isma'il, kunsan dama ance komai yana da silar shiryuwarshi, to ni silar shiryuwata marigayi ne, ya fara basu labarin tun haduwarshi da beeba da sanah a kaduna har tafiyarshi england business da yayi da ita da abin da ya faru ranar da ya kamata da wani, Innalillahi wa inna ilaihir rajiun abinda saleem da ismo suka dinga fadi kenan a ransu, mukhtar yace ranar da naji mutuwarshi wallhy na girgiza matuka har mutuwar ma ta zame min ayah, na dinga tunanin yanzu da na mutu ina sabon Allah in je ince mishi me, tun daga lokacin mata suka daina burgeni duk ko da irin kawo min kansu da sukeyi, ni dai burina a kullum bai wuce Allah ya yafe min ba, saleem yayi ajiyar zuciyah yace alhamdulillah tunda har ka gane gaskiya kuma ita kofar tuba kullum a bude take ka cigaba da rokon Allah shi gafurur raheem ne, ismo yace haka ne Allah ya yafe mana baki dayan mu, ameen suka ce dukkansu sannan suka cigaba da hada shaidunsu dan tun gobe zasu tafi mukhtar kuma jibi zai iso saboda aikinshi... Lailah ce tsaye ita da farouk a kan titin waff road motarta ta samu matsala farouk ya dago kanshi yace anty bari mu bar motar nan gurin mechanics din can gurin dan pelpon dinta ya tsinke zuwa gobe sai inzo in karba, tace oh my God yanzu sai ka samo mana napep mu karasa gida dan in muka ce zamu kira a kawo mana mota zamu dade ga su saleem sun karaso ga kuma waleed yayi bacci, yace wannan ba matsala bane rufe motar sai in samo, ta karbi key din ta rufe motar ta kwantar da waleed a kafadunta ta tsaya jiran farouk, ko 3mints baiyi ba sai gashi ya dawo da me napep shiga ciki tayi shima ya shiga yace bari suje tare sai ya juyo ya mika gyaran motar, a hankali suke tafiya suna hirar nasarar da saleem da ismo suka samu, me keke napep din yayi tsam yana jinsu yanata tunanin anya kuwa ba gidan da ya taba sauke wasu yan mata biyu bane da suke ta sake saken sa ma wani guba, shuru yayi musu har suka kai kofar gidan, anty laila ta fito daga napep din tana ma saleem da ya fito daga cikin mota magana,. farouk ya fito suka gaisa ya koma napep din yace malam mayar dani muje mu dawo dan Allah, me keke napep din yace to muje, suna tafiya shuru zuciyar me napep din na kitsa mishi yayi ma farouk magana, da kyar dai suna shan kwanan layinsu me napep din yace ranka ya dade gidan nan da na saukeku rasuwa akayi a cikinshi, farouk yace eh babana ne ya rasu, yace ayya Allah ya jikanshi da rahama, amma kamar naji kuna maganar kashe shi akayi ko , farouk ya kalleshi tsaff sannan yace eh, mutumin yace Allah ya bayyana wanda ya aikata, farouk yace ameen kawai ya cigaba da kallon titi, can me napep din yace lokacin da nake drivern taxi kuwa na taba sauke wasu mata anan kofar gidan, tun daga abuja na dakko ta tazo ta dauki kawarta suna ta hirar su nidai ina jinsu, har na sauke su suna hira daga jin hirar tasu ba alkhairi bace, dan harda maganar guba naji sunayi, duk da ban gama saurarar su ba nadai san wani suke son kashewa, dan suna sauka dayar ta mika ma dayar bakin nikab tace tasa a fuskarta, in dai takaice maka har suka fito ina gefe ina kallonsu suna dariya, naso dawowa washe gari gida inji abinda ya faru a gidan dan in fadi abun da nasani saboda nasan inda na daukesu dukkansu dayar a airport din abuja tunda muka taho take waya, dayar kuma anan hayin banki, kwatsam na samu labarin mutuwar mahaifina a ranar, wucewa kauyenmu kawai nayi bayan na kaiwa me mota motarshi, saida mahifina yayi sati biyu sannan aka raba gadon mu na dawo nan kaduna na siya wannan machine din dan inci gashin kaina, ko da na dawo na bi ta kofar gidan har sau biyu to in tsoron shiga in tambaya saboda sojoji da nake yawan gani a tsaye, kar ace min dan boko haram shiyasa kawai na bar zancen, dai2 lokacin suka isa waff road yayi parking ya juyo ya kalli farouk da ya zama kamar mutum mutumi saboda mamaki, mutumin yace dazu da naji kuna magana kuma saida jikina ya bani kuma Allah cikin ikonshi sai gamu a kofar gidan, farouk yayi ajiyar zuciya yace "Hukumul lahu la azabun" a zuciyarshi yace lallai manzon Allah s.a.w yayi gaskiya, ya kalli me napep din yace malam da gaske kake fada min wannan maganar, mutumin yace alkur'an ba karya nakeyi maka ba, to ribar me zanci in nayi maka karya, farouk ya sauka sauri2 yace ina zuwa dan Allah, karasawa yayi ya danka wa kanikawan motar yace gobe zaizo sai ya fadi kudin aikinshi, da sauri ya shiga napep din suka wuce ji yakeyi kamar yayi tsuntsuwa ya ganshi a gida, suna isa ya kira anty laila yace tana ina ne, tace ya shigo ciki suna ciki da su malam saleem, da sauri yace malam kashe machine dinka kazo muje, gaban me keke napep ya fadi yace bawan Allah babu abin da za'ayi min dai ko, farouk yayi dariya yace ay malam ka zama dan gida dan Allah shigo muje, ya kashe napep din ya shiga addua har suka karasa cikin parlon, basu tarar da kowa a parlon ba farouk yace mishi ya zauna yana zuwa, dakin anty laila ya shiga bata ciki, ya kirata a waya tace ya zagayo suna garden.. Bayan sun gama sauraron mati drivern taxi cikin farin ciki anty laila tace karya fure take bata ya'ya, gaskiya duk wanda ya rike Allah da manzonsa to wallhy bazai tabe ko ya dawwama ciki bakin ciki ba, kun ga ikon Allah cikin kankanin lokaci shaidu sun kewaye mu har sunyi mana yawa, isma'il yayi dariya yace irin wannan dabaibayin da sukayi ma zulfah ay wadannan shaidun basuyi yawa ba anty, saboda in an ki wani dole a yarda da wani, farouk yace hakane Allah ya kara taimakon mu.... Abba ya kamata kaje ka duba yarinyar nan ko dan cikin da ke jikinta, ka daina barin zuciya tana rinjaye akan ka daga baya kazo kana dana sani, ya dago kanshi ya kalli mummy yace wallhy mummy zuciyata ta kasa barina inje gurinta, kullum ganin ta nakeyi wacce ta rabani da farin cikina, mummy shaidun nan sun isa mutum ya gasgata wannan alamarin, wallhy ko kadan bana son adinga min maganarta, farouk dake zaune yana latsa waya ya maida earpiece kunnenshi ya fara bin wakar da karfi ya mike yana jan kumatun afrah dake homework, mummy ta harareshi tace umara wai kai meke damunka ne duk ka canza, yaro sai kace wanda yake kora wani abu, sadeeq yayi tsaki yace wallhy kuwa mummy tunda suka hada kai da anty lailah suna shirme wai suna bincike shikenan suke ji kamar ana kada su da ruwan hanji, farouk yayi dariya yace a gurinka ne shirme mudai muna gayyatarka kotu gobe saboda muyi maka tambayoyin mu na shirme, Sadeeq yayi tsaki ya harareshi yace to ba sai kaxo ka daukeni ka kaini ba, farouk yace oho dai kuma wallhy idan mukayi nasara ba karam--- muryar nurain ta katseshi, ya dan duka yace ina wuni yaya, nurain yace lafiya lau farouk, ya kalli mummy yace keyn dakin daddy zaki bani akwai wasu takardu da zan dauka, tace to ta mike tana hararar farouk, Binciken takaddun yakeyi mummy na tayashi, cikin drawrr kayanshi mummy ta bude taga diary da wata takadda a saman shi, idonta ya ciko da kwalla ta kalli tsohn diaryn ta dauko shi hade da takardar, zama tayi tana duba rayuwar da sukayi tare ta kunci da ta dadi har zuwa auren hadiza mummy duk inda ta bude sai ta zubda hawaye, rubutun da yayi a karshen diaryn shi ya daga mata hankali, ta dinga binshi tana maimaitawa, *** ga abin da ke cikin diaryn,, Innalillahi wa inna ilaihir rajiun, Yau alhamis 29 aug ta zame min ranar bakin ciki a rayuwata, ranar da mantata a gurina abu ne mai matukar wahala sakamakon kama matata Hadiza da cin amanata, zuciyata bazata iya daukar wannan bakin cikin ba dan bansan shekarun da ta dauka tana cin amanata ba, Allah na gode da baka sa muna rabo tare da ita ba,kuma a kullum ina rokonka ka fitar da gurbatattun iri a cikin zuri'ata.. Mummy jikinta na rawa ta dauki takaddar ta fara karantawa, Ni Hasheem na saki matata Hadiza saki uku abisa cin amanata da tayi, can kasa signing dinshi ne da date din da yayi, mummy ta dukunkune takardar tana tunani cikin tashin hankali a zuciyarta tace on 29 ciwonshi ya tashi washe gari ya tafi england, kenan wannan shine dalilin tashin ciwonshi, nurain ya dafata ta dago a firgice yace mummy tunanin me kikeyi tun dazu nake ce miki na gansu, tace hmmm sannan ta mika mishi takardar, cikin tashin hankali nurain ya gama karanta takaddar, ya kalli mummy yace mummy yanzu ya Za'ayi, tace kaidai bari duk na rikice nurain Allah ya kaimu gobe..... Mrs tijjani shattima.... [22:00, 06/02/2016] Aysha Ya'u Kurah: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 6⃣5⃣ By Aysha Ya'u Kurah ****10th October *** Tun asuba anty amarya da sanah ke zaune suna sake sakensu suka kira bamba da maimzy akan kar su yarda su tsorata, su dake sosai kar wata tambaya ta basu tsoro saboda har yanzu a ganinsu laila bata da wata kwakwarar shaida, sai gurin takwas suka rabu cikin farin cikin sanah ta wuce dakinta ta tarar da sadeeq na bacci ta shiga wanka ta shirya tana zaman jiranshi ya tashi ya shirya su tafi kotu,, karfe 10 kotun ta cika makil, kowa na zaune wasu sunyi jugum wasu kuma suna hirar ko yaya wannan rikitacciyar shari'ar zata kaya oho, Barr saleem, laila, da taheer suna zaune guri daya, laila ta kalli agogo karfe 10:05 yace saleem isma'il har yanzu bai karaso ba gashi yanzu alkali zai shigo, saleem ya kalli kofar shigowa kafin yayi magana ya hango ismo tafe rike da hula a hannunshi, karasowa yayi ya mika ma taheer hannu suka gaisa ya zagayo gurin da su saleem suke a hankali yace an gama tana can na bada gadin ta gurin yan sanda, anty laila tayi dariya tace shegiya lashe money tana tunanin zuwa bank sai ta ganta a court, ismo yayi dariya yana waige2 ya daga ma farouk hannu ya zauna, shigowar alkali ne yasa aka samu nutsuwa a kotun, Da bismillah ya fara kamar yadda ya saba, sannan ya bukaci a gabatar da jadawalinsu ba tare da bata lokaci ba, bayan introduction na lawyers "saleem da Tahir" sai mai gabatarwa ya mike ya gabatar da shari'ar da za'a cigaba na zulfa'u Adam, alkali yace batare da bata lokaci ba zamu fara wannan shariar da ta zama karashe, a shigo da mai laifi, aka shigo da zulfa'u da kamanninta suka canza saboda damuwa da rashin cin abinci, alkali yace barr tahir bismillah, tahir kurah ya mike yace ya mai shari'a ni bani da wata shaida da ta rage in gabatar saboda tun zaman farko na gabatar da shaiduna masu karfi wanda ya kamata ayi musu duba sosai sannan a bi wa wadannan bayin Allahn hakkinsu, saidai idan daya bangaren sun gabatar da nasu shaidun ina iya yi musu tambaya, nagode ranka ya dade, sai da aka dau mintina biyu sannan alkali ya dago kanshi yace barr saleem shin kun tanadi shaidun da zaku gabatar a kotu, barr saleem ya mike bayan ya shafa adduar da ya dade yana yi, sannan ya fara da bismillah yace ya mai shari'a kamar yadda kotu tasani ba dani aka gabatar da shariar farko ba, amma in shaa Allahu daga yau za'a kareta dani bi iznillahi ta'ala, zanso a bani dama in gayyaci sadeeq mijin zulfa'u saboda akwai wasu tambayoyi da zan mishi, alkali yace an baka dama, sadeeq ya mike ya isa gurin yana kallon zulfa'u da kanta ke kasa, bayan gabatar da suna da rantsuwa, saleem yace malam sadeeq ka fadi da bakin ka cewa mahaifinka ya kiraka a ranar da zai dawo, ko zamu iya sanin abinda ya fada maka, sadeeq ya kara hade rai dan duk ganinshi shirme sukeyi yace ya tambayeni ina matata,? saleem yace muna ji kai kuma wace amsa ka bashi, ya saci kallon zulfa yace lokacin muna tare da ita nace gata nan, sai yace min dayar fa,? saleem yace dakata sadeeq, ya juya yana kallon alkali yace ya mai shar'ia marigayi ya kira sadeeq ya tambayeshi ina matarka, be ce ina matan ka ba matarka kadai yace, da sadeeq yace mishi gata nan in da ita yake nufi bazai tambayi dayar ba, sai yace ina dayar dat means akwai wani abu da yake son fadi game da ita dayar matar tashi tunda har ya tmbayi ina take, ya maida kallonshi gurin sadeeq yace uhum a lokacin sai kace mishi ne, sadeeq cikin kosawa yace lokacin bata kasar nan tana india jinyar mahaifiyarta, saleem yace yauwaa mun gode malam sadeeq, ya juya yace ya mai shar'ia a rike wannan gurin dayar matarshi tana india jinyar mahaifiyarta, yace na gama tambayoyina akan sadeeq ya mai shari'a ban sani ba ko abokin aikina yana da ta cewa, alkali ya tambayi tahir yace a'a babu, sannan aka bukaci yaje ya zauna, saleem yace ya mai shari'a wacce zanyi ma tambaya ta biyu mahaifiyar sadeeq ce itama a wannan daren da mijinta ya dawo cikin damuwa ya fadi mata damuwace akan matar abba, har a lokacin bai ce matan abba ba, kuma gida daya yake da zulfa'u a ranar da ya dawo sun gaisa dashi sosai cikin farin cikin ganin surukarshi, in da ita yake nufi ya mai shari'a ay bazai ki fadi ba tunda gata a gabanshi, sannan yanzu zan kira wacce zanyi wa tambaya ta uku itace amaryar marigayi, anty amarya da bata dade da shigowa gurin ba ta karaso ta tsaya, saleem ya kalleta yace sannu anty, tace yauwa, yace anty ko zaki iya fada mana ranar da marigayi zai dawo kema ya kiraki kan maganar matarshi, ta girgiza kanta tace bai kirani ba, yace okk may be bai sameki bane ko kuma kema a ranar kina india gurin jinya, cikin rashin fahimta tace jinyar wa?, sanah cikinta ya saki sosai kiris ya rage fitsari ya fito, saleem yace jinyar yayarki mana, ko bakisan bata da lafiya ba, anty amarya tace gaskiya ban sani ba, saleem yace wow abun mamaki har yar uwarki ciki daya tayi ciwo baki sani ba, to duk ba wannan ba, ranar da abun zai faru ko zaki iya gaya mana inda matar sadeeq take? bafa zulfah ba, diyarki nake nufi, anty amarya tace ita bata kasar ma ta tafi dubai sarin kaya, sanah fitsarin dake rike a mararta ya fito da karfinshi gumi kota ina keto mata yakeyi, saleem yace iyye ashe business woman ce, to ya mai shari'a kaji dayar matar tashi dubai taje sarin kaya sai a hada shi da amsar mijinta a basu mazauni sosai a takadda saboda zata amsa su da kanta bayan nayi tambayar da zanyi ma wani yanzu, ya juya yace barr ko kanada tambaya ko jaa, tahir ya girgiza kanshi cikin rudu, saleem yace to anty mun gode zamu bukace ki anjima, ya mai shar'ia ina son a bani dama in shigo da wata shaidar , alkali yace an baka, aka fita aka shigo da mukhtar wanda ganinshi kadai yasa duk gabobin jikin sanah suka rike guri daya, Bayan tambayar suna da rantsuwa, saleem yace malam mukhtar ko kasan waccan ya nuna sanah dake zaune ta kura ma mukhtar ido, mukhtar yace farin sani ma, saleem yace a ranar 3 ga watan sept ko zaka iya fada min kana ina, mukhtar yace ina england tare da waccan yarinyar, sanah tasa ihu tace wallhy sharri yake min na rantse da Allah so sukeyi a kama ni, ni ban sanshi ba, alkali ya buga tebur yace baiwar Allah nan kotu ce ba gurin rashin da'a ba, ya kamata kisan irin maganganun da zakiyi, barr saleem ya kalli mukhtar yace ko xaka ita takaita mana labarin abinda ya kaiku england, nan da nan ya warware mishi komai har hoton da sukayi sai da ya taho mishi dashi sannan ya fada musu abinda ya hadasu fada har daddy ya shigo ya ji su, Innalillahi wa inna ilaihir rajiun abun da sadeeq da rabin mutanen gurin ke fadi kenan, da kyar aka samu nutsuwa sannan saleem yace ya mai shar'ia wadannan tambayoyin da nayi sune mafarin tafiya a cikin wannan shari'ar yanzu muna cikin binciken kasa uku kenan bamu san wacce kasa bace gaskiyar inda matar sadeeq taje INDIA, DUBAI ko ENGLAND, wannan amsar daga bakinta kadai zamu ji, sannan mu shiga cikin shariar ka'in da na'in nagode ya mai shari'a, Hutun rabi awa aka bayar ni kuma na kashe wayata nayi hanyar waje in nemo abin da zanci dan naji dan cikina na neman galabaita saboda yunwa, sai na dawo karasa dauko rahoto Mrs tijjani shattima.. [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: [18:05, 07/02/2016] Aysha Ya'u Kurah: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 6⃣6⃣ By Aysha Ya'u Kurah Bayan dawowa daga hutun rabin awa can na hango sadeeq ya dafe kanshi cikin tsananin rudu da tashin hankali, to ba sadeeq ba ma mijin sanah daukacin mutanen gurin suna zaune sun zuba mata ido cike da mamaki, sanah kuwa duk jikinta a jike yake tabbas da ta samu koda karamar kofa ce agurin to da babu abinda xai hanata gudu... Alkali ya fara magana cikin nutsuwa yace bayan hutun rabin awa yanzu zamu cigaba da gabatar da shari'a, barr taheer ko kanada jaa akan tambayoyin barr saleem, barr tahir ya mike yace bani da jaa ya mai shari'a amma wadannan tambayoyin da saleem yakeyi ko kadan basu cikin shariar da mukeyi, tambayoyi ne yake yinsu a bisa son zuciyarshi saboda rashin kwakwarar hujjar da zai fitar da wacce ake zargi, ko ma wace kasa sanah taje tunda har an tabbatar da bata kasar samm bai kamata ma a sako ta acikin wannan zancen ba, ya mai shari'a bisa la'akari da rashin shaidar da zata gamsar damu da kai nake rokon wannan kotu da tayi saurin yankewa mai laifi hukuncin da ya dace, tambayoyin da saleem yayi kuma wannan shari'a ce da zasu yi ta a gida ba anan ba, Alkali ya kalli taheer yace munji korafinka barr tahir, barr saleem bismillah, barr saleem ya mike yace ya mai shari'a zanso a bani dama inyi wa zulfau wasu yan tambayoyi, alkali yace an baka, ya fito ya karasa gurin zulfa yace malama zulfa'u ina son ki bude bakinki ki amsa min tambayoyin da zanyi miki , amsar tambayoyin sune zasu bamu saukin gabatar da shaida, zulfa ta gyada kanta, saleem yace ko zaki iya fada mana yanayin tsaftar ruwan da kikayi amfani dashi gurin dama kunun, zulfa a hankali tace tsafatatacce ne dan ko da na gama damawa sai da nasha, yace to bayan kin ajiyeshi a gurin ajiyar abinci babu kowa cikin gidan, tace eh babu kowa a ciki ni kadai ce, yace kuma har lokacin dawowar mutan gidan baki ga kowa ya shigo gidan ba saboda masu gadi sunce wasu mata sunzo gurinki, zulfa tace ina daki bayan na fito daga wanka sai naji ana buruntu a gurin dinning sai na fito dan nayi tunanin ko su mummy sun dawo ne, ko da na fito sai banga kowa ba na leka ta window sai na hango beebah kawar sanah kuma itama ta ganni, sai na koma na dauki wayata dake kan dinning na wuce daki dan a tunanina ko gurin anty amarya tazo, saleem ya juya ya kalli alkali yace ya mai shari'a zulfa'u taga kawar sanah a gidan, kuma masu gadin gidan sunce mutum biyu ne suka shigo neman zulfa'u kenan beeba ce ta zama biyu ko kuma dai tare suke da wata wacce ita zulfa'un bata ganta ba, wannan amsar inason jinta a bakin masu gadin ya mai shari'a amma ba yanzu ba sai lokaci yayi, yanzu dai in an bani dama inason inyi wa sanah wasu yan tambayoyi, sanah da idonta yayi ja rike da waya tana neman beeba ta mike ta karaso a hankali kamar wacce kwai ya fashe ma aciki, a zuciyarta tana fadin ya akayi shari'ar nan ta juye haka, kwarin gwiwa ta samu da ta tuna zata iya karyatawa tunda babu beeba a gurin, malam saleem ya kalleta bayan fadin suna da rantsuwa yace malama sanah a ranar da abun nan ya faru ko zaki iya fada mana kina ina, sanah ta share gumin fuskarta tana kallon sadeeq da anty amarya sannan ta dake tace ina india jinyar mahaifiyata, malam saleem yace wayyo Allah ya bata lafiya amma yanzu ta ji sauki ko, sanah ta gyada mishi kai, yace to da taji sauki ne sai kika wuce sarin kaya dubai, ko kuwa ya akayi, sanah ta daburce tace ehh dama inada shirin tafiya dubai sai kuma ciwonta ya tashi shine na tafi da niyyar in taji sauki sai in wuce, saleem yace amma ciwon na sirri tayi saboda kar wani ya sani ko, sanah tace ban ganeba, saleem yace abunda nake nufi ciwon nata babu wanda ya sani sai ke ko, sanah tace eh bata son a daga hankalin mutane ne shiyasa, saleem yace Allah sarki,, ko zaki iya kira mana ita a waya mu gaisheta, sanah jikinta ya fara rawa ta fara kame kame, tahir yace objection ya mai shari'a ya kamata mai tambaya ya daina ruda wacce yake tambaya ta hanyar tursasawa, saleem ya kalleshi yace laifi ne dan musulmi ya gaida mara lafiya, ya mai shari'a in akayi la'akari da zunzurutun ladan da ake samu in aka gaida mara lafiya inaga ya cancanta a kirata mu gaisheta dukkanmu har da kai ma dan mu samu ladan gaba daya ko ba haka ba ya mai shari'a ya karasa fadi yana ma tahir murmushi, anty laila dake zaune kanta yayi girma ta kasa magana saboda kwarewar aiki irin na saleem tayi murmushi tace aiki ga mai kareka, alkali yace korafi bai karbu ba barr tahir, barr saleem cigaba, saleem yace nagode ranka ya dade, ya kalli sanah yace kin kirata, sanah tace wayata babu charge, saleem yace to ay kin haddace numbr akanki ko, ko dayake ma barshi ga sadeeq bari mu kira da wayarshi, saleem yace malam sadeeq ko zaka iya kira mana surikarka mu gaisheta, sadeeq baiyi magana ba ya zaro wayarshi yayi dialing ya mika ma saleem, saleem ya karba wayar ya dawo gaban alkali yasa ta a speaker, ringing uku wayar tayi ta dauka cikin muryar isa tace sadeeq ina gajiya, sanah ta fashe da kuka hade da toshe baki, saleem yace lafiya lau mama kin dawo lafiya ya jikin, cikin rashin fahimta maman sanah tace sadeeq dani fa kake magana jikin wa kuma ina naje, saleem yace ance min baki da lafiya ne kun tafi india tare da sanah, tace a'a ni lafiyata kalau ba kuna tare da sanah a England ba ko kun dawo ne, saleem yayi saurin datse wayar yace ya mai shari'a da fatan kaji abinda mara lafiyar ta fadi ko, ya kalli sanah yace malama sanah nidai na shiga rudu gaskiya, na kasa gane wacce kasa kikaje tsakanin india, dubai , ko England, dan Allah ki fitar damu cikin duhu, sanah kukanta ya tsananta tace sharri zakuyi min wallhy wannan ba muryar mahaifiyata bace, to ma ina ruwanka da inda naje kayi bincikenka akan wacce kake tuhuma mana ni meye nawa a ciki tunda kowa ya tabbatr bana kasar, saleem yace oooo hakane fa, dan Allah kiyi hakuri na wuce gona da iri to bari inyi miki tambayar da ya kamata inyi miki, shin ko ke kika aiki kawarki beeba gidan a ranar tunda dai babu wanda take mu'amala dashi a gidan sai ke, sanah tace karya zulfa'u take ma beeba dan ta daura mata sharri itama bata kasar sanda abun ya faru kuma har yanzu ma bata dawo ba, saleem yayi murmushi yace to Allah ya dawo da ita lafiya, har yanzu dai ban gama dake ba, ya kalli mai sharia yace ya mai shari'a inason in gabatar da wata shaidar in an bani dama, alkali yace an baka, saleem yace ina son a kira min mati drivrn taxi, cikin minti biyu mati dan kauye ya hallara gaban kotu, bayan yayi rantsuwa saleem yace malam mati ko kasan wannan, ya kalli sanah yace kwarai na taba daukota daga airport din abuja zuwa kaduna, saleem yace to da kuka zo a tasha ka sauketa, yace a'a hayin banki mukaje muka dauki kawarta, nan ya kwashe duk labarin ya fada musu, sanah cikin kuka tace ya mai sharia wallahy karya yakemin wallhy ban taba ganinshi ba hadawa sukayi dan a kulla min sharri, wallahy karya suke min, dakyar mai shari'a ya iya sa sanah tayi shuru sannan ya tambayi tahir ko akwai tambayar da zaiyi ma mati, tahir yace babu amma ya mai shari'a daga jin wannan ansan shiryayyen plan ne, barr saleem raina ma kotu hankali kawai yakeyi dan har yanzu bai kawo mana shaidar da zamu gamsu ba, saboda haka ina rokon kotu tayi watsi da wannan shaidar.... Mrs tijjani shattima.... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: [18:23, 07/02/2016] Aysha Ya'u Kurah: ◆◆ZULFAH ◆◆ 6⃣7⃣ By Aysha Ya'u Kurah Alkali ya kalli tahir yace munji korafinka barr tahir, barr saleem cigaba, saleem yace ya mai shari'a ta yiwu wannan shaidar ba tayi karfin da za'a kori wannan shari'ar ba saboda yanda zamanin nan ya canza mutane zasu iya rantsuwa da alkurani akan karya kamar yadda mati yayi yanzu a gaban kotu, zanso kotu tabani dama in gabatar da shaida ta gaba isma'il Musa, alkali yace an baka, yace nagode ya mai shari'a, ismo ya mike ya dauko laptp dinshi ya fito ya tsaya bayan ya fadi sunanshi da rantsuwa, sannan ya fara bayanin haduwarshi da beeba sannan ya bukaci a jona flash din da ya ciro a jikin lptp dinshi a katon plasman dake court room din, cikin minti 5 aka hada komai kowa ya nutsu yana son sauraro da ganin abinda ke ciki, mamaki ya bayyana a fuskokin mutanen dake gurin musamman anty amarya da ko ina na jikinta ya dau rawa babu kakkautawa, tabbas su laila a shirye suke yau babu mai fitar dasu a gurin nan, bayan an gama sauraron bayanan beeba, sanah ta kara sa ihu murya na rawa tace wallhy wannan hadin computer ce in gaskiya ne ina beeban take, ta kalli saleem tace wai me na tsare maka ne da kake ta hada min wannan sharrin, ya mai shari'a wallhy wannan aikin computer ce,, saleem yayi murmushi yana kallon yadda jikinta ya jike da hawaye, yace ya mai shari'a babu mamaki wannan computer ce in akayi la'akari da yadda ilmin yanar gizo ya yawaita a wannan zamanin da muke ciki yanzu, amma xanso a kara bani dama ta kusa da karshe domin in gabatar da wata shaidar, mai shari'a cikin mamakin kwarewa da confidence irin na saleem yace an baka dama barr saleem, barrister saleem ya kalli ismo ya mishi alama da ido ismo ya fita yaje gurinsu beeba dake kuka tun shigowarsu, ta kalli ismo tace nurah ni zaka ma haka, ni zaka yaudara, yayi dariya sosai yace ke wai baki da fahimta ne, isma'il nake ba nurah ba, yace ma yan sandan su wuce da ita, sukayi gaba ismo ya bisu a baya,, sanah na ganin beebah ta lankwashe kanta gefe daya tace shikenan na mutu, ta toshe bakinta ya'yan cikinta suka fara karo da juna, kusa da sanah aka tsayar da ita, cikin muryar kuka beeba tayi rantsuwa sannan saleem ya fara mata tambayoyi, ta fara kame kame tana kuka, ta sadakar a ranta kawai gara ta fadi gaskiya may be ta samu sassauci tunda ba ita ta zuba ba, Wani wawan naushi sanah ta kaima beebah a baki bayan ta gama bayani, tace karya kikeyi wallhy yaushe kika ganni, beebah ranta ya baci sosai suka cakume juna suna masifa suna tonawa junansu asiri, da kyar aka samu aka rabasu dukkansu suna kuka sosai, saleem yayi murmushi ya kalli sanah yace anty wannan ma ki dubata da kyau babu mamaki fuska muka sa mata dan mu muki sharri, ya rage murya yace har yanzu kin kasa fada mana gaskiya da bakinki ba, duk ko da irin kwararan shaidun da muka gabatar, meyasa kika kashe shi,? meyasa baki tsaya kinyi tunanin duk wanda ya kashe mui'mini jininshi baya barinshi yayi kwanciyar hankali ba, meyasa baki tsaya kin roki gafararshi ki tuba ki koma ga Allah, babu mahaifin da zaiso raba danshi da matarshi menene aibu a cikinshi in kika tuba kika koma ga Allah kika rungumi mijinki da gidanki kikayi watsi da duk wasu abubuwa da kikeyi marasa kyau, meyasa kika zabi maida yayanshi marayu, meyasa?? Sanah ta fashe da kuka ta hada hannunta guri daya tace wallhy sharrin shaidan ne da rudin zuciya, dan Allah kuyi hakuri, hayaniyya ta kaure a gurin duk kokarin da alkali yayi akan ayi shuru amma abun yaci tura saboda masu Allah wadai da halin sanah, saleem ya kalli alkali yace ya mai shari'a shaidun sun gabata a gaban ka kuma sannan itama ta amsa da bakinta, yanzu kawai abun da ya rage min daga shi zan barka kayi naka shine a gayyato min wacce tayi ikirarin ita kawar zulfah ce da kuma saurayin nata, anty amarya ta sulale kasa saboda tsananin rudu tace yau na shiga uku, ganin an shigo da su maimzy suma suna zare ido yasata boye kanta a kasan kujera, saleem ya kalli maimzy yace aminiyar zulfah barkanki da warhaka, murya na rawa tace barka dai, yayi murmushi yace tooo maimzy yanzu dai kinji yadda sharia ta juya ko, maimzy ta hadiye miyau tace eh, saleem yace to yaya abun yake kiyi min bayanin yadda akayi shariar ta juye yanzu, kafin ki ce komai ina so in tunatar dake wani abu, rayuwar duniya ba matabbata bace, yanzu nan gaki a gabana in lokacinki yayi zaki mutu, karki ga Allah na ara miki lokaci kice zakiyi duk abinda kikaga dama, zaki iya gama fadin abinda zaki ce yanzu Allah ya amshi rayuwarki kinga kinyi pleasn wasu a duniya zaki je lahira ki tadda azaba mai radadi, kiji tsoron haduwarki da Allah ki fadi abinda kika sani saboda shaidarki bata da wani tasiri a wannan shariar ko kin fadi karya ko gaskiya bazaki canza shaidun baya ba saboda haka gara ma ki fadi gaskiya ko Allah zai yafe miki sharrin da kikayi a baya, jikin maimzy yayi sanyi sosai a hankali tace wallhy ban taba ganin zulfah ba tun da nake a rayuwata, ina zaune a daki bamba yazo min da kudi yace wai zamuyi wani aiki, ganin zunzurutun kudi har 200k yasa na amince ya fada min so yakeyi muje wani gida mu bada shaidar karya akan wata yarinya, bayan ya gama min bayani ya dauko ni ya kawoni gidan lokacin ana zaman makoki, muka shiga dakin matar da tasa shi aikin tayi min bayanin komai sannan suka yi waya da bamba, ni dai waya kawai suka bani da hoton da suka hada nawa ni da bamba aka cire fuskata aka sa ta zulfah, anan ta kara min dubu 100 tace in aiki ya gama kammala zatayi mana kyauta ta musamman, dan Allah ya mai shari'a kuyi min afuwa wallhy ba yin kaina bane, saleem ya juya ya kalli bamba da gumi ya jikashi yana hararar maimzy yace malam bamba yi hakuri ka daina harararta taji tsoron Allah ne ta fadi gaskiya, ka sani ko wannan ya zama sillar shigarta aljanna, yanzu ya rage naka ka karasa mana ka tafi ko kayi karya ka dawwama a prison har mahadi ya bayyana, murya dashe bamba yace duk abinda maimzy ta fadi gaskiya ne, hajiya hadiza amaryar marigayi ita ta sani, dalili kuwa shine,, ni dai kawali ne ina nemo ma manyan maza masu mulki mata in kai musu, to a wata ranar alhamis ne karfe uku na rana na kirata a waya dan ranar ne minister umar marke zai shigo kaduna dama sun saba haduwa da ita, da na kirata nake sanar da ita isowarshi nace mata muna 17 hotel, nan da nan tace gata nan zuwa to muna tare dashi da wani ashe mijinta ne ni bansani ba, bayan ta iso muka shiga dakin hotel din lokacin hon umar yana bawa mijinta labarinta, tana shigowa suka hadu da mijinta, cikin rudewa ta fita da sauri tana kuka sosai ta wuce gida shi kuma saida ya kusan awa a zaune kafin ya iya mikewa hon umar na bashi hakuri har ya rakoshi bakin mota bai iya ce mishi komai ba, bansan ya suka kare ba a gida, ni dai washe gari na kirata take cemin ay an fitar dashi england bashi da lafiya, kuma ta shiga dakinshi taga takaddar da ya rubuta mata na saki amma bai bata da hannunta ba, shine tace bazata yarda ya dawo ya bata takaddar ba saboda zata tashi a tutar babu duk irin bautar da tayi ma gidanshi, nan ta ce inzo in rakata wani guri, Gurin boka na rakata ya bata wani magani dan cewa tayi kasheshi zatayi, saboda tasan yana dawowa zai bata takaddar, a hanya ta sauke ni tace duk yadda ake ciki zata nemeni, kwana uku tsakani ta kirani da daddare tace aiki yayi kuma yanzu ta daura zargin akan wata yarinya saboda haka gobe muzo dan musan yadda zamu daure yarinya saboda binciken ya tsaya a kanta kadai, ya fara kuka yace nayi kuskuren biye ma zuciyata in aikata wannan aikin dan Allah ku yafemin, Innalillahi wa inna ilaihir rajiun shi kadai kake ji a cikin kotun, sadeeq dake zaune kanshi a daure hawaye na bin idonshi yace guba biyu kenan daddy yaci,,, sanah ma ta girgiza sosai da jin wannan jawabin,, saleem kuwa dafe kanshi yayi cikin rudun jin zancen bamba.... Mrs tijjani shattima... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 6⃣8⃣ By Aysha Ya'u kurah Kan anty amarya kallo ya koma, jalila ta mike daga kusa da ita da sauri tana kallonta, anty amarya dake durkushe a kasa tace sharri yake min jalila karku yarda da zancen shi, ya za'ayi in kashe daddy me yayi min? Magana taji a bayanta ta waiga da sauri taga wani dansanda, cikin firgici ta mike tace wallhy karya yake min, dan sandan yace karaso muje kiyi bayani a gaban kotu, anty amarya ta shiga gaba tana kuka har ta kai gaban alkali ta hade hannayenta gurin daya tace ya mai shari'a wannan mutumin karya yake min wallhy hada baki sukayi dan suyi min sharri, anty laila ta mike da sauri tace su waye suka hada baki dan su miki sharri, kin dauka kowa irinki ne wacce kullum zuciyarta ke saka sharri, waye ya kawo mana maimzy da bamba cikin gida, daga dakinki kuka fito tare kina kuka kamar dagaske, abunda baki sani ba anty shine shi sharri fa dan aike ne wallhy duk inda yaje sai ya dawo gurin wacce ta aikeshi, kawai yanzu ki saukakewa kanki kiyi ma kotu bayanin gaskiyar abinda ya faru dan da gaskiyarki da karyarki duk daya ce tunda shaidu sun gabata a gaban alkali gara ma ki fadi gaskiyar ko zaki samu sassaucin azabar da Allah zaiyi miki, Anty amarya ta durkushe tana kuka mai sauti tace na cuci kaina, nabi son zuciya na aikata ba dai2 ba, ban taba tunanin zuwan wannan ranar ba, lallai duk wanda ya dauki duniya da zafi yana cikin masifa kamar yadda na fada cikin ta yanzu, tabbas abinda bamba ya fadi gaskiyane, domin da zulfau ta gama aikin abincin sai na faki idonta kamar na fita, saida na bari ta shiga wanka sannan na fito na zuba maganin na fita daga gidan gaba daya, washe gari da naga ana bincike kuma babu mamakin bincikensu ya dawo kaina shiyasa na sa bamba ya kara dabaibaye zulfau a ciki saboda binciken ya tsaya a kanta ita kadai, sannan maganar saki tabbas nasan ya sakeni lokacin da na shiga dakinshi yana bacci naga takaddar, kafin in kai ga yagawa ya bude idonshi ya ganni da sauri ya mike yace gara da Allah yasa kika gani da kanki dauka kije Allah ya isa tsakanina dake, nan na fara gaya mishi bakaken maganganun da suka kara tayar mishi da ciwo,, da naga ya kwanta yana kuka sai na fita na yaga takaddar da niyar bazan fada ma kowa ba kuma bazan yarda yasan ina gidan ba, sai na fara tunanin in kawar dashi kawai saboda nasan in iyalinshi suka san mun rabu bazan ci wani abu daga cikin dukiyarshi ba, ta fashe da kuka tace sai gashi yanzu na tashi a tutar babu, babu kudi babu kima, "sannan kuma babu rayuwa nurain ya fadi da karfi idonshi na zubar da kwalla, ya karaso kamar zaki ya dagota ya shaketa yace wallhy yau saina kasheku dukanku, babu wanda zan bari da rai in har na barku to tabbas ban cika dan mahaifina ba, da kyar aka banbare hannunshi a wuyan anty amarya ya durkushe yana kuka mai tsuma zuciya, farouk, laila da jalila suka karaso gurinshi suna bashi hakuri suna kukan suma, babu wanda a gurin bai zubda hawayen tausayinsu ba, sadeeq ya mike ya fita da sauri kamar mahaukaci, hilal ya bi bayanshi yana kiranshi amma ina sadeeq har ya shiga mota ya tada ta ya fita, da sauri hilal ya shiga tashi ya bi bayanshi wani irin mahaukacin gudu sadeeq yakeyi ya doshi wani daji yana keta bishiyu yana kuka sosai dan a ganinshi duk shi ne silar mutuwan mahaifinshi, duk irin gudun da hilal keyi baisa ya cimma sadeeq ba, haka mutanen dake hanya wasun su suka biyosu dan ganin abinda ke faruwa, saida ya isa daidai wani katon rami sannan yaja baya hilal ya sauko da sauri ba tare da ya kashe motarshi ba yana ihu yana kiran sunanshi amma inaa sadeeq ya riga yayi nisa baya jin kira, runtse ido hilal yayi hade ihuuu ya durkushe a gurin sakamakon fadawar sadeeq wannan katon ramin, da sauri mutane sukayi dafifi a gurin ana kallon ikon Allah dan yadda motar ta tarwatse sunsan dakyar rai zai fita a ciki sai dai wani ikon Allah,, hilal kasa motsi yayi Idonshi ya kafe hawaye suka ki fitowa a cikinsu saboda tsananin tashin hankali, sai mutanen dake gurin ne sukayi iya kokarinsu dakyar aka janyo sadeeq da yayi paca2 da da jini babu alamar numfashi a tare dashi,, a rude mutanen da suka rikeshi sukayi motar hilal dashi baya hilal ya shiga ya rungume sadeeq sai a lokacin hawaye suka fara zuba a idonshi yana kuka yana fadin why marafa, meyasa zaka kashe kanka da gangan, kuka yakeyi sosai da kyar suka rarrashe shi wani a gurin ya shiga motar ya tuka suka wuce Mends specialist hospital... A kotu kuwa bayan an tsagaita da koke koke alkali ya tattara shaidu sannan ya kalli barr tahir yace ko yanada jaa, barr tahir jiki a sanyaye yace a'a ya mai shari'a,, alkali yace to bisa kammaluwar gabatar da shaidu kotu ta gamsu da shaidun da aka kawo mata saboda la'akari da karfinsu sannan kuma masu laifi sun saukakewa kotu ta hanyar amsa laifinsu da sukayi, saboda haka kotu ta wanke zulfa'u Adam daga zargin da ake mata da kuma tarar miliyan goma sha biyar saboda kazafin da akayi mata da zaman matsi da takura da tayi a police station,, sannan kotu ta yanke wa maimzy shekara biyu bamba kuma shekara sha uku a gidan yari saboda harda shi aka je aka karbo maganin da aka zubawa marigayi ya mutu dan da ya fadi da wuri hakan bazai faru ba, sannan bisa adalcin kotu da kuma saukake ma kotu da sukayi ta hanyar fadin gaskiya kotu ta yanke ma hadiza matar marigayi da sanah matar danshi hukunci ta kisa hanyar rataya,, sai kuma beeba da ta taimaka gurin nemo guba, kotu ta yanke mata hukuncin daurin rai da rai, ihuu suka dingayi suna kuka suna fadin a yafe musu, babu wanda yaji tausayinsu sai yar uwarsu aneesah dake kuka ta kira maman sanah ta fadi mata kuka ta dingayi itma a wayar kamar tababbiya,, alkali yace alhamdulillah mun gode ma Allah da ya kawo mana karshen wannan shari'ar kuma ya bayyana gaskiyar dake cikinta cikin kankanin lokaci, yaku mutanen dake zaune a gurin nan, shin me wannan shari'ar ta koyar daku, babu wanda yayi magana shuru kotun tayi saboda suna son jin kalaman hikima daga bakin alkali, alkali yace tabbas Allah mai girma da daukaka ya koyar da darasi cikin zamanmu na farko,,, a shariar karshe kuma ayah ce ta sakko daga gurin Allah swt, shin akwai wanda yayi tunanin fitar zulfah daga cikin wannan rikitaccan dabaibayin da akayi mata, sai gashi cikin watanin da basu kai biyu ba Allah ya wanketa da shaidu masu karfin gaske saboda gaskiyarta da kuma tsaftataciyar zuciyarta, shaida ta farko yadda karya ta shigo cikin tafiyar sanah wanda ta fadi ma mutane uku kasar da take, ta fadi ma mijinta taje india jinya, sannan saboda toshewar basira ta fadi ma kanwar mahaifiyarta taje dubai sarin kaya, sannan tayi ma mahaifiyarta karyar suna england ita da mijinta, ikon Allah kenan zai ta ara maka lokaci amma in yaso a lokaci guda alakadarinka zai karye, shaida ta biyu mukhtar yayan ismail wanda ikon Allah ne ya hada ismail da saleem har Allah ya kawosu taimakonta;, cikin labarinsu mukhtar ya gane akwai makarkashiya har Allah yasa yaga jawabin beeba ya tabbatar da gaskiyar abunda yake tunani har ya fada musu sirrinshi, shin in ba Allah ba waye zaiyi wannan, gurin ya rude da cewar Babuuu,,, sannan shaida ta uku shine mati drivern taxi wanda mutuwar mahaifinshi yasa shi barin tukin taxi ya siya napep Allah cikin ikonsa yasa a ranar da motar laila zata lalace shi kuma a lokacin Allah ya turoshi domin ya daukesu har yaji jawabinsu shima Allah ya matsi bakinshi ya fadi saboda dai yana son wanke baiwar shi mai yawan bauta mishi in banda Allah wanene zai iya wannan hadin cikin lokacin da ake bukatar taimako, nan ma kowa yace babuuu, sai kuma shaidar beeba da Allah ya toshe basirarta ya rufe mata ido da son kudi wanda har soyayyar su ya sakata yin SUBUL DA BAKA ( littafin my one nd only zeedee) ba tare da tayi tunanin abinda fadin zai jawo mata ba, lallai wanda ya yarda da Allah to tabbas baxai taba tabewa ba kuma babu wanda ya isa yaga bayanshi cikin sauki, sannan shaidar da tafi bani mamaki bai wuce shaidun mutane biyu ba wanda a farko suke bayan karya a karshe kuma suka ji tsoron Allah suka fadi gaskiya cikin gaskiyar har aka gano rikitaccan alamari wanda akayi shi bisa dodewar basira, dan da bata sako su cikin shaidu ba bincike bazai taba hawa kanta ba saboda babu wanda ya ganta sai Allahn da ya dode mata kwakwalwa ya sanyata sakosu ciki saboda ya tona mata asiri, lallai Allah mabuwayi ne gagara misali, ya yan uwana muji tsoron Allah, mu tuna da ranar da uwa bazata iya ceton danta ba, ranar da aikinka na lada zai taimakeka, ranar da babu wata inuwa sai inuwar alarshi, shin muna yiwa kanmu hisabi a kullum idan mukaje yin bacci, shin akwai wanda yake tuna in ya kwanta ba lallai bane ya bude idonshi gobe ta riskeshi, shin muna tuna akwai babban tashin hankali a gaban mu bayan an gama hisabi wanda shine tsallake siradi, duk musulmi mai hankali tabbas baya cikin kwanciyar hankali saboda bai san ina ne makomar shi, ya kamata dukkanmu nan da ma wanda baya nan yasan ba aikinmu bane zai kaimu aljanna rahamar Allah ita kadai ce zata kaimu aljanna, dan haka ya yan uwa mu yawaita tasbihi, istigfari da hailala, da kuma salatin fiyayyen halitta annabi muhammad sallalahu alaihi wasallam, bakin ciki bazai taba riskar wanda yayi riko da alkur'ani ba saboda shi alkur'ani jagora ne kuma ginshikine a cikin rayuwar mu baki daya, ina rokon Allah da ya hane mu duk wani aiki na sabo a gareshi yasanya mana tsananin son yin aikin da zai kusanto mu gareshi, ya Allah ya hadamu cikin aljanna firdausi baki dayanmu, ameen thumma ameen, jinjina gareka barrister saleem da kuma ismail da laila da ta tsaya kai da fata gurin binciken gano gaskiyar wannan alamarin saboda kyakyawar zuciyarta, wadanda suka mutu Allah ya jikansu mu kuma Allah ya sa mucika da kalmar shahada,,, ameen mutanen gurin suka fadi sannan kotu ta tashi kowa ya mike masu murna suna murna rolex da jalila da zabba'u suka rungume zulfa'u dake kuka sosai can kuma su anty amarya ce ke kuka yan sanda sun sakasu a gaba sun tafi dasu, barr saleem suka fita waje shida su ismo mutane sai sam barka ake musu cikin farin ciki, baban zulfa kamar zai durkusawa laila da saleem saboda murna yanata godiya babu kakkautawa, gurin motocinsu suka wuce sunata hirarsu cikin jin dadi, nurain na bude motarshi yaji wayarshi na ringing, kafin ya daga ta katse ya duba yaga misd cals da yawa, yace hilal lafiya, yana waige2 dan yasan ya ganshi a cikin court, kiranshi yayi, hilal ya dauka cikin kuka ya fada mishi abinda ya faru, a gigice yace whattt, innalillahi wa inna ilaihir rajiun, laila da su farouk suka ce lafiya yaya, ya fada musu abinda ya faru cikin rudu yace laila ku wuce gida bari inje asibitin, tace a'a mudai je tare farouk dauke su ka kaisu gida amma fa kar ka fada ma mummy komai sai munje mun ga jikin nashi kaji, farouk jiki a sanyayye yace too, suka wuce gida, anty laila da su malam saleem da baban zulfah suka wuce asibitin... Mrs tijjani shattima.... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 6⃣9⃣ By Aysha Ya'u Kurah Hankali a tashe suka karasa asibitin har lokacin likitoci na kan sadeeq da ya ji ciwo sosai a jikinshi, Allah ya taimaka babu karaya da buguwa amma har lokacin bai farfado ba, saida suka kusa awa akanshi suna dressing ciwukan jikinshi, sannan suka fita bayan an daura mishi drip, doctor na fitowa suka karasa gurinshi a rude suna tambayarshi, doctor yace su kwantar da hankakinsu babu abinda zai sameshi yayi musu bayanin komai yazo da sauki at any mmnt xai iya farkawa, suka tambayeshi zasu iya shiga yace ehh amma banda hayaniya, shiga sukayi da sauri suka ga gurin da yaji ciwukan goshinshi sai hannunshi da kafadunshi, alhamdulillah suka dinga fadi saboda Allah ya kiyaye sannan suka zauna jiran ya farfado... Suna karasawa gida mummy na parlor tana kuka sosai kamar ranta zai fita saboda ganin da tayi ma shariar a ait, afrah da amrah na kewaye da ita suma kukan sukeyi ayda na share ma mummy hawaye tana bata hakuri, ganin shigowarsu yasata mikewa ta rungeme zulfah tana fadin ki yafe min zulfah, zulfah na kuka itama tana share ma mummy hawaye tace wallhy ban taba kullatarki ba mummy, babu abinda kikayi min dan Allah ki daina kuka, mummy ta janyota suka zauna tana kallon ta cikin kuka tace tashi kije kiyi wanka kici abinci kizo ku tafi asibiti da farouk a duba lafiyar jikinki, zulfah ta mike suka wuce ciki Ita da jalila da zabba'u, wanka sosai tayi ta wanke kanta da yayi mugun datti tayi alwala ta fito tayi sallah tana godewa ubangiji da ya wanketa daga wannan zargin da ake mata, Abinci aka loda a gabanta kamar jaka ta bude baki tana hararar jalila tace ko jaki kika zubawa abincin nan banjin zai iya cinyeshi, jalila tace bansan iskanci kinsan wahalar da nasha kafin in gama miki girkin nan, gobe ma ranace in na tafi zanga wanda zai cigaba da dafa miki irin me dadin nawa, ta ajiye spoon din zata wuce zulfah ta janyo hannunta tace dan Allah anty jalila ki yi hakuri, haba amaryar isiyaku, zabba'u ta kwashe da dariya tace ay fa sai isiyaku, jalila ta zauna tace duk zaku sani wallahy zan rama ne in na tafi gobe baku kara ganina sai haihuwarki, zulfah tayi murmushi tace wai ku wa ya fada muku ina da ciki, jalila ta shafo cikin tace mummy mana, dan Allah ki haifo min takwara, zabba'u ta harareta tace ko kuma sakwara ba, kinji ta hannun daman ni zaki haifo ma takwara ko, ita dai abincinta take ci bata ko kallesu ba dan ita gani takeyi duk wasa suke mata, saida suka gama cin abinci sannan suka wuce asibiti, dubata dr balogun yayi da kyau sannan ya bata magunguna ya dibi jininta akayi test, doctorn na dawowa daga lab yace mata am happy 4 u kina da cikin wata biyu da kwanaki, shuru zulfah tayi bayan ta karbi takaddar ta fito ta sami farouk suka wuce asibitin sadeeq a mota sai murna farouk yakeyi kamar matarshi aka ce tana cikin, ita kuwa har suka karasa sukuku take dan har ga Allah bata son abinda zai kara hadata da sadeeq da a yanzu ta gama tabbatar da jikinta yake so zuciyarshi sam babu ita cikinshi, ta riga ta kudira a ranta zata rabu dashi ko da kuwa rabuwar zai haifar da bacin rai, suna karasawa farouk yayi2 ta shiga taki tace ya shiga ya fito, haka ya kyaleta ya shiga ya barta tanata sake sake, Kwanan sadeeq tara a asibiti jikinshi yayi sauki sosai sai dai ciwonshi da bai warke ba saboda zufinsu, da kuma karfin jiki, fada sosai nurain yayi mishi kamar zai ari baki, haka mummy da taji tayi kuka sosai itama tai mishi fada a waya dan bata fita saboda takaba, kullum in za'aje duba sadeeq zulfah excuses take bayarwa ko tace bata da lafiya ko kuma tayi baccin karya ko in sunje tace su shiga zata shigo,,, farouk da laila ne kadai suka dagota suma kuma sun yarda ta garashi din tunda zuciyarshi sam bata fada mishi gaskiya, in ya hau dokinta baya sauka sai da dana sani ... Satinshi biyu aka sallameshi ciwukan sun warke kadan ya rage su gama heeln kuma ya samu karfin jiki sosai, damuwarshi a kullum itace yasa zulfah a idonshi, yayi mamakin da ko sau daya bata zo duba shi, kafin su tafi ran da aka sallemeshi farouk na rike da bargo suna fitowa yace farouk wai ina zulfah ne, farouk ya hade rai yace jiya ta dawo gida kasan tabi babanta sai jiya barr saleem ya dawo da ita gida, ya kauda kanshi yace yaya abba barr akwai kirki wallahi, jiranka ma mummy takeyi akan takaddar zulfah saboda in ta haihu mummy da mahaifinta sun yanke hukuncin bawa saleem aurenta ay ya cancanci hakan ko yaya tunda kai da kyar zuciyarka zata kara baka hadin kan kasota,,, sadeeq sai da ya kusa faduwa saboda karo da yayi da kujerar reception din, da sauri farouk ya rikeshi yace sannu yaya ka dinga kallon gabanka ko sai na rikeka ne, sadeeq dai bai ce mishi komai ba zuciyarshi na suya har suka shiga motar suka wuce bai ce mishi komai ba, farouk ya dinga gimtse dariyarshi saboda yadda yanayin sadeeq ya canza har suka kai gida sadeeq baisan sun kawo ba, saida farouk ya tabashi yace mun kawo yaya,sannan ya bude motar jikinshi a sanyaye ya fito a kofar parlon ya tadda mummy tsaye tana jiran karasowar shi, yana shigowa suka rungume juna idonta ya ciko da kwalla tace karka kara irin wannan gangancin abba na, shima idonshi yayi ja yace yi hakuri mummy in shaa Allahu bazan kara ba, tace yawwa abbana ka dinga addua akan wannan zuciyar taka dan Allah dan ko kadan zuciyarka tana da rauni kuma kana biye mata ka dinga yawaita maimaita ""Allahumma ya muqallibal qulubi sabbit qalbi ana deenika"" kaji,, ya gyada mata kanshi tace to maza muje kaci abinci sai kayi wanka ka huta kaji, jikinshi a sanyaye ya mike,, kenan mummy da gaske takeyi zata rabashi da zulfah tunda da ba haka ba ay da ce mishi zatayi yaje dakinshi matarshi ta bashi abinci, yana isa dining room ya zauna mummy ta zuba mishi abinci, yana ci tana mishi hirah, fitowa zulfah tayi cikin wata doguwar rigar light orange silk material kanta ba dankwali sam bata kula dashi ba tace mummy gashi malam saleem ne, mummy tayi murmushi tace har sun isa ne, zulfa tace ehh tana murmushi, juyowar da zatayi suka hada ido da sadeeq ta dauke kanta tayi wucewarta tana tafiyarta mai jan hankali, binta sadeeq yayi da ido zuciyarshi kamar zata faso kirjinshi saboda tsananin kishi, mummy ta kalleshi bayan ta gama waya tace saleem akwai mutunci wallhy yaron kirki, sai yau suka tafi Singapore, mikewa sadeeq yayi yace uhumm, mummy tace to abincin fa kar dai har ka koshi, maganarshi a makoshi yake yinta yace banda apatite mummy, ya wuce side dinshi ba tare da ya saurari me xata ce ba.... Mrs tijjani shattima..... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: [8:47PM, 08/02/2016] Aysha Ya'u Kurah: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 7⃣0⃣ By Aysha Ya'u Kurah Yana shiga daki ya zauna ya dafe kanshi yanajin zugi a can cikin zuciyarshi, ko wanka ya kasa tashi yayi saboda tsabar bakin cikin dake dankare cikin zuciyarshi, To shi saleem din mahaukaci ne da za'a bashi matar wani tun bai saketa ba kuma da cikinshi ya yarda, lallai suna so ayi yakin da bazai taba karewa ba duk ranar da suka bijiro mishi da wannan maganar, haka sadeeq ya dinga tunani ya mike ya zauna kamar zararre sai can yamma ya samu yayi wanka ya fito ya shiga parlon mummy dan ya fara jin yunwa, tun kafin ya karasa yaji suna hira su uku kuma duk akan kwarewar aikin saleem ne, hango tahowarshi farouk yayi ta makeken show glass din dake parlon, ya maza ya canza maganar yace wallhy anty nakosa auren nan yazo wayaga ango da amarya, ya kalli zulfah yace ji nakeyi kamar in janyo watannin haihuwarki ki haihu musha biki, zulfah da bata fahimci auren wa yake nufi ba tayi dariya tace ay na fi ka kosawa in haihu in huta da wannan cikin duk da ba wani wahala yake bani ba amma na dan samu sauyin wasu abubuwa, anty laila tayi murmushi tace ay dama ciki ko baka laulayi dole ka samu sauyi har sai ka haihu zaka huta, Allah dai ya raba lafiya ameen sukace dukkansu dai2 lokacin sadeeq da ya dade tsaye yana jinsu ya karaso ciki a tunaninshi ba wanda ya ganshi bai san farouk tuni ya ganshi ba, farouk ya dauki wayar zulfah yayi flashing saleem yana kallon sadeeq yace sannu yaya abba, ko kallon inda yake sadeeq baiyi ba, anty laila tayi murmushi tace irin wannan cika da batsewar fa abba, ya kara hada rai ya zauna a dining yace lfy ba tare da ya kalleta ba, wayar zulfah ce ta fara ringing da sauri farouk yace saleem ne ya kiraki tashi maza kije daki ki amsa kar waleed ya hanaki ji kawoshi, zulfah ta mika mishi waleed ta karbi wayar tasa a kunnenta tana tafiya a hankali murya can kasa tace assalamu alaikum, sadeeq ya runtse idonshi da yayi jawur wani abu yakeji yana nukurkusarshi a ko ina na cikin jikinshi, kauda abincin da ya zuba yayi ya tashi ya fita daga parlon gaba daya numfashin shi yana sama yana kasa, garden ya nufa ya zauna cikin kunan rai dakyar da addua ya samu zuciyarshi ta dan lafa, yanata mamaki da takaicin yadda zulfa'u ta shareshi, ay ko sannu da jiki tayi mishi ko dan ďan da suke shirin raba uwarshi da ubanshi tun kafin yazo duniya,, bai bar gurin ba har saida gari ya fara duhu sannan ya fita ya tafi masallaci.. Wata hudu bayan wucewar wannan, alamura da dama sun faru ciki harda fitar takabar mummy, sadeeq kuwa tun washe garin faruwar wannan yayi kaura da gidan gaba daya dadin da yaji ma aikinshi sai weekend yake samun hutu, wani lokacin ya dawo gida wani lokacin yayi zamanshi duk ko da irin azabtar dashi da zuciyarshi takeyi akan zuwa ganin abinda takeso haka ya danne yafi karfinta saboda tsananin kishin zulfah na neman buga mishi zuciya, Zaune suke da mummy a parlor suna hira mummy na duba kayan jariran da suka siyo ita da anty laila, mummy ta kalleta a hankali tace zulfa'u kuna waya da abba kuwa, zulfah ta gyada mata kai tace eh mummy, mummy ta dago wata sweater tace da wace wayar kukeyi dan dai naga rabon da ki kunna waya an dade, tace umm dama da ta yaya farouk ne kafin ya tafi training kuma tunda ya tafi bamu kara waya ba, mummy ta fito da ido waje tace watan farouk biyu kenan da tafiya kina nufin tun lokacin bakuyi waya ba, zulfah ta sunkuyar da kanta kasa, mummy ta rage murya cikin rarrashi tace kiyi hakuri zulfa'u nasan kina fushi da abba, kiyi hakuri ki yafe mishi, abba mutum ne mai raunin zuciya duk sauran sun fishi karfin zuciyar jurar abu, dan Allah karki ga laifinshi akan abunda ya aikata nasan kinason shi kuma duk tunaninki bai wuce shi baya sonki ba ko, to wallhy kinji na rantse zan iya ce miki babu macen da abba yakeso a yanzu da ta wuce ke, dai2 lokacin anty laila ta karaso tace hakane mummy, saboda tsananin kishinki yanzu sam abba baya min waya ko yazo gidannan wkend baya nemana ko shiga inda nake haka ko kiran farouk baya yi ko farouk ya kirashi baya dagawa dan yana ganin kamar so mukeyi mu raba aurenku mu bawa saleem, mummy tayi murmushi tace ay shima umara ya cika tsokana ina jinshi rannan yana hango abba ya fara wayar karya da sadeeq ashe abun da yake nufi kenan ja'irin, anty laila tayi dariya tace kema mummy dan Allah karki bata mana plan mu hadu mu ganar dashi ta inda zai gane kurensa ya daina biye ma zuciya, mummy tayi murmushi tace to amma fa na kankanin lokaci dan bazan biye muku zuciyar abbana ta buga ba,, anty laila tayi dariya tace mun yarda mummy, nan suka cigaba da hirarsu hankali kwance zulfa ta kwashe kayan ta kaisu dakin mummy gurin da sauran kayan suke... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: ..... [1:09AM, 09/02/2016] Aysha Ya'u Kurah: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 7⃣1⃣ By Aysha Ya'u kurah Zulfa'u na zaune a dakinta tana shan wani maganin sassaken mangaro da mummy ke amso mata tun cikinta na wata 7, tana sha tana yatsina fuska saboda yadda take jin mutsu2 a cikinta, kwanciya tayi bayan ta gama sha tana tunano rayuwar da tayi tun zamanta da Marka har zamansu da su sanah da irin sharrin da akayi mata, ta shafa cikinta a zuciyarta tana gode ma Allah dan badan ya taimaketa ya wanketa daga wannan zargin ba da tuni an shafe babinta a doran kasa, wayarta ta dauka ta kira mahaifinta da nasarori ke binsu shi da kabiru dan yanzu har karamin gida ya siya a Na'ibawa inda yasa kabiru yayi aure ya bashi daki, ko bi takan marka bayayi dan baya kaunar ko sunanta yaji, tana fara ringing ya dauka suka gaisa ya tambayeta tana nan lafiya ko, ta amsa mishi cikin jin dadin jinshi cikin farin ciki, yace ya su hajiya ki kara yi musu godiya fa, mijinki ma kiyi mishi godiya satin da ya wuce yazo ya bani mota wallhy, dan Allah ki kara mishi godiya itama hajiya duk da na kirata na mata ki kara yi mata dan godiya bata kadan Allah ya sa aljanna ce makomarsu ya dawwamar daku cikin farin ciki, zulfah murya a dashe tace ameen baba ka gaida yaya kabiru da anty Badiyya, yace zasu ji in shaa Allah ya kashe wayar itama ta kashe tana mamakin yadda akayi sadeeq yasan inda mahaifinta yake, Allah ya saka mishi da akhairi abinda taji zuciyarta ta fadi kenan, kafin ta ajiye wayar taji tayi kara ta duba taga zabba'u da sauri ta dauka tace my z square, zabba'u tayi murmushi tace maman biyu ya kike, tace lafiya lau, zabba'u tace ya babynmu har yanzu shiru fa muke ji na kosa muzo mu sha suna, zulfah ta yatsina fuska cikin tsokan tace bashi da zuciya babyn nan naku har yanzu yaki fitowa may be babanshi yake son gani, zabba'u tayi dariya sosai tace wato shi babyn baya fushi da babanshi kenan, zulfah tayi tsaki tace yaki tayani in gaya miki ay yana fitowa sai na mishi dundu guda biyu nima in rama, zabba'u tace me zai hana ki tsoma shi cikin ruwan sanyi daga kin haifeshi, zulfah tace gud advise hakan za'ayi amaryar ismo, ke ni ban ma fa tambayeki ba, wato dan munafurci badan malam saleem ya fada min ba ke bazaki fada ba ko, wato ku lokacin ina cikin wani hali ku soyayyarku kuka kulla da ido ko, to bani labari tun daga day 1 or else,, zabba'u da takasa daina dariya tace else watt,, zulfah tace kema kin san sauran, zabba'u tace to ayi mana afuwa zanzo gobe sai kiji komai kinji, alamar tsayuwar mutum taji a gabanta takasa bawa zabba'u amsa ta maza ta dago kanta sukayi ido hudu yana tsaye ya harde hannu cikin kananan kaya, kauda kanta tayi da sauri tace sai kinzo dear ta kashe wayarta tana kokarin gyara maternity wear din dake jikinta saboda rigar is sleeveless, hularta ta dauka ta tura gashinta ciki ta fara kokarin mikewa dakyar ta mike tabi ta gefenshi zata wuce ya riko hannunta da sauri, ka sakeni ta fadi ba tare da ta juyo ta kalleshi ba, gabanta ya dawa ya dago fuskarta yana kallonta ba tare da yayi mata magana ba, kauda kanta tayi da sauri saboda wani irin rikitaccen kallon da yake mata ta fara kokarin kwace hannunta ya matseshi da karfi ya janyota jikinshi, cikin masifa tace dan Allah ka sakeni ji yadda ka wani jawoni kamar idonka baya ganin ina tare da lalura, a hankali ya fara shafa katon cikinta ya kwantar da kanshi kan kafadunta murya can ciki yace nayi tolerating punishment dinki na gaji haka, duk dan adam ajiizi ne babu wanda baya kuskure dan Allah ki daina bani wahala haka, idonta a runtse saboda duk ya sakar mata kasala tace nidai dan Allah ka barni bana son jin kalamanka, ya juyota ya rungumeta sosai yace babyna nason jin kalamaina kuma yanzun nan zamu gana cos I msd him or her alot, ta turo baki ta fara kukan shagwaba tace ni ka kyaleni wayyo cikina, yace ay ko mararki ce yau saina nayi magana da baby na saboda shi ay baya fushi dani, da sauri tace wallhy yama fi yin fushi dakai dan he htes you, yayi dariya ya dago kanta yace hakuri zan bashi karki kara cemin komai, ta bige hannunshi tace wallhy sai nayi ma---- tura bakinshi cikin nata yayi ya hanata karasa maganar da takeyi, cikin rudewa sadeeq ke sarrafata ko kadan baiyi duba da tsohon cikin da take dashi ba, bazai iya jurewa ba ko kadan saboda yayi missing dinta matuka gashi dai sau daya ya taba kusantarta amma wannan tarayyar ganinta yakeyi tafi dare dubu saboda taki gogewa a cikin zuciyarshi, rawa kafarshi takeyi saboda tsabar rudu har suka kusa kaiwa kasa, daukarta yayi tana ihu tana kuka tana mishi nuni da cikinta amma sam sadeeq bai saurareta ba dan bai ma san tanayi ba, kasancewar gidan babu kowa yasa babu wanda ya jiyo muryar sadeeq, addu'a ya dinga rada ma zulfa da karfi yana kuka yana rokonta Allah da Annabi akan kar ta rabu dashi, itama kukan takeyi saboda azabar ciwon marar da takejinta kamar zata fita, tabbas sadeeq yayi musabaha da danshi a wannan rana musabahar da ta kara dasa mishi soyayyar zulfah da abun dake cikinta mai yawan gaske, razanannen ihun da zulfah tayi ne ya dawo da sadeeq cikin hayyacinshi, da sauri ya dagota ganin zufa na keto mata ta ko ina yace lafiya menene, da karfi tace dole ka tambayeni mana wayyo bayana, ta rike bayanta tana kuka sosai, tsarki kadai yashiga yayi a bayi da sauri ya maida kayan jikinshi ya daura mata zani da hijab ya dauketa chakk yayi waje da ita yana shirin sata a mota motar nurain ta shigo shi da laila da sauri suka fito suna tambayarshi, cikin rudewa yace bayanta ne ko mara anty shiga muje plss, ta mika ma nurain waleed suka shiga motar nurain ma yashiga gaba suka wuce asibiti cikn tashin hankali dan kuka takeyi sosai saboda azaba, diamond hospital suka je nan da nan akayi labour room da ita, sadeeq sai kai kawo yakeyi yana adduar Allah yasa ba wani illa yayi mata ba, duk ya surkuce saboda tashin hankali, ta kusa awa a cikin dakin sannan wata nurse ta fito musu da katon yaro kyakkyawa kamar ubanshi a gyare cikin sweater, nurain ya karbeshi da sauri bayan ya ajiye waleed, sadeeq yace nurse ya jikinta, nurse tace da sauki ana mata dressing ne, sadeeq yace alhamdullilah, anty laila ta kira mummy dake gidan suna ta fadi mata cikin farin ciki ta mike da sauri ta tattara su afrah tayi sallama da mai jegon ta wuce ta shiga mota farouk yaja su suka wuce shima cikin farin ciki, Dakin da aka bata cike yake da familyn marigayi daddy in ka dauke jalila dake gidan aurenta, kowa cikin murna yake daukar yaron harda su afrah, farouk ya kalli sadeeq da bakinshi yaki rufuwa yace congrat yaya abba wannan babyn ni za"a bawa in nayi aure in rike ko mummy, anty laila tace ay dama namu ne dan autan mummy, yayi murmushi yace bari in fara ma saleem albishir dan nasan baku fada mishi ba ya fito da wayarshi ya fara neman layin saleem,, a zuciye sadeeq yayi kanshi ya kwace wayar yayi wurgi da ita ta tarwatse ya kai mishi mari da sauri ya goce yana ihu yana dariya, nurain da mummy suka mike da sauri suka rike sadeeq da yake shirin bin farouk waje yana masifa, mummy tace haba abba to yanzu me ya maka da ka fasa mishi waya harda kai mari, sadeeq ya kara hade rai yace mummy ni sa'anshi ne da zai fada ma wani haihuwar dana, ya bari shi in ya haifi nashi ya kirashi yayi mishi albishir din, wallhy mummy kija mishi kunne in ba haka saina ji mishi ciwo, anty laila ta kasa boye dariyarta sai da tayi mai isarta sannan tace to meye dan an fada ma saleem ay naga mun zama daya dashi ko, da ku dai sadeeq ya fadi kamar me shirin yin kuka yace wallhy mummy ki fada musu su fita harkata dan yaga anty na goyon bayanshi shiyasa ya raina ni, mummy tace hakilo, to yanzu wai kai duk dan za'a kira saleem ne yasa kake wannan masifar, ay ko saleem dole yaji tunda yanada muhimmaci a rayuwar zulfah, sadeeq yace rayuwarta kikace mummy nidai kar wanda ya fada mishi haihuwar dana, nurain yace to fah to yi hakuri abban daddy babu wanda zai kirashi zan musu fada kaji, farouk dake tsaye daga waje yace wallhy yaya kace ya biyani abubuwan cikin wayata in ba haka ba, in ba haka me zai faru sadeeq ya fadi yana karasowa kofar, farouk ya ruga da gudu yana dariya, mummy ta zauna tana dariya tace Allah ya shirya,, sai washe gari aka sallameta suka dawo gida, baki ko ta ina zuwa sukeyi mata barka harda su goggo amina anan take bata labarin marka na kwance hawan jini ya kwantar da ita sosai saboda damuwar salaha da ta maida ma bangis yara ta shiga karuwanci, zulfah taji tausayinta sosai tace Allah ya bata lafiya in shaa Allahu zanje duba ta bayan arba'in, jalila ma tun ana jibi suna taxo itama da tsohon cikinta, ranar suna yaro yaci sunan daddy HASHEEM ABUBAKAR MARAFA, (Daddy) mutane sun zo sunan sosai ciki harda su feenah dake soyayya da malam saleem sosai dan har an fara maganar aure, sadeeq kuwa ba karamin barin kudi yayi ba a sunan dan walima biyu yayi saboda tsabar farin ciki, haka akaci suna aka watse cikin farin ciki... Mrs tijjani shattima...... [15/12 14:48] Anty aisha ya'u kura: [10:37AM, 10/02/2016] Aysha Ya'u Kurah: ◆◆ ZULFAH ◆◆7⃣2⃣ By Aysha Ya'u Kurah Satin zulfah uku da haihuwa sunyi kyau sosai ita da babynta saboda kulawar da suke samu gurin mummy da anty laila, sadeeq ma na iya bakin kokarinshi akansu in yana gari duk da har yanzu bata gama sakewa da shi ba, shi kuwa ko ajikinshi dan koda yaushe in yana gari yana tare dasu yayita mata hirah wani ta basar wani kuma ta amsa mishi.. Kwance take a daki idonta a lumshe dan bacci takeji sosai saboda daddy baya barinta ta rintsa da daddare sai dai da rana, muryar afrah taji tana bubbuga pillown da take kai tace anty wai kizo inji mummy tana parlon baki kuma wai ki bani daddy in daukeshi, zulfa ta mike zaune tace afrah bazaki iya ba, afrah tasa hannu kan daddy tace Allah anty zan iya, ta daukeshi ta fita dashi kanshi na rawa dan bata iya rikon sosai ba, zulfah ta sauko da sauri ta dauki hijab tasa ta bi bayan afrah, sakkowa afrah keyi daga kan stps da kyar ga skirt dinta na hardeta, rikeshi tayi da hannu daya tana kokarin gyara skirt dinta, kukan da daddy ya tsanyara yayi dai2 da shigowar sadeeq da sauri ya ajiye jakarshi yayi gurinsu da gudu dan saura kadan ta sakeshi, cikin masifa yace uban waye ya baki yaronnan, tace mummy tace in dauko shi a kaiwa baki, sadeeq yace duk gidan nan babu wanda zai dauko shi sai ke wallhy idan na kara ganinki da yaron nan saina babbala ki, zulfa ta karaso da sauri tace afrah meya faru, ta mika hannu zata dauki daddy sadeeq ya kauda hannun ya harareta yayi tsaki ya wuce side dinshi yana jijjiga daddy, afrah tace anty fa mummy ce tace a dauko mata shi baki zasu ganshi kuma kinga ya tafi dashi, ta kama hannunta tace muje rabu dashi kinji, suka wuce parlon, da sallama suka shiga parlon ta karasa da murmushi ta tsuguna ta gaida malam saleem dasu ismo da mukhtar, suka amsa mata cikin fara'a sukayi mata barka, mummy tace ina daddyn yake, afrah tace yaya abba ne ya kwace shi a hannuna, mummy ta kalli zulfah tace je ki karboshi su ganshi ko,, ta mike ta fita tayi side dinsu da rabonta da shiga ta dade, can ciki ta shiga dan baya parlon, kwance ta sameshi ya daura daddy kan kirjinshi yana shafa bayanshi, ta karasa tace wai mummy tace ka bani shi a kai mata, idonshi a runtse bai bude ba yace sai ki daukeshi in kinada karfi, tace wallhy zance mata kaki bani shi fa, yace wa ya rikeki anan yi sauri kije ki fada mata mana, tasa hannu a kan daddy tace dan Allah ka bani shi baki ne fa zasu ganshi, sai a lokacin ya bude ido yace ay ba dole bane bakin su ganshi, fita anan kafin ranmu ya baci dukkanmu,, in kina son kaiwa bakin shi kuma kin damu dashi ay bazaki ba afrah ta kaishi ba, amma saboda kina saurin kije ki ga saleem shiyasa kika bata shi dan ki tsaya ki shirya da kyau, zulfah ta zaro ido zatayi magana mummy ta turo kofar tace wani irin wulakanci ne wannan zaku bar baki zaune sun zo tun daga wani gari ganin da, sadeeq yace mummy afrah fa ta ba shi saura kadan su fadi kuma ni gaskiya sai dai suyi hakuri dan har yanzu kin ga bai daina kuka ba, mummy ta rike baki cikin mamaki tace zanci mutuncinka wallhy in baka miko min yaron nan ba, sadeeq ya kara hade rai ya mika mata shi tayi tsaki ta fita da shi,, zulfah ta mishi gwaloo ta fita ta sauri tana dariya, ya koma gefen gado ya dafe kanshi zuciyarshi na zafi dan a tunaninshi saleem yazo da magana akan zulfah ne, saida ya dan jima a zaune sannan ya mike ya fita da sauri harda tuntube ya nufi parlon dan jin abinda suke tattaunawa, tun kafin ya karasa yaji mummy nata Allah ya sanya alkhairi Allah sa ayi damu mun gode sosai, zulfah ma na gefe tana murmushi tana godiya, karasowa yayi lokacin da yaji sun rufe kofar alamar sun fita, kusa da mummy yaje ya zauna kamar zaiyi kuka yace mummy sun gama ganinshi, ta harareshi tace bansani ba, wallhy abba ka fita idona in rufe, yace wai mummy ina kika taba ganin an daki mutum kuna an hanashi kuka, ni kawai ki bani ďana tunda bani kadai kukeson sawa cikin kunci ba harda shi saboda haka ki bani shi mu bar gidan gaba daya,,, zulfah ta gimtse dariyarta tayi ciki ya bita da muguwar harara, mummy tace kuncin me kuma zamu saku, ya kara narke fuska yace ba gashi kuna maganar aure da saleem ba, haba mummy kin fa san hukunci neman aure akan aure, wallhy badan akwai abinda nake hange ba wallhy da saina kulleshi tunda shi bashi da hankali, mummy tayi murmushi tace saidai kayi hakuri abba amma mun riga mun gama magana gara ta auri wanda ke sonta da zuciya daya babu kokwanto a zuciyarshi, yace to ni da zuciya uku nake sonta, ta mike tsaye tace waya sani ta wurga mishi katinan biki da yawa tace kayi gaggawar bata takarddarta dan ga kati nan har sun buga, tayi ciki ta barshi baki sake ya kasa bata amsa, saida ya dade da katin a jikinshi sannan ya mike idonshi jajur ya zubar da katin har yayi gaba kuma sai ya dawo ya dauki daya ya bude, murmushin da baisan daga inda ya fito ba ya bayyana a kan fuskarshi, ya kwashe sauran katin yayi sama dasu da sauri, dakin mummy ya shiga yana dariya yace wallhy mummy yanzu kin daina sona so kikeyi zuciyata ta buga, tayi dariya itama tace ay gara ta buga a kara dasa maka wacce tasan abin da ya dace, ya zauna gefenta ya daura kanshi kan cinyarta yace mummy I promise u bazan kara wani abun da zakuyi fushi ba in shaa Allah, tayi murmushi ta dafa kanshi tace Allah yasa abba nah, yace ameen... Bikin su saleem ya rage kwana uku lokacin tayi arbain har jalila ma ta haihu ta sami baby gal, shirin bikin sukeyi sosai saboda sai an daura na zabba'u in sun kaita abuja su tsaya na saleem, ana gobe daurin auren ne ta shirya zuwa gaida goggo marka, tun safe ta gama shiri saboda daga can zata wuce gurin bikin, wani rantsatstan lace ta sa ash nd red tayi kyau sosai haka daddy shima ta shiryashi yayi kyau sosai, tana tsaye gaban mudubi tana daura dankwali taji an rungumeta ta baya, ta kalleshi ta cikin mudubin tayi murmushi tace kayi kyau sosai, ya juyota yana kallon cikin idonta yace har na kaiki, ta shige jikinshi ta lumshe idonta tana shakar kamshin jikinshi tace kaima kasan kafini, ya matseta sosai ajikinshi yace kedai kike ganin hakan amma ni duk duniya ban ga wacce ta kaiki kyau ba, tace ummm dadin baki kawai zaka ma KWAILAH, yayi murmushi ya dan buge bakinta yace wannan maganar bance kar a kara min ita ba, ta turo baki tace sai an fada din ay ba karya nayi ba, ya dauki daddy yace to naji gama shiryawa ki same mu a dakin mummy, ta dauki red gyalenta tana fesa turare tace to mijin kwaila, ya fita yana girgiza kai yana dariya... Zaune suke kan tabarma, goggo marka na kwance ta zama kamar mujiya ta rame sosai saboda azabar ciwo, kuka takeyi sosai tana rokon zulfah gafara, zulfah ta share hawayen idonta tace na yafe miki goggo Allah ya baki lafiya, tace ameen kabiru ma jiya yazo ya gaisheni dan Allah ku hadu ku rokor min gafara gurin malam nasan na musguna mishi sosai dan Allah ku bashi hakuri, zulfah tace shima ya yafe miki goggo Allah ya yafewa duk musulmin duniya, in shaa Allahu zaki samu sauki, goggo marka ta kara rushewa da kuka tace ay ni yanzu gara in mutu zulfah, kinji labarin salaha da sukayi fada da wata akan saurayi tsautsayi ya ratsa ta buga mata kwalba yarinyar ta mutu yanzu haka tana an yanke mata hukuncin kisa ta karasa fadi tana kuka sosai, zulfa tace kiyi hakuri goggo dan Allah ki daina kuka Allah yasa hukuncin da aka yanke mata ya zame mata rahama, sadeeq yace ameen nan suka dan dade sannan da zasu tafi sadeeq ya bata kudi masu yawa da alkawarin zasu dawo su kaita asibiti... Gidan goggo amina suka shiga itama suka gaisheta sukayi mata alheri sosai, delu ma ta roki gafararta dan hanne na can gidan bangis in ka ganta bazaka taba ganeta ba. A mota suna tafiya yana ta janta da hira saboda yaga duk zuciyarta a jagule take, tunanin su goggo kawai takeyi, lallai duniya ba matabbata bace ji yadda Allah ya maida marka da su delu da ada suke ganin kamar sun fi kowa ita kuma da suka kaskantar da ita sai Allah ya daukaka ta, ikon Allah kenan, sadeeq ya dafa ta yace wannan tunanin ya isa haka shi dama Allah babu yadda bai iya ba, mudai cigaba da addua Allah ya tsarkake mana zuciyarmu, tace haka ne ameen, yasha kwanar wata unguwa mai kyau anan cikin Gra, ta kalleshi cikin rashin fahimta tace ba gidan su zabba'u ake bikin ba, yayi shuru har saida suka kai wani dankareran gida ya tsaya a waje ya kalleta yace ziyara muka kawo, tace gurin wa, yayi murmushi ya latsa hon yace "Anty Aisha Dangusau" ce ta kirani tace ya kamata muje mu sada zumunci, cikin kosawa tace to wai gurin wa, yace Gurin ""Captain Mus'ab Abdulhameed da Anty Nuwairah Ahmed Shattima"", zulfah ta fadada fara'arta tace badai na cikin littafin SIRRIN BOYE ba, sadeeq yace uhumm yess su, mai gadi ya wangame gate din zulfah cike da murna tace dama anan suke, wayyo Allah na kana nufin zan gansu kenan, yace a'a bazaki gansu ba hotonsu zaki gani cike da gidan, ta turo baki zatayi magana suka hango Aman da Amal sun fito da gudu sun nufo motarsu, zulfah ta kasa rufe baki saboda murna ta bude kofar tana kallon twins din da basu wuce shekara 11 ba, suka rungumeta amal ta karbi daddy zulfah cikin jindadi tabi bayansu tana murnan ganin fuskokin mutanen da ta dade da karanta labarinsu, sadeeq ya fito yace au wucewa zakiyi ki barni to jeki, ta dawo da sauri tace am sorry plss in na shiga ince musu ni wacece, ya rike hannunta yace kice sunanki "Zulfa'u Adam" wacce "anty Aisha kurah" bata gama basu labarinki ba har yanzu, tayi dariya tace nasan zata gama gajen hakurinka ne yasa baka jira ta gama ba ka dauko ni ka kawoni, yajata suka bi bayan su aman dake fada akan daukar daddy, da sallama suka shiga katafaren parlon gidan, Nuwairah na zaune da tsohon cikinta tana kallo, can gefe kuma mus'ab ne ke raba Hanan da junior fada akan kayan wasa, da sauri Nuwairah ta mike tana musu sannu da zuwa, ta rungume zulfah ta jata suka zauna mus'ab ya karaso gurinsu shima yana murmushi suka gaisa da sadeeq sannan suka zauna, hira sukeyi sosai Nuwairah taja zulfah ciki suka cigaba da hirarsu tana ta bata shawarwari akan zamantakewar aure sannan ta hada ta da magunguna masu kyan gaske, da gudu hanan ta shigo tana ihu kamar wacce aka yankata, Nuwairah ta dafe kanta tace yau na shiga uku, me kuma aka miki, tace ba anty amal bace taki bani baby in daukeshi, zulfah tayi murmushi ta janyota tace yi hakuri zan bar miki shi ma duka kina so ko, hanan ta daga kanta tana murmushin jindadi ta fita ta da gudu tana kiran sunan junior ita adole zata fada mishi, Nuwairah tayi tsaki suka cigaba da hirarsu, saida suka ci abinci sannan suka fara shirin tafiya gurin karfe uku, kayayyaki ne cike da leda mai aikin Nuwairah ta kai musu mota suka rakosu suna tafe suna hira, mus'ab yace ma Nuwairah kinji bikin barr saleem gobe ne ko, tace ehh yanzu nakeji in shaa Allahu jibi zamuje abujan muma daga nan sai mu hadu mu kai ziyara gidan su "Marwah da doctor Abdallah," zulfah tace gaskiya da naji dadi sosai in muka hadu dukanmu, daga nan sai muje gidansu "barr Abdulmaleek sawaba" saboda in ga kaka, Nuwairah tayi dariya tace kaka problem Allah ya kaimu yar kanwarmu, kuma ya kara hada kawunan mu, Ameen suka ce dukkansu sannan suka shiga mota yaran na daga musu hannu suka wuce cike da murnar karrama su da familyn capt Mus'ab sukayi..... Mrs tijjani shattima... [12:33PM, 10/02/2016] Aysha Ya'u Kurah: ◆◆ ZULFAH ◆◆ 7⃣3⃣ By Aysha Ya'u Kurah Washe garin daurin aure aka dauki amarya zabba'u aka kaita abuja, bikine aka yishi na nutsatsun masu ilimi ya kayatar matuka aka dau amare aka kaisu gidajensu, Karfe hudu bayan an gama budan kai zulfa da sadeeq suka fito suka wuce gidan Anty zarah inda Nuwairah tayi musu kwatance can suka hadu saida suka dan dade acan sannan suka shirya tafiya gidan su MARWAH dake maitama, Tun kafin su karaso Marwah ke kiran Nuwairah a waya saboda ta kosa suzo, suna karasowa mai gadi ya wangale musu gate din gidan saboda yasan da zuwansu, a waje suka tarar dasu, suna ganinsu suka karaso gurinsu cike da farin cikin re unioun din da sukayi yau, Abdallah ya mika musu hannu suka gaisa sannan suka shiga ciki, Marwah ma rugumesu tayi cikin farin ciki ta karbi daddy tace anty Nuwairah ina yaran ko hanan baki taho min da ita ba, Nuwairah tace wannan fitinaniyar ay da bazata barni in huta ba suna can gurin ummi, karasawa ciki sukayi cikin farin ciki suka zauna nan da nan aka cike gabansu da kayan dadi, sunaci suna hirah zulfah tace wai ni anty Marwah ina yaran ne, banga ko daya ba, Marwah tace suna can gurin kaka yau hutu nakeyi, zulfah tace ay ko yanzu muna gamawa zamuje in gansu dan inason ganin meenal da fatan ta daina wasan ruwa, abdallah yayi dariya yace ay yanzu ta girma dama gado ne kuma dole yaro sai yayi daga baya kuma ya sakeshi, Marwah ta harareshi tace me kake nufi, ya kalli mus'ab da sadeeq yace kunji na kira sunanta, duk suka kwashe da dariya, Marwah tace wallhy zan rama, nan suka cigaba da hirah har kusan 6 sannan suka shirya suka wuce Gimbiya street, abdallah ya kira abdulmaleek ko yana gida yace eh yanzu ma ya shigo, yace to gamu nan zuwa, cikin farin ciki yace to sai kun karaso, suna karasawa kowa ya fito a motarshi suka wuce ciki, suna shiga ciki suka tarar gidan a jike ko ina meenal da beebi yar lubna sunata tsalle cikin ruwa, abdallah ya dafe kanshi yace oh ni wannan gadon ashe bai saki diyata ba har yanzu, marwah tayi tsaki ko kallonshi batayi ba taja hannun Nuwairah da zulfah dake dariya suka shiga ciki suka barsu a waje, tun kafin su shiga ciki suke jiyo hayaniya suna murda kofar lubna ta hankada su zata fita kaka na tsaye rike da ludayin miya a hannunta tana masifa tace dan ubanki kizo ki tafi gidanki; haka kawai ke duk kika zo gidan nan sai kin sani magana, marwah ta janyota tana dariya tace wallhy buga mata kaka har yanzu taki ta girma, kaka ta ajiye ludayin tace yaushe zata girma ta hadu da sahoramin mijin da baya kwaba mata, lubna tace wallyy mijina ba sahorami bane haushin rashi ne dan ba ke kika sameshi ba, abdulmaleek da suka fito tare da haffy yace ohh ya Allah, wai ku bakinku baya gajiya ne, haffy tayi murmushi ta rungume su zulfah dake tsaye suna dariya tace sannunku da zuwa, kaka tace baki lale2 wannan jarababbiyar ta hana mu gaisa, lubna tace oho dai naci dubu sai ceto, abdulmaleek ya karasa waje inda abdallah suke tsaye yana ma su meenal fada, ya mika ma su mus'ab da sadeeq hannu ya kalli abdallah yace in dai wadannan yaran ne wallhy bakinka sai ya gaji, abdallah ya mika mishi hannu yace kuma sai sunxo gidan kaka sukeyi saboda sangarta, suka karasa ciki suka zauna aka gaggaisa cikin farin ciki sunata hirah dasu kaka da baki ya kasa rufuwa sai labarin dariya take basu, basheer ne ya shigo da sallama shima ya zauna anata hirar dashi kaka nata mishi masifa akan ya dauki jarababbiyar matarshi da mabarnaciyar yarshi su tafi, basheer dai dariya kawai yakeyi saboda ya riga ya saba da jarabar kaka, sai kusan tara suka fara shirin tafiya dan anan sukayi sallar magrib da isha, har waje suka rakosu suna sallama tare da adduar Allah ya barsu tare.... Four years ltr Zulfah ce driving ta dawo daga skool kanta ciwo sosai yakeyi saboda karatun exams kuma bata samun yin baccin dare, tunaninta daya yanzu tana shiga gida su daddy da kanwarshi Nour zasu dameta dan ko ta korasu cikin gida gurin su mummy dawo mata sukeyi dukkansu har su waleed kuma so takeyi tayi bacci kafin ta tashi tayi girkin dare, farouk ne ya fado mata a rai wanda ake shirin bikinshi nan da wata daya, kiranshi tayi ya dauka yace madam ya akayine, tayi tsaki tace kaidai bari tace yanzu zan dawo skull umara ka taimakeni ka kwashi yarannan dukansu ku fita yawo wallhy bana jin dadi kuma bazasu barni in huta ba, yayj dariya yace gaskiya kin takurani da yawa amma zanyi anytn 4u tayi dariya tace godiya dubu ango, yayi murmushi ya ajiye wayar ya kwashesu suka fita suna murna sosai, Sai gab da la'asar ta farka ta shiga bayi tayi alwala tayi sallah taji kanta ya rage ciwo, kitchen ta shiga ta fara sarrafa abinci kala kala, sai gurin magriba ta gama ta shiryasu ta kimtsa ko ina taje tayi wanka, tana tsaye tana goge kanta da karamin towel sadeeq ya shigo da ruwan sanyi a hannunshi, rungumeta yayi sosai sannan ya juyota yace babyna ya skool, tayi tsaki ta karkatar da kanta gefe tace boko ba dadi, ya ajiye ruwan a kan mudubi yace ay dama daurewa akeyi hope exams din da sauki ko, ta gyada mishi kai, yace gud Allah bada saa, tace ameen, wayarshi ta fara kara zainab ta gani akan wayar ta juyar da kanta ta fara kokarin cire jikinta cikin nashi, ya kara matseta sosai ya dauka yace gayu ya akayi ne, tace fyn marafa kuma kai na jika shuru bayan nagama shirya program din, gashi nan masoya sai kira sukeyi, yace goshh wallhy sweety na ce ta mantar dani komai amma zamu zo tare yanzun nan, zee tace zaka sani yanzu da tym ya tafi ne zaka zo, sai dai kayi promisn dina zaku zo gobe, yace in shaa Allahu tace to Allah ya kaimu, yace ameen sannan sukayi sallama ya kashe wayar, ya kalli zulfah yace kishina akeyi, ta runtse idonta ta girgiza kanta, yasa hannu yana shafa wuyanta yace karya kikeyi, ta noke wuyanta ta danne hannunshi tace ni dan Allah ka bari, ya matseta a jikinshi yace bazan bari ba gobe zaki raka ni wani guri, ta noke wuyanta, yayi murmushi yace gulma ko, an fada miki banji labarin da kike bawa anty laila bane, ya kara rungumeta yace ashe ni dan gata ne ma an dade ana sona tun kafin a ganni, ta kara boye kanta cikin kirjinshi tace wallhy sharri zaka min, labe ka koma kana mana kan jin sirrin mu ko, ya fara goga kanshi cikin gashinta yace na labe din ba gashi najiyo abinda ya kwantar min da hankali ba, ya dago fuskarta yace Alhamdulillah nagode ma Allah da ya bani mace mai kamala wacce ta hada komai da komai, tayi murmushi itama tana shafo fuskarshi tace kace mun gode ma Allah dai, sai dai muyi adduar Allah ya barmu tare, Ameen thumma ameen ya fadi hade da yi mata wasu abubuwa masu wuyan fadi, Haka rayuwar familyn marigayi daddy ta kasance cikin farin ciki da kaunar juna tabbas adduar daddy ta bisu domin kuwa Allah ya fitar mishi da bata gari cikin iyalinshi, kullum cikin mishi addua suke, haka duk wata sai an sauke alkurani an sadaukar zuwa kabarinshi, Allah ya jikan dukkan musulman duniya ameen ya Allah... Tammat bi hamdulillah Alhamdulillah Allah nagode maka da ka bani iko da damar karasa littafin nan, kurakuren da nayi a ciki Allah ka yafe min su, Allah ka shige mana gaba a dukkan alamuranmu, Godiya ta musamman ga mijina uban ya'yana Allah ya barmu tare.. Ina muku addu'a a kullum ya'yana abin alfaharina Nuwairah Shattima Nour Shattima Anwar shattima Allah ya raya min ku kan tafarkin addinin musulunci, Jinjina gareku masoyana na Facebook da WhatsApp Allah ya bar kauna ina son duk musulmin dake cikin duniyar nan, Allah ya sadamu da alkhairi a ko yaushe kuma ya hada fuskokin mu a aljanna firdausi, Jinjinar ban girma zuwa gareki Hadiza isah Ameh mrs Jabeer Allah ya barmu tare kawata ya raya mana yaranmu, sai kuma kawalli Ummu abdool Allah ya barmu tare, Sannan zan mika godiyata da gaisuwa zuwa ga masoyana wayyo ina ma zan iya kiran sunanku dukkanku, Badiyya, Aneesah, Huris da Aysha dangusau kuzo ku tayani lissafosu dan Allah, kalmar godiya tayi kadan zuwa ga masu min addu'a wadanda nasani da wanda ban sani ba Sai dai kawai ince Allah yasa aljanna ce makomarmu.. Ga naku godiyar yan uwana masu kaunata dukka yan group dina na World of hausa novel amma banda NO SHAKING da HANNE CILLARE Allah ya barmu tare yan uwana.. Lovely sisters Rufaida umar fans Classic ladies novels Feenat jafar novels Hausa novel na Raff mukhtar Da kuma Hausa novel na dearest Sheedat Da novel's one Kai da duk ma sauran groups din ma da ban fada ba Allah ya barmu tare.. ameen Aysha Ya'u Kurah na muku fatan alkhairi Mrs tijjani shattima.....

Comments

Featured Post

Yadda Zaka Chanja Bayananka Na BVN

table of contents title